Hiyaam Page 5 Complete by Nimcy Luv


Ya yi saurin janye fuskarsa, sai ta kuma matso da tata har goshinta na sauka a nasa, ta washe fararan haƙoranta masu kyau ta ce "Kai kaɗo ne ko? Kai kyakkywa ne zaka zo a yi mana aure irin wanda ake yi?" Nan ma bai magana ba sai kallon ta kawai da yake yi, ya zame kaɗan ya yunƙura ya tashi sai a lokacin yaga ɗanyen barkonon data yatsar a wajan.


"Wayyo Allah, kana da kyau kai kyakkywa ne, amma baka da lafiya shi ya sa baka da kuzari"


Ya yi mata shiru.


"Me kake yi a nan? Kai ma ɗan gidan Moddibo ne? Ina naggenka? Ina Innarka ta mutu ko tana raye? Kuma kai ma kana ganin kayan cikin mutane? Mutum nawa ka taɓa ci? Ka taɓa fita maitar dare? Wa aka taɓa cewa ka kawo aci? Kai kaɗai kake kama kurwa ko haɗin gwiwa kuke yi?" Tambaya take ta yi masa daga wannan zuwa wannan, shi kuma ya juya mata baya.


Ɗan zabura ya yi kaɗan jin ta cakume shi sai ta yi baya. "Innalillahi!" Ta lumshe idanunta "Jikinka laushi kamar burudin da Saleh yake bani idan ya taɓa ƙirjina" Sannu a hankali ya juya ya kalle ta, don tsayi tana da tsayi amma bata kai Anarsa tsayi ba, kyau kuma bai san waye yafi wani ba, wannan akwai surutu kamar aku, ana kuma maganarta a sanyaye take kuma babu ƙuruciya a tattare da Ana magana cikin hikima take yi. Ana ta zama budurwa completely, wannan yanzu take girman.


***

"Barde, Gwamnati ai taku ce" Barde ya jinjina kai yana faɗin 


"Shi ya sa naga nine na hannun daman Gwamna. Na ji abin arziƙi na offers data fito daga hukumar Ma'aikata ta Jiha, kuma dai kai ne Kwamishinan ilimi, dole na yi kamun ƙafa da akai" Giɗaɗo ya buɗe fararan idanunsa ta cikin glasses ya kalli Barde kamar ba zai magana ba, sai ya ce "Mun tattauna da Indabawa jiya, an ware naku da za ku bawa iya family ɗinku, Offer ɗin me kyau ce, hatta salary duk da ba'a kammala yanke nawa za'a bada ba. Waɗanda za'a bawa Allowance ma daban suke. Don haka za'a dinga siyar da Offer ɗin akan dubu ɗari uku, ba zamu rabawa yaran talakawa a aikin banza ba, ba sanin darajar ilimin sukai ba duk sune ƴan iskan gari"


Barde ya ce "Allah mutumina? Shi ya sa nake yinka ba, masu Gwamanati da kan su" Giɗaɗo ya miƙe tsaye yana gyara zaman suit ɗin jikinsa wacce ta yi masa kyau sosai.


"You're not nice Barde. Zuwa anjima zan shige Qatar dani da Madam, wai tana buƙatar hutun sati biyu ne kawai a can"


"Dole Madam ta huta da yawa, kuɗi yazo Alhaji" taɓe baki Giɗaɗo ya yi, mutum ne me ji da kan shi uwa uba ilimi da izza professor matakin ƙarshe kuma Dr. Suka ɗan fito harabar babban wajan. Barde ya ce 


"Yanzu airport zaka shige kenan Giɗaɗo?"


"Nop, ina da meeting da Kwamishinar kuɗi, domin tattauna batun gina sabbin makarantu a jihar. 2 weeks zan yi na dawo akwai zama a Executive Council Majalisar zartawa"


***


Ta fashe da wani irin matsananci kuka tana jin kamar ƙasa ta tsage ta shige ko kuma ta mutu kafin azo kanta. Mutumin ne ya ce 


"Ko duka matan duniya za su ƙare ba za mu saurara sai UWA MAMAA ta bayyana ta cece mu daga halaka, sai ABAR BAUTA ta bayyana" 


Jin abin da ya ce ya saka Batty fashewa da kuka da ƙarfi ta ce "Do Allah idan akwai ɗiyar data san sunanta UWA MAMAA ta fito, walle bana son abin nan da ake yi kowa"


Daga daga cikin dakarun wajan ya zube a ƙasa yana ɗaga hannu ya ce "Ya shugabana shin babu wata alama da za'a iya haska mana yadda za mu UWA cikin sauƙi haka?"


"Akwai"


"Sanar dani Shugabana"


Ya shaƙi iskar wajan, yana wani irin ɗaci da raɗaɗi da yake cin zuciyarsa, ya dubi yarinyar dake kwance cikin jini har yarinya idan ya lissafa ya lalata budurcinta mata kusan arba'in kenan amma har yanzu haƙarsa bata cimma ruwa ba, da ƙyar ya ce 


"Akwai wasali UKU da aka bamu na farkon sunanta, a ciki ɗaya akwai wasalin daya fara da sunan UWA MAMAA shine kawai"


Farinciki ya kama duka jama'ar wajan.


"Ka bamu sunayen wasalin?"


A hankali cikin taƙama ya ce 


"Akwai A akwai F da H"


Ajjiyar zuciya Batty ta sauke jin babu wani wasali da ya yi iri ɗaya da BA tunda sunanta BATTY ne sai ta samu nutsuwar zuciya.


A haka aka dinga tambayar sunansa aka dinga ware wanda farkon sunansu ya yi ɗaya, a nan ne Batty ta hango wata mata a cikin babban keji da ƙaton ciki a jikinta tana kuka da ihu tana kiran Batty tare da yi mata alama ta gudu ko kuma dai tazo ta taimaka mata. Daidai nan kuma layi yazo kan Batty.


"Ya sunanki?"


Ta ce "Batty"


A hankali ya maimaita sunan "Batty"


Tun kafin ya yi magana ta ce "Amma na gaskiya Fatima ne kuma mayya ce ni....


Read the complete chapter 5 on ArewaPen.


Like the book

Share the link 

Drop a message 


Bright pens 

08164069385

Post a Comment

We welcome your thoughts! Please keep comments respectful, relevant, and free from hate speech, spam, or false information. Offensive or promotional content will be removed, and repeat offenders may be banned. By commenting, you agree to follow our Community Guidelines.

Previous Post Next Post