Matar Damisa Page 4 Complete na Asmertah Writer - Abokiyar Hira Novels

Matar Damisa

*★MATAR DAMISA★*


> By Asmeetah writer 


PAGE 4

Fitowarta kenam daga toilet, tana d'aure da towel a kirjinta, gashin kanta a baje agadon bayanta   ta wanke shi fess har wani shining yake ga ba'ki ga tsayi  har ya kusan isowa 'kugunta,  dake gashin Fulani ne da ita! 
Ayush farar mace ce ta asali, ga manya manyan idanuwa  gashin ido kuwa zara-zara ba'a magana,  azo kan gashin gira  acike tam da gashi har girar ya kusan had'ewa 2,  ga shaden ta luf-luf kwance da gashi,  gashin gaban goshinta kuwa ya sau'ko sun had'e da girar ta.
Allah yayiwa Ayush baiwar suman gashi  ga kyau ba'a magana, ga tsayin hanci kamar Wanda kullum ake dad'a tsayinsa,  lips d'inta kuwa kamar bakin tsuntsu  tsabar 'karanta tana da 'karamin baki, colour bakinta yaci maroon sosai  kamar wacce ta shafa jan-baki, kuma haka bakinta yake tin tana jaririya,
Ayush ko kad'an bata makeup saboda kwalliyar fuskarta Wanda Allah ya tsara mata mah ya isheta,
Ko tayi makeup ko kartayi kullum Ayush a cikin kyau take,  doguwar mace ce, siririya marar kauri,  sai dai akwai kayan alatu kam 
Ta waran 'kirjinta ba'a magana  a cike fam kamar meyin ciko sai dai bata saka rigar breziya,   saboda gurin da ta zauna da mahaifiyarta basa samun kud'i balle suyi siyayyan kayan da zasu saka, sai riga kala d'aya da take using dashi kullum.....
                        Anzo gurin kuma  wato waran Baanbom d'inta   ga hips kuwa kamar ita tayiwa kanta, ta ko Ina a cike yake a jinkinta  duk da batada jiki amma tana da kyakykyawar surar jiki....
Tsayawa tayi a gaban mirror ta kammala shafa cream mai shegen 'kamshi ta feffesa turare a jikinta ta gama gyara gashin kanta ta d'aure da rivon,    shikenam makeup d'inta kenam ko powder bata shafa ba  amma fuskar yanda kasan an tsara kyakykyawan makeup ne.
Ta nufi yanda Doctor Fatima ta ajiye mata kayan da zata saka,     wata dan'kararriyar doguwar riga ne na kanti mai bell a jiki  black color.
Zura rigar tayi sannan ta d'aure kunkumin ta da bell d'in,   kunkumi kamar na sauro sai tilin 'kugu,  ga breast d'in ya fito sosai  Masha Allah  kayan ba 'karamin kyau sukayi mata ba.
       Ba tare da ta rufe kanta ba  ta bar room d'in tana taka matakala a hankali ta sau'ko falo, ta nemi d'aya daga cikin jerin kujerun falon ta zauna ta d'aura 'kafanta d'aya akan d'aya  tana fuskantar television Wanda a ciki ake showing India film.
                 ( (Ashe Ayush er Hutu kenam, wato da ace a gidan masu kud'i Ayush ta fito waii da anyi 'karyar rai))

"Mom please stop crying,  banyi haka don na 6ata miki rai bane, just I can't believe any body,  ni ban yarda da wannan yarinyar ba,  zaifi ta bar mana gida" 
Junaid ne yayi maganar yana ri'ke da hannun mom d'insa.
               Doctor Fatima d'agowa tayi da rinanan idanuwanta wad'anda sukayi jawur tsabar kuka,  "Junaid ba wai na'ki batunka bane kana da gaskiya,  bama bu'katar yarda da kowa  domin yarda da Bara'atu ne yayi silar mutuwar mijina mahaifinka,  wanda Inna tuno da hakan nakanyi kuka mai rad'ad'in gaske,  amma abunda nakeso ka Sani shine  wannan yarinyar da zata zauna damu Yarinya ce 'karama like bazata wuce 20yrs ba 
Bata da mummunan 'kudiri a ranta face neman taimakon da takeyi,  tana bu'katar kulawa,
Mace ce mai rauni inta bar gurin mu bamu San hannun wanda zata fad'a ba  maybe mai cutarwa ne,
Kar muyi gaggawar rabuwa da ita domin idan ta shiga hannun mungu tabbas sai Allah ya tambaye mu  tinda nasan mahaifiyar ta bata raye  marainiyace  bata san yanda mahaifinta yake ba  shin yana raye ko ya mutu sai Allah, 
Please my son"
                 Dogon Numfashi yaja sannan yace "OK mom na Amince ta zauna a tare da mu, but idan naga robish anything can happen".  Yakai karshen maganar yana kallon mom d'insa  
Murmushi ita kuwa tasau na farin ciki tace "insha Allahu ba abunda zai faru, thank you my son" 
               Mi'kewa yayi akan lallausar gadon sa yana fad'in "OK call her for me, I want to see her" 
                Mi'kewa tsaye tayi tace "to Zan kuwa Kira ta yanzu tazo ta gaida Boss d'in gidan". Tana shirin fita  yace "mom please am hungry  let me eat something"  yana kai karshen maganar ya wani d'aure fuska kamar bai ta6a yin murmushi ba,
     Mommy kuwa ganin hakan yasa ta kwashe da dariya tana fad'in "OK don't worry, yaro ba wasa da eating"  fita tayi ta bar d'akin, shi kuwa rufe idonsa yayi kamar maiyin bacci ...

