Sara da Sassaka Page 9 Complete by Ayshacool


 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

SARA DA SASSAƘA...

Ayshercool 

YOTA/002

P9

Aka kunna fitilar ɗakin, da sauri Alina ta rufe idanunta, saboda ba ta son haske idan tana wannan ciwon kan.

Nurse ce ta ƙaraso tana turo trolley. Ta ce "Yi haƙuri Alina, zan ba ki magani ne"


Ta gaida Mamman ya amsa, ya sake duban Alina ya ce "Kar ɓi ki sha kafin ta baki maganin"


Ta girgiza kai ba tare da ta ɗago kanta ba, ta ce "Ina Anty ta tafi?"


Nurse ɗin ta ce "Ta je sayo miki magani, ba a samunsa a nan haka"


Ya sake tausasa muryarsa ya ce "'yar ƙwalisa daure ki sha ko kaɗan ne"


Ya yi maganar yana ajiye mata a kan cinyarta. Idanunta a rufe ta fara laluben cokalin dan ta sha. Ya ɗebo ya kai bakinta. A hankali take karɓa, amma idonta a rufe. Kaɗan ta sha ta ce ta ƙoshi amai take ji, ba za ta iya ci gaba da sha ba. Nurse ta kama hannunta, ta buɗe cannula ta fara yi mata allura. Alina ta kawar da kanta gefe ta rintse idonta, saboda yadda ba ta son allura. Ya fakaici idonta, ya zura hannu a aljihunsa, ya ciro sirinji, ya kalli Nurse ɗin da idonsa, ta koma gefe ya kama hannun Alina, cire sirinjin da ta saka mata, ya saka wanda ya ciro a aljihunsa ya fara yi mata. A gigice ta buɗe idonta ta kalle shi.

Sai dai ba ta yi magana ba, jikinta ya saki ta fara bacci, a hankali ya gama zuba ruwan allurar a jikinta, sannan ya gyara mata kwanciyarta, ya kalli Nurse ɗin ya ɗaga mata babban yatsansa alamar jinjina.

Sannan ya yi mata alama da ta tafi. Ta juya da trolley ɗin ta fice. Ya ciro babbar waya a aljihunsa, ya ɗauki hotunan Alina.

Ya kwashe sauran kayan ya fice ya bar ɗakin da sauri.


Ba a yi mintuna goma da fitarsa ba, Nadiya ta shigo ɗakin, ta ƙarasa gaban gadon Alina tana faɗin. "Fatima, haryanzu ba ki tashi ba?" Ta yi maganar tana dafa goshin Alina.

Ta ajiye magungunan da ta sayo, sannan ta ciro wayarta da ke ta ringing.


"Hello masoyi"


"Na'am ya jikin nata?"


"Jiki Alhamdillah, tana ta bacci, ka san ƙa'ida sai ta yi kwana biyu tana fama"


"Na kusa shigowa garin ai nan da awa biyu in sha Allah"


"Wai dawowa zaka yi da gaske? Aikin fa"


Ismail ya ce "Kin san hankalina ba zai kwanta ba, ba na son ciwon kan nan da take yi, na kusa shigowa in sha Allah. Kin samu magungunan kuwa?"


"Eh na samo su, amma da kyar aka bani su, wai ba a sayar da su barkatai"


"To Alhamdillah, da ta tashi a bata ta sha, kuma su yi mata duk abin da yakamata, su tattara mini bills ina dawowa zan bayar, dan bana tunanin akwai isassun kuɗi a file ɗinmu"


Nadiya ta jinjina kai tana faɗin "Ai ka san ko babu ko sisi, za su yi mana duk abin da yakamata, sai ka ƙaraso"


Ya amsa da "To shikenan" Ya katse wayar.


*****


Tun da Baffa ya zo, Rahama ta rasa nutsuwarta gaba ɗaya, kanta har wani ciwo yake yi mata. Tabbas babban dalilin da ya sanya ta karɓi soyayyar Bukar, amfani da shi ne ta gano haƙiƙanin wace ce wadda aka tozarta mata ɗan uwa saboda ita. Amma daga baya ta fahimci kamar shi ma bai san wace ce ba, sai dai kyawawan ɗabi'unsa ya sanya ta saki jiki da shi, har take jin ta fara sonsa. Ta sake tuna maganganun da Saleh ya gaya mata. Ji ta yi tana son ta haɗu da Hanne ko ta halin ƙaƙa. Litattafan da suke gabanta ma, sai ta ture su a gefe, ta nemi guri ta kwanta saboda ba ta jin dadin komai.


