https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
*MORE PAGES AVAILABLE AT AREWAPEN*
*Masu nema daga farko, su duba cikin channel link ɗin nan*
SARA DA SASSAƘA...
AYSHERCOOL
YOTA/002
Page 8
Sannu a hankali ya ajiye wayar, jikinsa na ci gaba da tsuma, ya tashi tsaye a hankali yana waige-waige, ya ga ko zai hango wani a gurin, da ko shi ne ya bayar da rahoton zuwan matashin, amma bai ga kowa ba. Zuciyarsa ta raya masa haɗin baki ne, ana sane aka turo shi, dan a gani ko zai faɗi wani abu ko ba zai faɗa ba. Ya sanya hannu ya ɗauki Alqur'aninsa ya tafi yana ta istigfari.
*****
Tana tsaye daga nesa da shagonsa kaɗan, ya buɗe ƙofar ya tsaya yana kallonta. Doguwar riga ta saka, da wani ɗan ƙaramin mayafi, hannunta riƙe da flask ɗin Abinci. Tun kan ta ƙarado, ƙamshin turaren da take yi, ya karaɗe ilahirin gurin. Ta saka jam baki a bakinta, idanunta kuma ta saka kwalli.
"Ɗan Albarka"
"Mmm 'yar ƙwalisa"
Ta yi murmushi ta ce "Bacci ka ke yi ne?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.
"Me ki ka dafa mana ne yau?"
"Buɗe ka gani" Ta yi maganar tana miƙa masa flask ɗin Abincin, ya karɓa ya buɗe, ya ga tuwon shinkafa da miyar wake. Ta miƙa masa ledar hannunta ta ce "Ga zoɓo mai muslmin sanyi kuma"
"Na gode sosai 'yar ƙwalisa"
Cikin jin nauyinsa ta ce "Nima na gode, sai anjima"
Ya ɗan yi gyaran murya ya ce "Ina kuma za ki je?"
"Zan je titi ne sayo wa Antynmu abu"
"'Yan mata mayafin nan ya yi ƙarami fa, ana ganin jikinki. Kuma ga shi kin yi kyau sosai da sosai"
Ta rufe fuska ta ce "Dan Allah ka daina bani kunya mana"
"Hmm ba kunya nake baki ba, gaskiya na faɗa, kuma mayafin nan ya yi kaɗan, ba ki san kin fara girma bane?"
Ji ta yi tamkar ta nutse saboda kunya da ta mamaye ta. Ta ɗan kwaɓe baki ta ce "Yanzu zan dawo fa" Ta yi maganar a ɗan shagwaɓe.
"A dawo lafiya, na gode sosai da abinci" Ta juya ta tafi, ba tare da ta sake cewa komai ba.
Yana zaune bayan ya gama cin abincin, ya jiyo hayaniya a waje, sarai ya ɗauki muryar Isma'il sai bala'i yake yi, har ya basar saboda ya riga ya fuskanci Ismail masifaffe ne lamba ɗaya. Sai dai tuna cewa ba a jin kansa, idan ba Alina aka taɓa ba, ya sanya ya tashi da sauri ya leƙa.
Aikuwa kamar yadda ya yi tsammani, wani matashi yake yi wa hargowa, tun daga titi ya gano shi, ya bi Alina yana yi mata ɗan kira, ya biyo su a babur sai da suka shigo cikin layi, ya rutsa su yana zazzaga wa matashin bala'i. Tuni mutane suka taru su na ba wa Isma'il haƙuri. Alina kuwa yanayin fuskarta ya nuna rashin jin dadin tijarar da yake yi wa matashin, ga jama'a ya tara musu, sai ɗaga murya yake yi. Takaici ya sanya ta wuce gida ta bar su a gurin.
Da kyar aka ba shi haƙuri, matashin ya tafi.
Mamman ya girgiza kai kawai yana murmushin gefen baki.
Kamar guguwar baƙin hadarin kaka, haka Ismail ya shigo gidan yana ci gaba da bala'i.
