![]() |
| Asalin hoton, Khames Alrefi/Anadolu via Getty Images |
A yau, Falasɗinawa za su fara tsallaka iyakar Rafah tsakanin zirin Gaza da Masar, wadda aka rufe kusan shekaru biyu bayan sojojin Isra’ila sun karɓi wasu sassa na Gaza.
Sake buɗe mashigar Rafah, wanda aka dade ana jinkirta shi, wani muhimmin sashe ne na yarjejeniyar tsagaita wuta da shugaba Trump ya tsara a Gaza.
Rahotanni sun nuna cewa Isra’ila ta ce za a bar marasa lafiya 50 tare da iyalansu biyu su tsallaka iyakar kowace rana, sannan wasu mutum 50 daga cikin waɗanda suka bar Gaza a lokacin yaƙi za a ba su izinin komawa.
Yanzu haka, dubban Falasɗinawa marasa lafiya da masu rauni na jiran damar barin Gaza domin neman magani.
Tags
Labaru
