Ragayar Dutse Page 12 Complete by Nana Haleema

Kida a Ruwa

 *RAGAYAR DUTSE.*

              ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*

*Page 012.*

Rehaan ya bi Jazy da kallo ya ce, "ina ka je?." Jazy ya ce, "na je masallaci mana." 

Ya harare sa ya ce, "nima ai na je, amma ban ganka ba." 

Ya ɗan shafa kansa ya ce, "ana idar da sallah na je na sha tea. Meye ka ke nemana kamar na ci maka bashi?" Ya faɗa ya buɗe room ɗinsa. 

Rehaan ya ja tsski ya ce, "bana so ka dinga yawo, kar a yi noticing muna cikin hotel ɗin nan."

Jazy ya shiga ɗakin sa yana cewa, "kai dan kana ɓoye kan ka ni bazan ɓoye kaina ba, kai ake nema ai bani ba."

"Shine ka je ka sha tea baka taho min dashi ba, nawa da aka kawo min ya zube." 

Jazy ya wani kalle sa ya ce, "Kai! Ba fa yaron goye bane ba kai, in baza ka je ka ka siya ko ka yi order ba ka bar shi. Ni bacci nake ji, sai anjima" ya faɗa yana rufo ƙofarsa ya bar sa a tsaye.

Ray ɗaki ya shiga yana kallon inda tea ɗin ya dan ya ɗan zube masa a jiki, ya ja tsaki ya cire rigar ya ajjiye sannan ya zauna a kan gado. Sai kuma ya jawo wayarsa ya duba ya kuma ajjiyewa bai ce komai ba.

     Islaha kuwa cike da takaici ta sauka groundfloor, a reception ta haɗu da su Saleem suna niyar zuwa floor ɗin. Ta kalle su ta ce, "na manta handbag ɗina a mota, shine zan je in ɗauko." 

Muslim ya ce, "gata na ɗauko miki, na san dole zaki nema ta." Ta karɓa fuskar ta babu walwala. 

Saleem da ya san halinta ya ce, "ya dai?."

"Wani ɗan rainin hankali ne ya buge ni ya zuba min tea, kuma dan wulaƙanci ina magana ya yi min banza kamar bai yi laifi ba. Ji inda ya ɓata min riga, ga abaya mai sauri riƙe dauɗa."

"Ina fatan ba ki mayar masa ba?."


"Kaima ka san bazan zuba masa ido ba ko?."


"Islaha nan fa hotel ne, akwai mutane mabanbanta wanda baki san matsayinsu ba. Ki dinga kula."


Ta ɗan yi tsaki ta ce, "sai me? Dan yana da wani matsayi baza a nuna masa kuskurensa ba?. Tea ne a hannunsa fa, ya buge ni ya zube min a jiki, ba a hannuna tea ɗin yake ba, amma yi haƙuri ya gagaresa faɗa. Kuma sai in zuba ido ina kallonsa, ya zubawa banza mara gata ko?."


"A'a, ni ban ce ba."


"Ka ma ce ɗin, ka san ba bari zan yi ba. Kuma bai yi kama da ɗan ƙasar nan ba ko kaɗan." 


Saleem ya girgiza kai ya ce, "nidai ina so ki rage wannan tsiwar taki, gidan wani zaki je." 


Ta ɗan harare sa ta ce, "gidan Hamma zan je ai, ya san kuma ya nake. A haka ma na ƙyalesa ne saboda Hamma ya roƙe ni kar in yi faɗa, Allah da sai na tara masa jama'a."


"Daman shi ya taɓarɓara ki ai."


Suka yi dariya a tare, suka nufi elevetor suka shiga zuwa floor ɗin.


Sai da ta sake kallon inda ta ga Rehaan amma babu alamunsa, wajan babu kowa sai waiter da table tana knocking ɗaya daga cikin ƙofofin wajan inda suka yi order abinci. 


Suna shiga suka zaunna akan kujerun da suke ɗakin, ita kuma ta shiga bathroom ta ɗan wanke inda tea ɗin ya zube mata, ta dawo ta zauna a gefen gadon ta ce, "tsakani da Allah awa nawa zamu kwashe a wajan nan? Bamu da tabbacin a ina wannan bawan Allah yake." 


Muslim ya ce, "wallahi har na gaji Islaha, har yanzu babu cikakken information akan inda zamu same sa." 


Saleem ya ɗauki waya ya ce, "bara na kira Chairman, ya kira PA ɗinsa ya faɗa mana ko da floor ɗin da yake ne, in yaso sai mu tara zuwa lokacin sallar azahar."