"Wallahi Alina idan ba ki kiyaye ni a kan gayyar mazan nan da suke bibiyarki ba, a gabansu zan naɗa miki duka wallahi. Ke ba ki san halin da ƙasar nan ke ciki ba na rashin tsaro, kowa ba abin yarda ba ne, amma da yake kin fi kowa mutunci kowa sai ya biyo ki yana yi miki surutun banza kina washe baki, mara hankali kawai da ba ta san ciwon kanta ba"
"Yaya wallahi ban san shi ba, biyo ni kawai fa ya yi"
"Rufe mini baki ina magana kina magana" Yadda ya yi maganar cikin ƙaraji, ya sanya babu shiri, ta shige bayan Nadiya tana ɓuya.
"Ki ci gaba kar ki fasa. Wataran sai kin janyo mana abin da ya fi ƙarfinmu, ko tilasta mana komawa inda muka fito yadda mu ma za a kashemu kamar yadda aka kashe iyayenmu. Shi kansa wannan ɗan iskan da ki ka saki jiki da shi kamar ubanki, ki ka liƙe masa kallonki kawai nake yi. Gaba ɗaya mutumin nan da ganinsa ka san munafuki ne ba shi da gaskiya. Ƙirarsa da idonsa duk na miyagun mutane ne, babu ta inda ya siffantu da wani almajiri, amma kin liƙe masa, na rasa uwar da yake gaya miki. Amma za ki ga matakin da zan ɗauka a kanku"
Alina ta fashe da kuka, Nadiya ta rungume ta ta yi ƙasa da muryarta ta ce "Ki daina kuka rabu da shi, ya yi faɗansa ya gama, kar ma ki sake kare kanki, ƙyale shi"
Bayan fitar Ismail Alina ta ce "Antynmu ni shikenan haka zan zauna, yaya ya korar mini ƙawaye, ya hana ni hulɗa da kowa? Kuma wallahi Mamman mutumin kirki ne, ai kema kin san ba zan je inda zan lalace ba, ai ina bin nasiharku ba zan baku kunya ba. Kuma ni ba saurayina bane"
"Na sani Alina, amma duk wanda zai so mu, ba zai kai yadda Yaya yake sonmu ba. Duk abin da yake yi, yana yi ne, domin ya bamu kariya kar wani abu ya cutar da mu, ki yi haƙuri wataran sai labari" Alina ta jinjina kai.
"Alina" Nadiya ta kira sunanta tana nazartarta.
"Na'am"
"Son Mamman ki ke yi ko?"
Alina ta ɗago da sauri ta ce "So kuma? Haba Antynmu, ni wallahi ba son shi nake yi ba, kina ganin mutuncin da yake yi mini, ni kawai dai mun saba ne. Yana da kirki kuma yana koya mini karatu"
Nadiya ta jinjina kai tare da yin murmushi ta ce "Shikenan tashi ki je"
Ismail kuwa yana dawowa daga sallar isha'i, ya manta da faɗan da ya yi wa Alina, sai da bai ganta a tsakar gida ba, ya tambayi Nadiya ta tuna masa ai ta yi bacci tun faɗan da ya yi mata.
Bayan kiran sallar asuba na farko, Mamman ya buɗe ƙofar ɗakinsa domin kama ruwa ya yi alwala, kawai ya yi tozali da Isma'il a tsaye kamar bayyanar aljan.
A tsorace ya ce "Lafiya kuwa?" Ya yi maganar yana kallon Isma'il.