Sai dai tana ɗarsa batun son Bukar a zuciyarta, sai mutumin nan ya bujiro mata, ya mamaye ko ina.


*****


Mariya na zaune tana goge uniform ɗin ta na Islamiyya.

Mama ta dube ta ta ce "Mariya, dan Allah idan kin je, ki ba wa malam haƙuri, in sha Allah a satin nan za ki kai kuɗin makarantar ya ƙara haƙuri"


"Tom zan gaya masa in sha Allah"


Hafsa ta shigo ɗakin da sallama tana cire hijjabinta.


Mama ta amsa ta dube ta ta ce "Yaya?"


"Na fita kenan Yaya ya kira ni, ya sako mini dubu uku, ya ce mu yi haƙuri mu lallaɓa, ya je wa Naja visiting shekaranjiya ba kuɗi a hannunsa"


Mama ta ce "Hafsa ba dai gaya masa ki ka yi cewa bamu da komai a gidan ba?"


"Haba Mama kema kin san ba zan gaya masa ba. Dama ba son zuwa gurin Kawu Babballen nan nake yi ba, da an taɓa shi shi ma cewa zai yi ba shi da shi, mu je yaya ya bamu"


Mariya ta ce "Ya ma haɗa ka da masifa ma"


Mama ta ce "Allah sarki yaron kirki, Ubangiji Allah ya tsare mana shi, ya yi masa jagora. Allah dai ya saka masa da alkhairi. Mariya kan ki tafi makarantar nan karɓo mana gari kowa ya sha, mu cancana kuɗin"


"To Mama" Haka ta ci gaba da yi musu addu'a da fatan, Allah ya haɗa mata kan su.


Miƙa ya ɗan yi, idanunsa jawur saboda gajiya, ya cire bindigarsa ya ajiye yana duba wayarsa.

"Haris yane? Ka zo mu je cin abinci, rana ta yi fa"


"Oga Suleiman ka je kawai, bacci nake ji ne"


"Kai Haris, bacci a yanzu, shikenan bari na je"


Haris yana jin yadda cikinsa yake ƙugi, saboda yunwar da yake ji, amma ya rage kayan jikinsa ya nemi guri ya kwanta.


*****


Alina ce ta yi shiru tana tunanin da gaske Mamman ya zo, ko kuwa mafarki ta yi? Cikin kulawa Yaya yake ta jera mata sannu cike da kulawa.


Ta jinjina masa kai, tana ƙara riƙe hannunsa a cikin nata.


"Sannu Alinan Yaya, Ubangiji Allah ya yaye miki wannan ciwon kai, ya yi miki maganinsa"


Suka amsa da Amin.


"To yanzu ya ki ke ji?"


Ta ɗan yi shiru ta ce "Kan ya daina ciwo, ni yanzu mu tafi gida kawai" Ta yi maganar da sigar magiya.


Ismail ya ce "A'a ki yi haƙuri ya ƙara sakinki tukuna"


Ta kwaɓe fuska ta ce "Yaya gobe in Allah ya kaimu Asabar, idan ba a ji karatuna ba, makina zai iya yin ƙasa a cire ni daga cikin yan sauka"


Nadiya ta ce "Alina ai larura tana gaban komai, ki bari dai mu gani"


Ta shagwaɓe tana yi musu magiya.


Ismail ya ce "Ina ganin hakan za a yi, tun da haka take so. Bari na je na ji nawa ku ka ci"


Nadiya ta ce "To shikenan"


Ya fito reception, suka gaggaisa da ma'aikatan, kasancewar sun san shi sosai, patient ɗin su ne, mussaman saboda yawan rashin lafiyar Alina.


Ya ce "Hajiya duba mini file ɗinmu, nawa ku ke bi na, nawa Alina ta ci?"


Aka ciro file, ya sake cewa "Ina ga wancan karon bai fi dubu uku ce ta yi saura a file ɗin ba"


Matar ta ɗaukko file ta duba, ta kalli Ismail ta ce "Ai ba a binku ko sisi, kun biya"


Ismail ya ce "Hajiya ya idon ne? Duba dubu uku ce a cikin file ɗin, sun kawo Alina kwanansu biyu yau. Ki ga nawa suka ci na saka muku yanzu" Ya yi maganar yana daddana wayar hannunsa.