Ta wara ido ta ce, "har azahar?." 


Saleem ya ce, "muna da mafita ne Islaha? Dole haka zamu yi." 


Saleem ya kira Chairman suka yi magana, bayan ya kashe ya ce, "Sun yi magana da PA ɗinsa, ya ce zai turo mana hoton wanda suke tare, ya ɗan fi sa sauƙin gani, amma yana da ƴar shariya kaɗan. Ya ce indai mun gansa kamar mun ga Mt Rehaan Yola ne."


Islaha ta gyaɗa ki tana taɓe baki ta ce, "taɓ, ka ce wannan aikinka ne, dan bazai wulaƙanta ni ko ya share ni ba wallahi. Kun san in hakan ya faru da faɗa za a rabu dani. Garin son ganin Ray mu ƙare a police station."


Muslim ya ce, "wallahi aikin ki ne ba mu ba, ga ki a tare damu me zamu yi?. Ai indai da mace a irin wannan tafiyar namiji baya saka baki. Macen ma irin ki, mai kyau da sa a." 


Ta ɗan yi murmushi ta ce, "Aa fa, ni wallahi ba za a wulaƙanta ni a banza ba. Zan iya ɓarar da komai wallahi, sai dai Chairman ya saka a kulle ni" ta faɗa tana ɗaukar wayarta da take ƙara.


Ganin Hamma ne sai da ta yi murmushi sannam ta ɗauka ta saka a kunne ta ce, "Hamma ina kwana."


"Islaha kun gama?."


"Ina fa, har yanzu ban samu damar ganinsa ba. Ba mu san a wanne floor yake ba har yanzu."


"Babu lokacin dawowar ki kenan?."


"Gaskiya babu."


"Kina ina yanzu haka?."


"Mun yi reserving room, ina ciki."


"Su kuma fa?." Ta ɗan kalle su ta ga Muslim ya zuba mata ido, saɓanin Saleem da yake danna wayarsa.


Ta ɗan sauke numfashi, ta yi ƙasa da murya sosai ta ce, "muna tare." 


A ɗan fusace ya ce, "a ɗaki ɗayan ku ke?." 


Ta ɗan girgiza kai ta ce, "eh, da yake muna tattaunawa akan yadda abin zai kasance ne."


"Islaha gaskiya bazan jure wannan shirmen ba, ki zauna ɗaki ɗaya da maza biyu a hotel?."


"Kar ka damu, aiki ne ya kawo hakan. Na san ka yarda dani ai ko?." 


Sai da ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "ki kula, zuwa anjima in baki dawo ba zan zo." Kafin ta yi magana ya kashe wayar, ta yi murmushi tana ajjiye wayarta a gefe.


Muslim ya ce, "Isalaha kina son Hamma da yawa." Ta ɗaga ido ta wani kalle sa, sai ta share bata basa amsa ba. 


A lokacin Saleem ya ce, "yauwa, ga hotonsa an turo min. Sunansa Jafar Yola, inkiya Jazy. Cousin ɗin Rehaan ne kuma abokinsa, da babansa da babansa uba ɗaya suke."


Muslim ya karɓa yana kallon hoton Jazy ya ce, "wannan ai na san shi, indai zaka ga Ray to daƙyar baka gan shi ba. Da yawan hotunansu a tare suke." 


Ya miƙawa Islaha ta karɓa tana kallo, ta ɗan buɗe ido ta ce, "kai wannan ai na gan shi."


A tare suka ce, "a ina?." 


Ta kalle su da mamaki ta ce, "a floor ɗin nan, lokacin da nake faɗa mu ku an zuba min tea, elevator ɗin da ya fito na shiga, har sai da basa hanya ya wuce." 


Saleem ya ce, "oh Islaha! Meyasa baki yi masa magana ba?."


"Ban san shi ba ai, ko guest ɗin na mu ban san shi ba, ban taɓa tsayawa na ƙare masa kallo ba balle na riƙe fuskarsa a raina."


Muslim ya ce, "kai, mun yi wasa da damar mu." Ta ɗan yi shiru ta ce, "Hakan yana nufin Jazy da Ray a wannan floor ɗin suke." 


Saleem ya ce, "Za ki iya gane room number ɗinsa?." 


A tare suka miƙe suka fito bakin ƙofar, tana kallon ɗakunan da suke a kulle ta ce, "ban ga ɗakin da ya shiga ba, amma ina da tabbacin a wannan floor ɗin ya yake."