Shima fa Junaid asalin kyakykyawa ne, white chaculate  ba ba'ki bane still bai kai asalin farin fata ba domin ko rabin farin Ayush bai d'auko ba,  but mutumin akwai dogon hanci ga bigger eyes bakin shima 'karami ne,  dirarren namiji ne ga tsayi ga fad'i ga jiki ga-ga-ga-gaaaa abubuwan sunyi yawa yara kamar su suka halicci kansu ,   shima akwai tara suman Gashi akansa baya son aski sai dai akwai son gyara suman kullum Gashi a kwance lufff  azo kan jikinsa duk gargasa ne ta ko Ina a jikinsa a kwance luf domin ba 'karamin cream na gyaran jiki Junaid yake amfani da shi ba,  Gashi tin daga kan sajensa har zuwa gemunsa a kwance yake.....

Fitowar Doc. Fatima falo ta tarar da Ayush zaune tana ta kallo hankali kwance,
    Sauran kad'an Mommy ta juya da gudu ganin Ayush ta d'au Aljana ce 
               Ayush ce ta kalli gurin da mommy take ta sau murmushi "Aunty na fito ban ganki ba"
        Ajiyar zuciya mom tayi sai a yanzu hankalinta ya dawo dai dai jin muryar Ayush d'in
   "Wayyo Alhamdulillah Ashe Ayush d'in ce". Ta 'karaso yanda Ayush d'in take.
              "Masha Allah Ayush kinga yanda kikayi kyau ne, danma bakiyi makeup ba da ba'a San irin kyau d'in da zakiyi ba, said dai a kulleki saboda sumar da samari zaki rin'ka yi a titi"

Kwashewa da dariya Ayush tayi  
    Tana kallon Doctor Fatima wacce ta 'kura mata ido
           Ita kuma Ayush sai zabga uban murmushi take dimple d'in nan gwanin burgewa.

"Gaskiya zanso Junaid yaga yarinyar nan ko zai 'kyasa, inada burin ta zamo surkata na samu jikoki kyawawa" Doctor Fatima ce maiyin maganar zuci,  daga bisani tayi gyaran murya  sannan  tace "Yawwa Ayush Oga yana son ganinki"
        Cikin mamaki Ayush take kallon Momy tace "wayene Oga kuma Aunty?  Kodai mai gidan kike fad'a?"
         Duk lokaci guda tayi tambayar still Idonta akan Mom,
     Short laugh Mom tayi sannan tace "eh kusan hakan ne, 'karamin maigidan ne domin babban maigidan ya rigamu gidan gaskiya,  'karamin maigidan kuma shine yaron gidan"
           Sai a yanzu Ayush ta dawo nutsuwarta taja ajiyar zuciya 
"Toh shikenam Aunty Zan jeni, Allah ubangiji ya ji'kan maigidan"
              Amsawa Mom tayi da Amiin.
             Mi'kewa Ayush tayi tana tambayar yanda yake zata je gaisuwa,   
Nuna mata hanya Mom tayi yanda zai sadata da d'akin Junaid,  ta fara tafiya kenam Mom ta tsayar ta tana fad'in "tsaya ki tafi masa da lunch d'insa  domin ya sanar mun da cewa yana jin yunwa.
              Tsayawa Ayush tayi tana jiran momy cikin en mintina saiga Mom da manya manyan kuloli har kashi hudu asaman glass tray ta d'aura a kayi hannunta ri'ke da flas da'kananun kofina a Jere saman glass tray d'in,
Yanda Mom ta d'auko haka Ayush ma ta d'auka 
Tana hawan upstairs a hankali tabi yanda akayi mata kwatance sai gata a d'akin Junaid,
'Daki wayam ba kowa, sai'karewa d'akin kallo take yayi matukar burgeta 
Ta sau'ke kayan abincin a saman dinning d'insa, 
Taje gaban mirror tana duban kanta, kwatsam sai ta hangoshi ta cikin madubi yanata sharar bacci akan gadonsa,  dake akwai labule ta tsakanin gadon hakan yasa bata ganshi da wuri ba.
Juyowa tayi da sauri tana le'kashi ta bud'e labulan a hankali tana so taga fuskar shi amma sai dai hannayensa suna kan fuskarsa ta kasa ganin fuskar...........