"Da gaske fa nake, an biya har da canjin dubu talatin a file ɗin." Ya kalle ta, ya ja file ɗin gabansa ya fara dubawa. Shekaranjiya ranar da aka kai Alina Asibiti aka saka kuɗi dubu saba'in a file ɗin, kuma da sunansa a saka. Ya yi shiru.

Ya kira Nadiya a waya, ya ce ta zo reception. Ba a jima ba sai ga ta ta iso.


"Masoyiyya, waye ya biya kuɗin Asibitin Alina?"


Nadiya ta ce "A'a ba a biya ba"


Ya ce "To zo ki ga"


Ta ƙarasa ta kalli file ɗin, ta ce "Gaskiya ba su biya ba"


Aka kira wayar wanda ya yi duty ranar, ya ce ta POS kawai ya ga transfer, ya ga sunan Isma'il a jiki, da narration, dan haka ya yi setting bills ɗin.


Ismail ya yi shiru yana tunani, bai sake cewa komai ba, ya ce Nadiya ta haɗa kayanta su tafi.


*****


Babbar mace ce, za ta shekara Arba'in da uku, ta sha kwalliya, ta fito katafaren falonta, ta yi turus ta ɗan tsaya tana kallonsa.


"Baba Mai Kano saukar yaushe?"


"Ko na koma ne?" Ya yi maganar yana ɗan kallonta.


Ta gyara zaman gilashin fuskarta, ta ce "Wane mutum inji mutuwa, barka da sauka"

Bai amsa ba ya nufi fridge, ya buɗe ya ɗauko coc mai sanyi, ya ɗauki glass cup, a saman fridge ɗin, ya zuba ya sha. Ya dawo falo ya zauna. Ya dube ta ya ce "To kina lafiya?"


"Mmm ba gani kana gani ba, Alhamdillah na godewa Allah"


"Ya jikinki fa?"


Ta yi murmushi ta ce "Alhamdillah"


"Allah abin godiya. Amm na ce duk takardunki masu muhimmanci su na nan a ajiye inda na sansu ko?"


"Eh me za a yi?" Ya miƙe tsaye ya ce "Abu nake nema"


Ta dube shi ta ce "Me za ka yi ne?" ya yi gaba cikin hanzari ba tare da ya ce komai ba.


"Mai Kano me za ka yi ne wai? Kai ba ka zo gurin mutum ba, a yi ta maka magana ka mayar da mutum iska, ba za ka amsa ba"


Ya shige bedroom ɗin ta, wardrobe ya buɗe, ya din ga duddubawa ya ciro wata takarda, ya din ga kallon takardar a tsanake, daga bisani ya tashi ya mayar da wardrobe ɗin, ya fito falon ya tarar da ita a zaune, da remote a hannunta, tana canza tasha.


"Sai anjima" Ya furta yana nufar hanyar fita.


"Ina fatan baka hargitse mini ɗaki ba?"


"Ki saka a gyara miki" Ya yi waje da sauri.


BAYAN KWANA HUƊU.


Tun daga nesa ya zuba mata ido, har ta shigo cikin kantin nasa.


Guri ta samu ta tsaya tana hararsa.


"'Yar ƙwalisa, ya aka yi ne, ya jikin?" Ta murguɗa baki ta yi shiru.


Ya fito daga cikin kantin, ya zauna a gefenta a kan bencin da yake ciki.


"Me na yi miki ne?"


"Sau ɗaya ka zo duba ni, baka sake nema na ba?" Ta yi maganar tana tura baki.


Ya yi murmushi ya ce "Ki yi haƙuri, tsoron yayanki nake ji, kin san ba ya son alaƙata da ke, amma kina raina na damu sosai da sosai, kamar na cire miki ciwon".


"Ba wani nan" Ta yi maganar tana zumɓura baki.


"Da gaske nake 'yan matan Yaya"


Ta ɗan ɗago ta saci kallonsa, ya kashe mata ido, kawai ta hau dariya. Shi ma ya yi dariyar. Ya ce "Kin rame sosai, me yake saka miki ciwon kai haka?"


Ta gyaɗa kai ta ce "Nima ban sani ba, tun ina ƙarama, wani Likita dai ya ce Magrine headache sunan shi. Ka san ranar da ka zo duba ni ɗin nan, bayan ka tafi...