"Ba lafiya ba, gurinka na zo"
Ya ajiye butar hannunsa, ya ce "Allah ya sanya ba laifi na yi ba"
Ismail ya ce "Na je gurin mutumin da aka ce ka yi karatu a hannunsa, ya tabattar mini da kai ɗalibinsa ne, sai dai Haryanzu ni ban ji na yarda da kai ba. Amma na san komai girman gona akwai kunyar ƙarshe. Na fuskanci amfani da ƙarfi gurin raba ka da kanwata, zai iya zama cutarwa a gare ta, ka yi amfani da yaudara ka sanya kusanci tsakaninka da ita. Kuskure mafi girma da za ka yi shi ne fara soyayya da Alina, na kuma fuskanci idan ban yi da gaske ba abin da zai faru kenan. Ka sani akwai layin da idan ka ƙetara a kan Alina zan iya sadaukar da rayuwata na yi zaman prison na har abada saboda ita"
Mamman ya kalli Ismail ya yi murmushi ya ce "Ban san dalilin da ya sanya ka tsane ni har haka ba. Ni da Alina zaren ba kalar yadin bane ba, kawai mutumtaka ce a tsakaninmu. A ɓangarena na yi maka alƙawarin, kare martabar Alina, ba zan faɗa soyayya da ita ba, sai dai ban yi maka alƙawarin hana ta sona ba" Wani mugun kallo Ismail ya yi masa ta hasken fitilar solar gurin, ya yi ƙwafa ya juya ya bar gurin.
Gari ya fara haske, Ismail ya yi sallama a ƙofar ɗakin Alina, ta amsa masa murya ƙasa-ƙasa. Ya ɗaga labule ya shiga. Ta tashi zaune daga kwancen da take, ya zauna a gefen katifarta yana kallonta.
"Alina fushi ki ke da ni, ko gaisuwa ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a zan gaishe ka, tsoro nake ji, kar na je wani laifin na sake yi ne"
Ya ɗan jinjina kai, tare da kaɗa ƙafafuwansa da ya miƙe, ya ce "Ƙanwata, na san maybe kin yi fushi da Yaya, amma duk abin da Yaya yake yi, ƙoƙari yake bawa halittu mafi soyuwa a gare shi kariya, wato Fatima da Nadiya, a duniya yanzu ba ni da kamar ku, gurin baku kariya daga duk abin cutarwa, sai inda ƙarfina ya ƙare.
Ke yarinya ce Alina, haryanzu ba kya banbance mene ne daidai da akasin haka, kuma kina kan shekaru mafiya hatsari na ruɗin ƙuruciya, zuciyarki a buɗe take, duk abin da ya yi mata daɗi, ko ya burge ta, karɓa za ta yi. Shiyasa nake taka tsantsan gurin tantance miki aya da tsakuwa. Ni gaba ɗaya mutumin nan bai yi mini ba, yana da sifofin munafukai marasa gaskiya. Amma ba na son ɓata miki rai shiyasa nake ta saka muku ido. Ki yi haƙuri faɗan da na yi miki, amma ki yi a hankali kar ki kawo mana abin da zai kawo mana barazana ga kwanciyar hankalinmu."
Har ya yi magana ya gama, Alina ba ta ce uffan ba, ya tashi ya fita.
Gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi, ba ta son abin da za ta ɓata wa yayanta rai, amma gefe guda sun shaƙu da Mamman, rana tsaka ta daina kula shi ba ta kyauta ba. Ga shi gaba ɗaya cikin abin da bai fi wata ɗaya da satuttuka ba, suka yi wannan shaƙuwar.
*****
Ruƙayya ce ta ƙura wa Rahama ido, yadda take ta juya abu a kofi ta kasa sha.
"Rahama ya ne? Me yake damunki ne?"
Ta ɗago ido ta kalli Rukayya, ta sunkuyar da kanta.
"Ke kalle ni, mene ne?"
Ta girgiza kai alamar, babu komai.
"A'a da komai, mene ne?"
"Baffa bai zo ba, bai kuma kira kowa ba a gaya mini dalilin rashin zuwan nasa, a tsorace nake" Ta ƙarasa maganar hawaye na cika mata ido.
Ruƙayya ta ce "Haba Rahama, wataƙila wani abin ne ya hana shi zuwa, amma da yardar Allah zai zo"
Rahama ta ɗan rausayar da kai ta ce "Duk da ƙaunar makaranta da nake yi, a duk lokacin da na taho, hankalina a tashe yake. Saboda rashin sanin abin da yake faruwa a garinmu. Garinmu babu cikakken zaman lafiya da kwanciyar hankali".