Saleem ya ce, "shikenan, hakan ma an samu cigaba ai. Mu koma tukunna." 


Suka dawo ɗakin Islaha ta ce, "da na san shine da nayi masa magana, ohh! Yanzu a ina zamu sake ganinsa?." 


Muslim ya ce, "kar ki damu, ba laifi bane ba hakan, rashin sani ne. Amma yana da kyau a nuna miki hoton Ray kar aje shima kin haɗu dashi."


Ta ɗan yi dariya ta ce, "babu baƙata, wataƙila in na gansa zan gane sa." 


Saleem ya ce, "zata gane Ray, ai ba ɓoyayye bane ba." Suka koma suka zauna suka cigaba da tattaunawa. 


Islaha ta gaji da zama, kwanciya take son yi amma bazai yu ba saboda waɗanda suke tare. Duk ta takura, zaman ya ishe ta, har bacci take ji yana ɗaukarta. 


Saleem ya kalli agogo ya ga ƙarfe takwas na safe, ya ce, "ya kamata mu samu tea mu sha. Muslim mu je mu samo abinci mu barta a nan." Suka miƙe suka fita suka bar ta a ɗakin.


Basu jima da fita ba ta taso ta fito tana sake kallon wajan ko zata ga Jazy amma babu kowa a wajan. 


Ƙarar elevetor ta ji sai ta juya tana kalon wajan, ta yi tsaki ganin wraiter tana tura table ɗin abinci. Ta kalli Islaha ta ce, "morning madam." Islaha ta yi murmushi ta amsa, ita kuma ta wuce room ɗin da tazo tana knocking.


Ɗan buɗe ƙofar da take knockinga aka yi, ta ɗan kalli wajan sai ta ga bata ganin kowa sai waiter ɗin da ta shiga ciki da table ɗin. Ƙarar elevator ta sake ji, ta juya ta ga Saleem da Muslim sun dawo.


Saleem ya miƙa mata tea ya ce, "me ki ke yi a nan?." 


Ta ce, "ina dubawa ko zan sake ganinsa." 


Saleem ya ce, "mu shiga ciki, bazai yu mu tsaya a nan ba, har gwara mu mu je kan kujerun can mu zauna mu jira mu gani. Amma mu fara cin abincin." Bata ce komai ba ta koma suka biyo bayanta.


Har ƙarfe goma suna zaune babu labari, duk sun gashi da zaman waje ɗaya. 


Islaha ta ce, "zama a nan bazai yu ba  Hamma Saleem, mu fita mu je mu zauna a kan louge chairs ɗin can, mu dinga kallon masu shige da fice, kar mu je muna nan su bar hotel ɗin. 


Saleem ya ce, "haka ne, mu je." 


Muslim ya ce, "ku je zan fito." Ba musu suka fita suka bar masa ɗakin.


Muslim ya ɗauki wayarsa yana tsaki ya ce, "Ummi kin dame ni, meye wai?." 


Daga can ɓangaren ta ce, "bana so Islaha ta yi nasara a akan wannan aikin shiyasa na damu, ka san abinda zaka yi ka lalata haɗuwarta da Mr Ray."


"Na fi ki sanin abinda nake yi, na fi ki sanin abinda zan aikata. Ki daina takura min da waya, kin san ta da shegen wayo, zata iya gano wani abun."


"Shikenan" ta faɗa tana kashe wayar.


Ya kalli kan gadon ya hango handbag ɗinta, ya ƙarasa ya buɗe ya ɗauko invitation card ɗin da yake ciki, ya ninke shi ya saka a aljihu. Ya ɗauko wani irinsa sak a aljihunsa ya musanya da nata, ya mayar da jakar inda ya ɗauka ya ajjiye. 


Ya girgiza kai yana kallon jakar ya ce, "za ki haɗu da Mr Rehaan Islaha, amma a police station zaki ƙare, dan ni kaɗai na san me na rubuta. Baza mu taɓa bari ki yi nasara akan mu ba wallahi, sai mun ɓarar da duk wata nasara da za ki samu a rayuwar ki, baki isa ki zo a bayan mu ki fi mu ɗaukaka ba. Kina samun damar hira da Mr Rehaan shikenan kin yi mana fintinkau, sai mu gani in hirar zata yu" ya yi ƙwafa yana cize bakinsa sannan ya fito. 


A zaune ya same su suna hira ita da Saleem shima ya zauna ya shiga sahun hirar.