Ya katse ta da cewa "Waye ya zo duba kin?"


"Kai mana, lokacin da ina Asibiti fa"


Ya girgiza kai ya ce "A'a ban zo ba"


Ta yi saroro ta ce "Ka zo mana, na manta kalar kayan da ka saka, amma ka manta ka zo. Har ka kawo mini yoghurt"


"Ta yaya zan zo bayan yayanki yana yi mini kashedi a kanki"


Cikin mamaki Alina ta kalle shi, ta ɗan dafa kanta ta ce "To mafarki na yi kenan? Har ka ɗaga ni zaune fa, lokacin Antynmu ta je sayo mini magani"


Ya ce "Anya kin gama warkewa kuwa, ko dai a koma Asibitin nan? Gaskiya mafarki ne, yanzu me zan ɗaukko miki da za ki ci?"


Ta girgiza kai ta kasa cewa komai, saboda mamakin da ya cika ta.


Ta tashi tsaye ta ce "Ni ba na son cin komai, ga wannan" Ta yi maganar tana ba shi leda.

Ya saka hannu ya karɓa yana faɗin "Me na samu?" Ya buɗe ledar ya fito da abin da yake ciki.

Hankici ta saƙa mai kyan gaske, ta saƙa shi fari da ja, ta rubuta Ɗan albarka, sai kuma hular sanyi ita ma ta rubuta ɗan albarka a jiki. Sai uban ƙamshi suke yi. Sosai yake murmushi, ya ɗago ya kalle ta, ya tsare ta da idnaunsa, kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya ce "'Yar ƙwalisa, wannan duk nawa ne?"


Ta ce "Eh, ka din ga canza hula, tun da na ga kullum da hula ka ke zama, ko ka na da sanƙo ne?" Ta yi maganar tana dariya. 


Kawai ya yi wata 'yar gajeriyar dariya, jin abin da ta faɗa. Ya cire hular kansa, kansa cike da suma ya ce "Ba ni da sanƙo, ina dai saka hular ne ina rufe kaina"


"Eh na gani ka bani gyaɗa zan koma gida na yi bacci, magungunan nan bacci suke saka ni, duk su kashe mini jiki"


Ya miƙe ya ɗaukko bokitin gyaɗar ya ce "Ɗauki iya wadda za ta ishe ki"


Ta ɗauki ƙulli biyu ta ce "Wannan ta isa"


Ya kalli kantin, ya dube ta ya ce "Sai kuma me zan baki?"


Ta girgiza kai ta ce "Wannan ta ishe ni"


"Kai 'yan matan, na rasa me zan ce miki ne ma gaba ɗaya, amma na gode sosai da sosai Lina, Thank you in ji turawa. Nima yakamata ki din ga koya mini turancin nan"


Ta ce "To shikenan, zan din ga koya maka, amma ka daina wannan godiyar ta yi yawa. Ai ba zan biya ka ɗawainiyar da ka ke yi da ni ba"


Ya saki murmushi ga ta yarinya sai manyance, da iya tsara magana.


Ya ɗan lumshe idanunsa, yana nazartar fuskarta. "Ke ki ke ɗawainiya da ni ai, ki bani abinci, ki taya ni hira, ga kyauta kin bani, kuma... Sai kuma ya yi shiru.


Ta ɗaga kai suka haɗa ido, ta yi saurin sunkuyar da kanta ƙasa.


"Sai ka ce na baka wata duniya, ai ba yawa,na gode nima" Ta fice daga kantin, tana tafiya a hankali. Ya zura mata ido, har ta ɓacewa ganinsa.


*****


"Sadauki"


"Allah ya taimaki Madugu"


"An gama saita komai?"


"Na gama Madugu, umarninka kawai muke jira"


"To ku jira ni daga yanzu zuwa kowane lokaci, ku saurare ni, ina jiran a gama gyara mana hanya ne, saboda ba a son kuskure a aikin, sama ta ka zamu kai mamayar"


Sadauki ya ce "Allah ya bar Kacalla Sumale, kai mu ke saurare"


"Good"


*****


Sosai ya zuba wa kayan da Alina ta ba shi ido, yana murmushi.