Rukayya ta dafa kafaɗarta ta ce "Babu abin da yake faruwa sai alkhairi. Share hawayenki ki gama ci, ki zo mu je Clinic akwai marasa lafiya" Ta jinjina kai ta kammala abin da take yi suka bar Hostel ɗin.
A clinic ɗin suka tarar da wata ɗaliba da ƙofa ta ji wa rauni, zai yi mata ɗinki. Yana ganin Rahama ya hau murmushi ya ce "Ai yanzu nake saka ran na aika a nemo mini ke, na ga yau ban ganki ba"
Ruƙayya ta ce "Yaushe za ka ganta, tana can tana shagwaɓa, wai Baffa bai zo mata visiting ba, tun da yan gidanmu da suka zo mata dodanni ne"
Ya ɗan yi dariya ya ce "Ai ba a shiga tsakaninku, ina ga idan ki ka yi Candy sai kin jira Rahama"
"Wannan dole ne" Ta yi maganar tana dariya ta wuce ɗakunan da ake ajiye ɗalibai idan ba su da lafiya"
Rahama kuma a gefen Likitan ta zauna, tana ci gaba da yi masa tambayoyi kamar yadda ta saba.
*****
Misalin ƙarfe biyu da rabi na dare, yana tsaye a jikin tagar ɗakinsa, yana shan sigari, ya sha ta kai uku. Sannan ya dawo ya canza kayan jikinsa, zuwa shirt da dogon wando, ya samu wani mayafi, ya rufe fuskarsa, ya ɗaga ƙasan fulonsa, ya ɗauki abun da zai ɗauka, ya ɗau ƙaramar wayarsa, da wata wallet, ya rufe ɗakin ya fita.
Da safe Ismail na kallon Alina nata rawar jikin kai wa Mamman Abincin safe, wanda da wani abin ne ya nuna baya so, da tuni ta bar abin, amma nasihar da ya yi mata ba ta shige ta, dan bai ga alamar za ta ja baya da hulɗa da mutumin nan ba. Shi dai fargabarsa ɗaya kar Alina ta faɗa soyayya a shekarun ƙuruciya, mussaman da mutum irin wannan da haryanzu ya kasa nutsuwa da shi.
Ba ta fi mintuna uku da fita ba ta dawo, tana faɗin "Antynmu ga Abincin Mamman, baya nan ko ina ya tafi da sassafen nan, idan ya dawo ya ƙwanƙwasa miki ya karɓa, ko ki aika masa idan ɗan malam ya zo karɓar nasa" Ta ƙarasa maganar tana ɗaukar jakarta.
"Yayanmu na tafi" Ya ɗaga kai ya kalle ta, ya yi shiru bai amsa ba.
Ta ɗan tsaya cak tana kallonsa, ta sake cewa "Yaya na tafi"
"Sai kin dawo" Ya furta a taƙaice, jiki a sanyaye, Alina ta fita. Sai ta ji gaba ɗaya duniyar ta yi mata babu daɗi, ganin fushi da damuwa ƙarara a fuskar Yayanta.
*****
Rahama na zaune a class ɗin su, kasancewar lokacin prep ne, tana zaune tana karanta wani littafi, da yake ƙunshe da yadda turawan mulkin mallaka suka mamayi Afrika, da sace musu wasu daga kayan tarihinsu, da kuma mallke musu kadarorinsu. Kawai ta din ga jin zafin abubuwan da suka gudanaz saboda yadda ta yi zurfi a karatun gani take kamar a gabanta abin ya faru.
"A Yelwa" da sauri ta ɗaga kai.
Prefect ɗin da ta kira sunanta ta ce "Ki je ofishin pc ana neman ki"
"Tom"
Ta amsa tana tattare litattafanta tana zuba wa a cikin jakarta, ta yinƙura ta tashi ta fita. Hannunta na cikin hijjabinta tana tafiya a hankali.
Muryar Baffa ta jiyo, su na magana da principal ɗin su. Da sauri ta ƙarasa cikin ofishin. Murmushinta ya gaza ɓoyuwa. Ta gaisa da Principal sannan Baffa ya fito suka keɓe.