Tun suna zaman daɗin rai har suka gaji, ta koma ɗakin ta sake dawowa ta zauna, suma suka koma ɗakin. Kiran sallar azahar ya saka Saleem da Muslim fitowa daga ɗakin, suka kalle ta tana inda take a zaune. 


Muslim ya ce, "zamu wuce masallaci." 


Ta ɗaga kai suka sauka ita kuma ta rufe ido cike da gajiya da kasala. 


Ƙaramin bacci ne ya fara ɗaukarta, a lokacin Jazy ya buɗe ƙofa ya kalli inda take, ya ganta a zaune akan kujera ta ɗora ƙafa kan ɗaya amma idanunta a rufe. 


Ya ɗauke kai, ya fito ya yi knocking ɗakin Ray ya buɗe masa ya shiga. Ƙarar rufe ƙofar da Jazy ya yi ya saka ta buɗe ido, ta miƙe zaune ta nufi ɗakin dan ta yi sallah.


    Jazy yana shiga ya bi Ray da kallo da yake sanye da ƙananun kaya marasa tsaho. Ya ce, "har ka dawo daga sallar ne?."


"Ban je ba, a nan na yi."


"okay, ƙarfe nawa zamu wuce?."


"Ban sani ba nima." 


Jafar ya zauna yana kallon sa ya ce, "ƙarya ka ke, duk bala'i yau sai mun koma gida wallahi." 


Shi dai bai ce komai ba ya waya da ya ɗauka yana dannawa.


Jazy ya ce, "wannan room ɗin na kusa da naka, ashe wani babban ɗan siyasa ne a ciki, ya gayyato wata yarinya ta taya shi kwana, yanzu zancen da nake yi maka ta yi masa sata ta gudu."


Ray ya ce, "Allah ya ƙara, saboda son tonawa kai asiri ne ya saka suke son suke mu'amala da ƴan nigeria. In iskancin ka ke so ka je ka smau baturiya, babu sata balle yi maka video ta yaɗa." 


Jafar ya taɓe baki ya ce, "matsalar su ce ba tamu ba."


"Na ga yarinyar, kuma na ga fuskar ta, har bayan ta wuce ya leƙo yana cewa ta manta facemask ɗin ta." 


Jazy ya kalle sa ta ƙasan ido ya ce, "zaka taya sa bincike a kamata kenan?."


"Da zan ganta kyauta zan yi mata, ta ci kuɗinta hankali a kwance." 


Ya yi dariya ya ce, "ka shirya kawai malam, ina so na ci girkin Mummyna wallahi."


Ray ya kwanta ya ce, "bacci zan yi, zuwa dare sai mu koma." 


Jafar ya miƙe ya ce, "wallahi zaka neme ni ka rasa, domin bazan tsaya kana wahalar dani ba. In ba dan Mamy ba, bazan tsaya ina saurarenka kana abinda ka ga dama ba, kaima ka san baka isa ba" ya faɗa yana fita daga ɗakin. 


Kallon inda Islaha ta zauna ɗazu ya yi, bata nan amma akwai id card ɗinta a wajan. Kamar bazai ƙarasa ba, sai ya ƙarasa dan ya duba, haka kawai bai yarda da ita ba.


Ya ɗauki Id card ɗin yana kallo, ya girgiza kai a bayyane ya ce, "no wonder, ashe yar jarida ce." 


A daidai lokacin Islaha ta fito daga ɗakin ta ƙaraso wajan. 


Suka haɗa ido da Jazy, kamar a mafarki ta ganshi yana kallon ta, ta ƙaraso da sauri ta ce, "Good day Mr Jafar." 


Ya bita da kallon up and down, ya ƙi yi mata magana sai kallonta kawai yake yi kamar mai son gano wani abun a jikinta. Islaha itama kallonsa take yi kamar yadda yake kallonta, tana jira ya amsa mata. 


Kamar bazai ce komai ba, sai daga baya, cikin yanga da jan aji ya ce, "so why are you following me?."


Ta kalle sa tana ɗan murmushi ta ce, "I'm not following you, sir. I don't even know you personally. My colleagues were the ones who showed me your picture."


 Ya kalli Id card ɗinta ya kalle ta, kafin ya yi magana ta ce, "zan iya samun lokacinka?." 


Fuskarsa babu walawala ya ce, "for?."


"A few questions sir." 


Ya ɗan girgiza kai ya ce, "So you've been following me just to ask me a questions?."