Ayush tsayawa tayi a bakin gadon da Junaid yaketa sharar baccinsa ya rufe fuskar da pillow,     tana tunanin ta tashe shi ne ko kuma ta kyale shi kawai tayi tafiyarta
Lokaci guda ta yanke shawarar tashin shi yaci abinci kada yayi sanyi,         cikin 'karfin hali ta haye saman gadon tana rarrafawa a hankali cike da fargaba  saida tazo saitinsa ta tsaya cak ta kasa tashin shi.
                  Shi kuwa adai dai lokacin ya fara wani irin mafarki mai tsoratarwa,   A cikin baccin yaga wata ba'kar Damusa mai jajayen idanuwa ta tsaya daf dashi tana shirin Kai masa hari!   A gigice Junaid ya Kai mata naushi da iya 'karfinsa  
Wayyo a madadin ya naushi Damusan ashe  a Ayush ya kaiwa wannan naushin a saman Nononta ta 6angaren dama, wani irin 'Kara tayi ta wantsilo 'kasi sai datayi dungure sau uku  ta tsinci kanta a bakin 'kofa,  hankali a tashe ta mi'ke tana tangal tangal kamar wacce tasha kayan maye!  a haka ta fice daga d'akin...
                Shi kuwa cigaba da baccinsa yayi hankali kwance.