"Baffa na zata ba za ka zo ba, hankalina a tashe na fara tunanin ko wani abin ne ya faru a gida"
Jikin Baffa a sanyaye ya girgiza kai ya ce "Babu abin da ya faru, sai dai tsoron faruwar tasa ne ya sanya na kasa zuwa ko ina."
Rahama cikin kaɗuwa ta ce "Baffa mene ne?"
"Ramata dama akwai wata alaƙa a tsakanin ki da yaran manoma ban sani ba?"
Ras gaban Ramata ya faɗi, ta hau tambayar kanta, ya aka yi Baffa ya sani, duk ɓoye-ɓoyen da take yi.
"Kin yi shiru Ramata, ke yanzu ba kya duba mana halin da muke ciki ko? Sai kin janyo ke kaɗai ɗin da ki ka rage mini, kema na rasa ki ko wata fitinar ta tashi ko?"
Ramata ta yi ajiyar zuciya, ta gyara zamanta ta ɗan kalli Baffa ta sunkuyar da kai ta ce "Baffa abin da ka faɗa ba ƙarya ba ne, Bukar ya daɗe yana bibiyata tun ƙawancen da nake yi da Hanne. Sai dai na saki jiki na ba shi dama ne, ba domin komai ba, sai dan na san wacece wadda ake zargin Ironmu a kanta, na tattara hujjar da zan bi hakkinsa" Ta ƙarasa maganar tana kallon Baffa.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Ramata yaushe ki ka koyi baƙin taurin kai haka? Ni da nake ubansa na haƙura na fauwwala wa Allah, ke da ba ke ki ka haifar mini shi ba, ki dage sai kin ɗauki mataki, a gurin wa za ki ɗauki matakin? Ramata kar ki ɓata mini rai , ki yi abin da za ki janyo mana tashin hankali, ba zan iya kirga iya tashin hankali da barazanar da na gani a rayuwata a zamana a garin nan ba, yakamata na huta haka"
Rahama ta yi shiru tana goge hawaye, saboda yadda komai yake dawo mata tun daga cikin kwanyarta har zuwa cikin idanunta. Baffa ya koma yi mata nasiha, ya bata abin da ya riƙo mata ya tashi ya tafi.
Gudun kar hankalin malamansu ya dawo kanta, a zo ana tambayarta lafiya, ko su zata kukan tafiyar Baffa take yi, su yi mata faɗa, dan haka ta goge hawayenta ta tashi ta tafi. Sai dai da aka tashi daga prep, ta kai kayan kwanarsu ta ajiye, ta tafi keɓanttacen guri ta zauna tana tunani.
Tabbas tana son bin jinin ɗan uwanta, amma ta fuskanci yanayin shari'a a ƙasar nan ka na buƙatar ilimi, kuɗi da kuma hanya, idan ba haka ba wahalar banza za ka yi ta sha, idan ba Allah ya tarfawa garinka nono ba. Mussaman ita da ga ƙarancin shekaru kuma ba ta da tabbacin samun cikakken haɗin kan mutanen garin, kowa cewa zai yi babu ruwansa saboda tsoron manoma da ake ji a garin.
*****
Yana riƙe da leda a hannunsa, yana ƙoƙarin shiga layin, ya ga daidaita sahu na ƙoƙarin fitowa, da Alina a ciki a kwance a jikin Nadiya. Da sauri ya tare a daidaita sahun ya riƙe ƙarfen yana kallon Nadiya ya ce "Lafiya kuwa?"
Nadiya ta ce "Alina ce babu lafiya za mu je Asibiti"
A ɗan rikice ya ce "Subhanallah, Asibiti kuma meya same ta"
Cikin basarwa Nadiya ta ce "Tana da ciwon kai mai tsanani ne, mai Napep mu je, kar ta ci gaba da galabaita" Mai baburin ya ja suka tafi. Mamman ya tsaya yana bin adaidaita sahun da kallo, da tunanin ina yayanta za su tafi Asibiti sukaɗai? Kuma kwanaki uku kan ya yi balaguron da ya yi, lafiyarta ƙalau.