"Yes, Mr Jafar." 


Ya ɗan taɓe baki yana girgiza kai, zai yi magana ta ce, "don Allah, give me a chance."


A lokacin Saleem da Muslim suka zo wajan suna kallonsu da mamaki. Jafar ya bisu da kallo, ya kalle ta ta yi sauri ta ce, "there are my colleagues." 


Ya ɗan kalle su kafin ya ce wani abu ta sake cewa, "please Sir." 


Ya ɗan kalle ta ya ɗauke kai, yana kallon ɗakin da Rehaan yake, ya sake kallon ta ya ce, "Okay, come in" ya faɗa yana shiga ɗakin da yake. 


Ta juya ta kalli su Saleem, Saleem ya yi mata alamar da ta shiga kar ta ɓata lokaci, ta daidaita nustuwarta ta riƙe handbag ɗinta ta shiga da sallama.


Ya amsa yana zama a akan kujera ya nuna mata wacce take kallonsa ya ce ta zauna. 


Ƙarewa ɗakin kallo take yi, ganin kamar ba a hotel ɗaya suke ba, ganin ɗakinsa mai kyau da girma fiye da nasu, komai na ciki luxury, ga sanyi da ƙhamshi mai daɗi da yake yi. 


Bayan ta zauna, ya ɗora ƙafa kan ɗaya yana juya id card ɗinta a hannunsa. Kafin ta yi magana ya ce, "Miss Islaha from toron guiwa tv."


Ta girgiza kai ta ce, "Yes, Mr Jaafar." 


Sai ya canja harshe zuwa hausa ya ce, "okay ina ina jinki, me ke tafe dake?." 


Da mamaki ta kalle sa, dan gaskiya bata ɗauaka yana jin hausa ba, ta ɗauka turanci kaɗai yake ji, ko fulfulde bata saka a ranta yana ji ba, tunda ance ba a nan suke rayuwa ba. Gayen ya burge ta sosai, dan ya haɗu, irin ƙarshen haɗuwar nan. 


Ta ɗan yi ajiyar zuciya cikim nutsuwa ta ce, "Sunana Islaha daga toron guiwa tv, na zo nan dan na bawa Mr Rehaan invitation, da neman izinin hira dashi."


Ya ɗan buɗe ido da mamaki ya ce, "ya aka yi ki ka san Rehaan yana nan?." 


Ta ɗan yi murmuahi ta ce, "ban sani ba Sir, Chairman ne ya kira ni tun daren jiya, ya ce na shirya zuwa nan na haɗu dashi."


"Shi Chairman ɗin na ku ya aka yi ya sani?."


"I don't know Sir."


"You know, miss Islaha." 


Ta ɗan yi murmushi ta ce, "Sir in na sani bazan ƙi sanar da kai ba, ban san ya aka yi ya sani ba."


"Well, in baza ki faɗa min ba za ki iya tashi ki fita" ya faɗa yana nuna mata ƙofa. 


Islaha ta ɗan yi shiru, in ta fita ta rasa damar ta, sannan in ta faɗa masa ta zama maƙaryaciya. 


Ta ɗan yi murmushi ta ce, "zan iya zuwa na tambayi abokan aikina akan hakan? Amma sai ka bani dama" ta faɗa cikin muryarta mai sanyi tana kallon sa.


Ya ɗaga mata kai alamun ta je, ta yi godiya ta miƙe ta fita. 


Jazy ya girgiza kai ya ce, "Lallai akwai ƙaramin yaƙi, ashe har an san da labarin dawowarsa, duk wanda ya yi gangancin fitar da labarin nan shi da Rehaan" ya faɗa yana ƴar dariya sanin halin kayansa.


A hankali ta ɗan yi knocking sannan ta shigo da sallama, ta koma inda ta tashi ta ce, "An samu  maganar daga wajan P.A Bilal." 


Ya ɗan yi murmushi yana girgiza kai, sannan ya ɗauko waya ya kira Bilal ya saka a speaker.


Bilal yana ɗauka ya ce, "Good day Sir." Jazy ya ce, "gidan tv nawa ka bawa labarin dawowar Ray?." 


Bilal ya yi shiru bai ce komai ba. Jazy ya ce, "baka jin magana ko? Me ya ce maka a airport?." 


Bilal ya ce, "a yi haƙuri, na riga...." 