Mommy tana shirya musu kayan abinci  a dinning 
Ta jiyo kukan Ayush     da sauri ta waiwaya bayanta domin ganin abunda take ji,
Ayush bata tsaya wata-wata ba sai yaraf ta fad'i 'kasi tana ta faman juye-juye da shanbe-shanbe  "wayyo Allah Zan mutu, kirjina ya fashe ciwoo".  Ta Kama Nononta da hannunta domin ba 'karamin zogi yake yi mata ba 
Duk ta rasa Ina zata saka kanta,  idanunta duk sun kad'a sunyi ja tsabar azaba ga wani gumin da yake yarfo mata..
             "Ayush lafiyanki kuwa? Ke da waye? Meya sameki" haka mommy taita jero mata tambayoyinda bazata iya amsa su ba a yanzu,
           Ganin yanda taketa juyi a gurin yasa mommy tsorita da sauri ta kamo Ayush tana fad'in muje mu d'aki kiyi hakuri"
             Ayush KO mi'kewa bata iya yinsa   kamar Wanda wuta yake ci akan Nonon haka take jin rad'ad'in nan.
               Zaunar da ita tayi a bakin gado,  tana fad'in "sannu ko, wai meya faru ne Ayush?"
        A lokacin Ayush ta d'an dawo hayyacinta duk da zafin da gurin yake yimata          da 'kyar ta bud'i baki tace "buguwa nayi" bakinta na kakkarwa kamar maijin sanyi,
                "A'a Ayush ki gaya mun gaskiya, shin da mai kika bugu?
           Kamar bazata yi magana ba can tace "na bugu da 'kofar d'aki ne"  murya sanyi sanyi take magana.
      Mommy tace "kin tabbata?"
Kai Ayush ta d'aga mata alamar eh.
        Mom tace "to muga gurin da kika ji ciwon"  ta 'karasa maganar tana  faman cire rigar Ayush!
            "A'a Aunty ki Bari kawai ba wani ciwo sosai bane"  a cewar Ayush wacce kanta ke kallon 'kasi alamar kunya.
               Mommy kallon ta take cike da mamaki tace "to banda abunki nifa mace ce er uwarki sannan in baki manta ba ni Doctor ce, dubaki zanyi naga wani kalar magani ya dace ki sha"    da kyar Ayush ta yadda  ta zame rigarta daga sama  sannan a hankali ta zame breziyar ta   Mommy tana ganin yanda Breast d'inta d'aya ya kumbura suntum ga yayi jawurr abunka da farar mace  
"Innalillahi wa inna'ilaihi raju'un, Ayush duk wannan ciwon a buguwar 'kofa yake? Ki duba kiga?". 
             Banda zubda hawaye ba abunda Ayush take, ita kad'ai tasan irin rad'ad'in da take ji!
       Da sauri Mommy ta tashi tana fad'in "wannan bana zama bane kina bu'katar treatment" 
             Ta fice daga d'akin gaba d'aya ta susuce   a ranta tana tunanin Junaid ne yayi mata wannan d'anyen aiki  daman ya nuna baya son zamanta a gidan.
               Ayush kuwa tashi tayi ta nufi toilet  tsayawa tayi a gaban mirrow tana fad'in "wannan bawan Allah ba 'karamin mungu bane, azzulumi  daga tashin sa a bacci yaci abinci shine zaiyi mun wannan hukunci,  Allah zai saka mun"  ta 'karasa maganar tana zubda zafafan hawaye,  ga Nono d'aya kuwa yayi timm kamar Wanda ya Tara ruwa.
  Tana cikin sambatun ta tajiyo bud'an 'kofar d'aki. 
Mommy ce ta shugo hannun ta ri'ke da boxes na pharmacy,  ta 'kara ficewa ta dawo da kulolin abinci  ta ajiye a saman table,  zama tayi a bakin gado tana jiran fitowar Ayush,   ba jumawa Ayush ta fito da d'aurin towel a kirjinta tayi using da hot water  domin jikin ta ya samu 'kwari.
               "Ayush en mata anyi wanka kenam, Bari na za6a miki 'karamar riga wanda zakifi jin dad'in zama da ita" 
Ta bata doguwar riga sleeping dress mai short hand  marar kauri  ta Sanya a jikinta  bayan pant babu komai a jikin ta sai wannan longer shirt,  zama tayi kusa da mommy wacce ta d'auko magunguna tana 'ko'karin bud'e mata su  ta bata lokaci guda ta Kora su, daga baya Mom ta d'auko Allura tana 'ko'karin yi mata,  tabb d'in Ayush taga makiyarta wato Allura da gudun gaske ta nufi toilet ta danna sakata tana fad'in "wallahi baza'a mun Allura ba, Dan Allah Aunty kiyi hakuri ki ban ko wani irin magani amma banda Allura"
          Mommy sake baki tayi tana kallon ikon Allah  kwashewa da dariya tayi tana fad'in "Ayush da girman ki kike tsoron Allura?  Nake ga Allurar zaifi miki amfani cikin gaggawa KO!"
Ba yanda mommy bata yi da Ayush ba akan ta fito amma furr Ayush ta'ki Allura sai hakura tayi  tace "toh shikenam ganan Abinci kizo kici tinda kin'ki Allura"
                      Momy cikin fushi tabar d'akin ba wai saboda Ayush ta'ki Allura bane,  tana so taje ta samu Junaid ne akan Abunda yayiwa Ayush,  Sam bai kyauta mata ba,

Bayan fitar Mommy daga cikin d'akin  Ayush ce ta bud'e 'kofar toilet a hankali ta lalla6o  ta d'auki Alluran da mommy ta ajiye saman table tasa a cikin boxes ta rufe,   sannan ta d'auki flask din abincin ta zuba a plate  paten doya ne da wake, sai ta tsiyayi ruwan tea a cup  tana ci tana Kora tea,  daman ba 'karamin yunwa take ji ba, tinda ta shugo gidan nan take had'uwa da 'kaddarorinta bata samu tasa komai a cikita ba,     Ayush fah ansamu eating kamar ba gobe,  tana ci tana yarfa hannaye tsabar zogin da Nononta yake yi mata kawai dai jurewa take........

Mommy
Kamar zata dungura haka take hawa upstair nan  tana zuwa ta bangaje 'kofar d'akin   tana shirin yin masifa,     abunda ta gani ne yasa ta tsaya cakk  ta zaro ido waje  bakinta na kakkarwa take fad'in "Innalillahi wa inna'ilaihi raju'un, JUNAIDDD"   
         wani irin gigitaccen ihu tayi ta fad'i 'kasi sumammiya....

Ikon Allah mai Mommy ta gani haka???  

Duk yanda akayi ta ga abunda yafi 'karfin tunaninta ne!.

Post a Comment

We welcome your thoughts! Please keep comments respectful, relevant, and free from hate speech, spam, or false information. Offensive or promotional content will be removed, and repeat offenders may be banned. By commenting, you agree to follow our Community Guidelines.

Previous Post Next Post