Ya din ga jujjuya hular, ta saƙu sosai da sosai, sai ƙamshin turare take yi, ga handkachief ɗin ma ya yi kyau sosai, har beza ta yi masa da wani abu mai ƙyalƙali. Ya kai hancinsa ya shaƙi ƙamshin turaren da suke yi, irin wanda take yi ne. Ya yi murmushin gefen baki, ya haɗe su a guri ɗaya, ya ɗaga ƙasan kayansa ya saka su.


*****


YELWA 


Tarin makiyaya ne maza, dattawa da matasa, su na zazzaune, a kan wata ƙatuwar tabarma, su na tattaunawa.


Moddibo da ya kasance shi ne jagora a ɓangren makiyayan garin, ya yi gyaran murya yana magana "To tunatarwa ce dai da muka saba yi duk shekara, yanzu ma ga mu mun zo da ita.

Mun san wasu za su dawo da dabbobi gida, wasu kuma za su fita da su. To ga kuma labarai marasa daɗi da muke samu, ga kuma rigimgimun cikin garin nan. Saboda haka nake roƙonku, duk inda za ku je, ku kasance mutanen kirki, duk inda ku ke ku wakilan makiyaya ne, makiyayi kuma ba a san shi da tashin hankali da neman rigima ba. Domin girman Allah ku kula da dabbobi, kar su shiga su yi wa kowa ɓarna. Sannan wanda za a bari a gari, kuma ina roƙon waɗanda za a bari a gida, kowa ya kula da dabbobinsa, kar ya bari su shiga gonar wani su yi ɓarna.

Hausawa sun ce; kowa ya kwana lafiya shi ya so. Kun san mutanen nan sun fi ƙarfinmu ta kowacce fuska, tsokanarsu ko neman rigima da su, ba zai haifar mana da ɗa mai ido ba. Mu na sane da tabon da yake zukatanmu, na cutarwa da suke yi mana, da har abada ba zamu warke ba, dan haka kowa ya kula dan Allah"

Duk suka amsa masa da In sha Allah. "Ko akwai mai magana"


Baffa ya ɗaga hannu, Modibbo ya ce "Mu na saurarenka Jibo"


Baffa ya miƙe ya ce "To 'yan uwana Assalamu alaikum, ni ɗorawa zan yi abin da ka faɗa. Mu na jin yadda al'amuran rikicin manoma da makiyaya ke komawa wani abu daban. Duk ma'abocin jin radio, ko wanda yake shiga birni, na san yana da labarin hakan. Saboda haka nake sake roƙonmu mu ƙara kulawa sosai, dan kamar jira suke yi wani abin ya haɗo mu ma su far mana. Sannan duk wani abu da muka gani baƙo da bamu yarda da shi ba, mu sanar da junanmu...


Ɗan uwan Baffa  ya ce "Dan Allah Modibbo, idan an gama taron nan mu tafi, ya tashi sai iyayi yake yi mana. Koma mene ne ba ɗanka ne yaje ya tsokane su ba, ya ƙara tayar mana da tsohuwar gabar nan ba, da bai je inda 'yarsu take ba, ai da abin bai ƙara tsauri ba."


Wani a gefe ya ce "Gaskiya ne, yo mutumin da bai iya kula da gidansa ba, ya ɗauki yarsa ya kai wata uwa duniya ne, zai wani tashi yana mana surutu da sunan shawara?"


Sai jikin Baffa ya yi sanyi. Maddibo ya tsuke fuska ya ce "Jatau, Iro meye haka? Iro da aka kashe mana, ai ba Jibo kawai aka yi wa ba, mu aka yi wa. Kisan gillar da aka yi masa zuriyar makiyaya aka yi wa. Kuma ba domin mu na son zaman lafiya ba sai mun bi kadin jinin iro. Batun kai Ramata birni wannan abu ne da shi ya shafa. Mu na jinka Jibo ci gaba da magana"


Baffa ya girgiza kai, fuskarsa ɗauke da murmushin ƙarfin hali, ya ce "Ahh dama shikenan maganar tawa, na gode" Ya nemi guri ya zauna yana yaƙe.


****


"Vice"


"Ranka ya daɗe"


Ya yi taku biyu da sanda a hannunsa, ya nemi guri ya zauna, ya ɗaga idanunsa, ya saka a cikin na kan Kangiwa.


"Na san ka san faɗin tashin da muka yi, muka kawo ku kan mulki ko?"