Ya katse sa ya ce, "ayi haƙuri dame Bilal? Sau nawa kana yi kana bada haƙuri, dan ka ga ina sakawa ya ƙyale ka ko?. Shikenan wannan tsakanin ku ne, bazan shiga maganar ba" kafin Bilal ya ce wani abu ya yanke wayar.


Ya kalli Islaha ya ce, "Miss ƴar jarida, kin samu labarin ya dawo jiya. Kuma sai ku zo interview yau?."


"no Sir, ba mun zo interview ba ne, mun zo mu yi inviting ɗinsa ne, duk lokacin da ya saka mana, a ko ina ne muna maraba da hakan. Mu dai burinmu ya amince mana ɗin." 


Ya ɗan kwanta a akan kujerar ya ce, "Kin san babu channel ɗin da ya taɓa hira dashi?."


Islaha ta ce, "shiyasa nake so na zama first presenter da zan fara interview dashi, ina mafarkin hakan a rayuwata  Sir." 


Ya yi murmushi, dan yanayin yadda take magana da ƙarfin guiwarta ya burge shi sosai. 


Jafar ya ce, "meyasa?."


"hira da Mr Reehan ba abu ne mai sauƙi ba, iya tattaunawa dashi babbar nasara ce a gare ni." 


Ya ɗan girgiza kai ya ce, "to kuma sai ga ki a zaune a wajan Jafar ba Rehan ba."


Ta sake yin murmushi mai kyau ta ce, "in na ga Mr Jafar kamar na ga Mr Rehaan ne. Wannan zama da na yi tare da kai shima babbar nasara ce, at least a tarihin rayuwata zan ce na zauna da Mr Jafaar har mun yi magana. Ina komawa gida, zan rubuta a diary na."


Ya girgiza kai tana jinjina girman wayonta, ba ƙarya ta iya aikinta sosai. Haka ake son ƴan jarida da iya harshensu, da iya sarrafa magana, sa amfani da yanayin fuskar wanda suke tare.


Ya ce, "ta ya dan kin ga Jafar zai zama kin ga Ray?."


"Saboda duk abu ɗaya, jini ɗaya ba wasa bane."


Ya yi murmushi yana jinjina ƙarfin wayonta, muryata ko rawa bata yi in tana yi masa magana, ko kaɗan babu tsoro a tare da ita. Aikin ya ratsa ta, ta ƙware babu da wanda baza ta yi hira ba.


Ta yi ƙasa da murya ta ce, "I've been here since 4 a.m. and haven't even had breakfast, just because I want to see your cousin. Please, ka bani damar ganinsa."


Da mamaki ya kalle ta ya ce, "dake muka haɗu za ki shiga elevetor ko?." 


Ta ɗaga kai ya ce, "ni ce." 


Ya ɗan yi murmushi ya ce, "kuma ba ki ga Rehaan ba?."


Ta girgiza kai ta ce, "ban gan sa ba, kana tare dashi?." 


Ya girgiza kai da mamaki ya ce, "kafin yanzu, kin taɓa ganin Rehaan?."


"Actually ina ganin hotunansa amma bazan iya cewa ga kamanninsa ba, in na ce ban san shi ba ban yi ƙarya ba. Wannan shine gaskiya."


"Good girl!" 


Ya furta yana girgiza kai jin ta faɗa masa gaskiya, dan tabbas ta ga Rehaam bata ganesa bane ba. Kuma gwara hakan, da ta tunkaresa da wata magana da an shiga tara.


"Miss Islaha yanzu dai Rehaan bacci yake yi, ko da ba bacci yake yi bazai amince ba. Kuma Bilal da ya ba ku labari zai koresa ne. Dan ba ya so ya faɗa ba a cika ba."


Islaha ta yi shiru bata ce komai ba. Jazy ya ce, "A taƙaice ban yi miki alƙawarin ganinsa a yau ba. Ba yau ba ma, gabaɗaya wannan zuwan bana tunanin zaki samu damar da ki ke so." 


Cikin rashin damuwa ta ce, "zan jira daga nan ko yaushe ne, burina da fatana ya amsa gayyata, ya amince na zama ta farko."


Jay ya ce, "Don't worry, ƙarfin guiwarki da nutsuwar ki, da gaskiyar ki ya burge ni. Dan haka na yi miki alƙawarin ke ce mace ta farko da Rehaa

Post a Comment

We welcome your thoughts! Please keep comments respectful, relevant, and free from hate speech, spam, or false information. Offensive or promotional content will be removed, and repeat offenders may be banned. By commenting, you agree to follow our Community Guidelines.

Previous Post Next Post