Wayarsa ya ɗaukko mai madannai, ya daddana, sannan ya ƙarasa shagonsa ya shiga.
Ya gama abin da zai yi ya fito ya zauna a bakin hanya, ko zai ga dawowarsu, amma bai gani ba, dan ya yi mamaki a yadda yake da Alina, babu yadda za a yi ya yi magana ba ta ɗago ba.
Wata maƙwabciyarsu, da take jikin gidansu Alina, ya gani ta fito daga layin, ta riƙo kwando da kwanukan Abinci. Ya tashi ya ƙarasa, suka gaisa. Ya ce "Dan Allah Asibiti za ki jegurin su Alina?"
Ta ce "Eh zan kai musu Abinci ne"
Cikin damuwa ya ce "Subhanallah, wane Asibitin ne?"
"Bright ne, a can suke kwanciya idan ba su da lafiya"
"Dan Allah kar ki ce na dame ki, dama tana yawan rashin lafiya ne?"
Maman Hanan ta ce "Gaskiya dai dan kwana biyu ma Alina ta yi lafiya, amma tana da yawan rashin lafiya"
Ya jinjina kai ya ce "Shikenan na gode sosai"
Alina na kwance a kan gadon Asibiti, Idanunta a lumshe, ɗakin an kashe fitila, saboda ba ta son haske, idan ciwon kan ya tayar mata.
"'Yar ƙwalisa" Ya kira ta a hankali.
A hankali ta motsa ta buɗe idanunta a saboda hasken fitilarsa da ya haske mata fuska. Sai dai idonta ya yi ja sosai.
"Sannu" Ya furta yana ƙasa da muryarsa. Ta mayar da idanunta ta lumshe, ta ce "Ina ka tafi babu sallama, nake ta neman ka?" Ta yi maganar cike da kasala da rashin ƙwarin jiki.
"Na je gida ne, kin san Innata ba ta da cikakkiyar lafiya ita ma."
Ta jinjina masa kai kawai.
Cikin tausasawa ya ce "Me yake yi miki ciwo ne?" Ta ɗaga hannunta a hankali, ta nuna masa kanta. Kawai ta ga ya saka hannu yana share mata gumin da yake tsatstsafowa a goshinta. Ta buɗe idanunta tana kallon fuskarsa ta hasken fitilar wayarsa. Ji ta yi zuciyarta ta fara bugawa da sauri da sauri, har numfashinta ya fara fita da sauri.
Idanunsa da suke ba ta tsoro ya tsare ta da su. Ga kusancin da yake tsakaninsu, wani irin ƙamshi jikinsa yake fitarwa mai kwantar da hankali. Hakan ya ƙara sanya mata kasala da wasi-wasi.
"Yaya Mamman" Bai amsa ba sai kallonta da yake yi.
"Ƙamshin turare ka ke da ƙaurin wani abu, kamar... Sai kuma ta yi shiru."
Ya ɗan ja dogon hancinsa, ya basar, ya ce "Tashi zaune ki ci abin da na kawo miki" Kafin ta yinƙura ya riga ta ya ɗaga ta zaune.
"Wayyo Allah kaina, ka yi mini a hankali mana, zai rabe biyu" Ta yi maganar muryarta na rawa.
Ya jinginar da ita, sai dai gaba ɗaya a tsorace take, idan ban da Yaya babu wani namiji da ya taɓa gangancin kai hannunsa jikinta, ko da kuwa samun kusanci da ita ne. Bayan rashin ƙwarin jiki da take fama, wani irin yanayi take ji a jikinta da ya ƙara kashe mata jiki fiye da da.
Ya janyo ledar da ya zo da ita, ya fito da yoghurt, ya fito da fruit, ya ce "Wanne za ki ci?" Tsura masa ido ta yi, tana tsoron kar wani ya shigo ya gan su a haka, saboda yadda yake zaune daf da ita, gaba ɗaya a tsorace take. Ta zuba wa wuyansa ido, idan ba gizo idanunta suke yi mata ba, sarƙa ce a wuyansa, sai dai ba ta fitowa sosai, tana cikin rigarsa, tana son ta yi magana amma ta kasa.