"Na sani Allah ya baka yawan rai"


"Masu iya magana sun ce, ɗan halal baya manta alkhairi, sai dai farawa da bismillah, Kankiya yana ƙoƙarin nuna mana, an tura motar zai bule mu da hayaƙi, ba tare da sanin direban da yake tuƙin motar namu ne ba. Tun da ya nuna zai mana butulci, ba zai yi mana biyayya ba, zamu yi masa yaren da zai gane. Idan ka amince ka bamu haɗin kai ɗari bisa ɗari, zamu mayar da shi fanko, ka jagoranci ƙasar, zuwa lokacin zaɓe mu hankaɗe shi, kai mu ɗora ka."


Cikin mamaki yake kallon Makama, murya na ɗan rawa ya ce "Ta yaya hakan zai faru ranka ya daɗe?"


"Wannan aikinmu ne, kai dai ka zama mai biyayya kawai, idan ba haka ba daga kai har shi, zaku rasa zamu nemo wanda za mu tsayar, dan ba za ku yi tazarce ba, dabara ta rage ga mai shiga rijiya. Idan ka shirya ka amince, zamu hargitse ƙasar kai kuma ka ji da sauran...


Ayshercool 

08081012143




AMANA KAYAN MATAN

Ingantattun magungunan mata 'yan sokoto.


Ina kuke manyan mata, mata ƴan ƙwalisa, ba muna mata ba. Ku zo maza ku garzayo mun zo muku da babbar harka ta ingantattun magungunan na mata. Ina macen da take son burge mai gidanta? Ina wadda take son zama shalele a wurin mijinta? Ina macen dake son zama ƴar gata a wurin Oga? Ina wadda take son mijinta ya yi alfahari da ita, kullum yana riritata kamar ƙwai? Ina macen da ta samu matsalar ƙaruwa a wurin haihuwa? Ina wadda sanyi ya yi mata yawa ta buɗe? Ina macen da take da ƙarancin ni'ima a jikinta? Ina wadda take jin zafi a wurin saduwa? Hajiya kin taɓa amfani da maganin da zai matse ki ya mayar dake tamkar buduwa? Ko har yanzu kina nan a buɗe kamar bakin gari? To muna masu farin cikin sanar daku mun zo muku da ingantattun magungunan gyaran jiki na mata masu kyau da inganci kamar su..


Gumbar madara 

Gumbar mata

Gumbar aya 

Gumbar chaku 

Gumbar dake saukar da ni'ima

Gumabar taƙadari

Gumbar riɗi 

Gumbar dabino

Gumbar uku alkhairi 

Kazar amare

Jijjiɓen saniya

Tabaje

Tsimi

Rikita mai gida

Jigidar tada sha'awa 

Ruwan boom ruwan daɗi kenan

Ɗan matse

Karya gado

Maganin sanyi

Zumar ƙarin ni'ima

Zumar rage ƙiba

Zumar ƙarin ƙiba

Zumar riɗi

Mai zamani

Emergency powder 

Tarhama 

Kafi budurwa

Sabon budurci

Alfijir

Gamzaki

Garin dahuwar nama

Sabaya

Miskin ɗahara

Da dai sauran su. Namu ba irin na su bane, bamu fito ba sai da muka shirya, muka tabbatar da kwaliti da inganci kayanmu. Ƴar uwa gyara shi ne mace, aka ce ko kina da kyau ki ƙara da wanka, ina matan dake cewa ba sa shan kayan mata iya fruit kawai suke sha? To ku sani ko wane allazi da amanun sa, aikin fruit daban, aikin waƴan nan daban. Hajiyata ki saki jiki kawai ki zo musa labule, a gwangwaje ki da kayan da zaki rikita my house da su. Ki susuta shi, ya zamana duk inda yake kina maƙale a cikin ƙalbinsa. Matuƙar kika yi amfani da kayanmu, ina mai tabbatar miki da ba boka, ba malam za ki mallaki mijinki ciki ruwan sanyi, sai yadda kika yi da shi. Ga mai buƙatar kayanmu zai iya tuntuɓar waƴan nan lambobin 08163516796 ko 08081012143 muna aika saƙon mu a ko'ina.

Post a Comment

We welcome your thoughts! Please keep comments respectful, relevant, and free from hate speech, spam, or false information. Offensive or promotional content will be removed, and repeat offenders may be banned. By commenting, you agree to follow our Community Guidelines.

Previous Post Next Post