Ya ci gaba da bin ta da kallo, da mamakin abun da yake gani a tare da ita.
Ya buɗe robar yoghurt ɗin ya ce "Na baki a baki ne?" Ya yi maganar yana kallon ta. Laɓɓansa take kallo a hankali, kamar yau an canzo shi gaba ɗaya. Idan su na magana bai fiye son su din ga haɗa ido ba, kuma yana ƙoƙarin kiyaye duk wani abu da zai sanya ko hannunta ya taɓa, ko zama ta yi yana nesa da ita, amma yau kamar zai rungume ta. Ba haka ba hatta muryarsa tamkar an canza ta. Muryar ta ƙara buɗewa, kuma babu alamun wasa a cikin muryar tasa.
Babu tsammanni su ka ji an buɗe ƙofar ɗakin gaba ɗaya.
AMANA KAYAN MATAN
Ingantattun magungunan mata 'yan sokoto.
Ina kuke manyan mata, mata ƴan ƙwalisa, ba muna mata ba. Ku zo maza ku garzayo mun zo muku da babbar harka ta ingantattun magungunan na mata. Ina macen da take son burge mai gidanta? Ina wadda take son zama shalele a wurin mijinta? Ina macen dake son zama ƴar gata a wurin Oga? Ina wadda take son mijinta ya yi alfahari da ita, kullum yana riritata kamar ƙwai? Ina macen da ta samu matsalar ƙaruwa a wurin haihuwa? Ina wadda sanyi ya yi mata yawa ta buɗe? Ina macen da take da ƙarancin ni'ima a jikinta? Ina wadda take jin zafi a wurin saduwa? Hajiya kin taɓa amfani da maganin da zai matse ki ya mayar dake tamkar buduwa? Ko har yanzu kina nan a buɗe kamar bakin gari? To muna masu farin cikin sanar daku mun zo muku da ingantattun magungunan gyaran jiki na mata masu kyau da inganci kamar su..
Gumbar madara
Gumbar mata
Gumbar aya
Gumbar chaku
Gumbar dake saukar da ni'ima
Gumabar taƙadari
Gumbar riɗi
Gumbar dabino
Gumbar uku alkhairi
Kazar amare
Jijjiɓen saniya
Tabaje
Tsimi
Rikita mai gida
Jigidar tada sha'awa
Ruwan boom ruwan daɗi kenan
Ɗan matse
Karya gado
Maganin sanyi
Zumar ƙarin ni'ima
Zumar rage ƙiba
Zumar ƙarin ƙiba
Zumar riɗi
Mai zamani
Emergency powder
Tarhama
Kafi budurwa
Sabon budurci
Alfijir
Gamzaki
Garin dahuwar nama
Sabaya
Miskin ɗahara
Da dai sauran su. Namu ba irin na su bane, bamu fito ba sai da muka shirya, muka tabbatar da kwaliti da inganci kayanmu. Ƴar uwa gyara shi ne mace, aka ce ko kina da kyau ki ƙara da wanka, ina matan dake cewa ba sa shan kayan mata iya fruit kawai suke sha? To ku sani ko wane allazi da amanun sa, aikin fruit daban, aikin waƴan nan daban. Hajiyata ki saki jiki kawai ki zo musa labule, a gwangwaje ki da kayan da zaki rikita my house da su. Ki susuta shi, ya zamana duk inda yake kina maƙale a cikin ƙalbinsa. Matuƙar kika yi amfani da kayanmu, ina mai tabbatar miki da ba boka, ba malam za ki mallaki mijinki ciki ruwan sanyi, sai yadda kika yi da shi. Ga mai buƙatar kayanmu zai iya tuntuɓar waƴan nan lambobin 08163516796 ko 08081012143 muna aika saƙon mu a ko'ina.
Ayshercool
08081012143
