RAGAYAR DUTSE.
©️ Nana Haleema.
Book 1
Page 011.
A Abuja suka sauka, daga nan suka hau jirgi zuwa Yola. Tunda suka sauka a airport yake jin duniyar kamar tana juya masa, yana zaune ana duba passport ɗinsa, ya saka nosemask da baƙin glasess, ya kawo Face cap ya saka dan baya so a gane sa.
Motocici ne guda biyu a ajjiye suna jiran fitowarsa. Bilal da driver da Mansur, sai mai kula dashi Shams suka ƙaraso wajan, duk da ba dan sun ga Jazy ba bazai gane sa ba, ya kulle fuska gabaɗaya ba a gane shi.
Cikin girmamawa suka ce, "welcome Sir."
Maimakon ya amsa sai ya kalli Jazy, ya ya kalli Bilal, da yaren fulani ya ce, "ina fatan baka faɗa
ba?."
Cikin girmamawa ya ce, "yes Sir, ban faɗawa kowa ba."
Ya gyaɗa kai ya kalli Jazy har zai yi magana sai ya fasa ya yi musu alama da su tafi.
Ya kalli Jazy ya ce, "ni fa bana son zuwa gida, mu je hotel mu zauna, zuwa da safe sai mu koma."
Jafar ya ce, "kana da matsala wallahi, yau muka saba shiga gida yanzu? Wai me yake damunka ne?."
"Nima ban sani ba Jazy, kawai bana so in je yanzu. Hotel zan je in kwana ,gobe ko jibi sai in je gida."
Ya harare sa ya ce, "baka da hankali, har sai jibi ma?." Ya yi shiru bai ce komai ba.
Jazy ya ce, "Rehaan ka zo mu je ka shiga mota mu tafi, bana son wannan abinda ka ke yi."
"Wallahi baza ni gida yanzu ba, ku je kawai, ni hotel za a kai ni."
Jin ya ce wallahi sai Jazy ya ce, "Tunda na karɓi amanarka daga wajen Mamy dole na yarda, amma da baka isa ka saka ni ba wallahi. Fine, mu je gabaɗaya, amma da safe zamu je gidan."
A hankali yake takawa zuwa wajan motar, suna zuwa Mansur ya buɗe musu ƙofa suka shiga, Shams ya shiga gaban motar aka ja motar.
Sai bayan sun fita sannan Jazy ya faɗa musu hotel ɗin da zasu kai su.
Rehaaan ya ce, "bana so kowa ya san na dawo, har Mamy." Suka amsa cikim girmamawa.
Ya yi shiru yana kallon titi, jinsa yake yi uncomfortable, sam baya ƙaunar zuwa Nigeria bai san meyasa ba, gashi dai a Nigeria danginsa suke, uwa da uba da ƴan uwa duk suna Nigeria, amma ya fi son rayuwarsa a turai ya fi masa komai daɗi.
Baya son dawowa gida ko kaɗan, saboda ba yi jin daɗin zaman gidan, tunda kusan kowa na gidan ba ƙaunar zamansa yake yi a ciki.
Shi mutum ne mai son sakewa da ƴan uwansa, yana so ya ja ƴan uwansa a jiki sosai, ya nuna musu ƙauna, ya kashe musu abinda yake dashi. Babu inda yake yi masa daɗin zama kamar cikin family, a nan kaɗai yake sakewa ya yi hira kamar ba shi ba. Amma su ba haka ne a ɓangarensu ba.
Ajiyar zuciya ya yi a lokacin suka tsaya a hotel ɗin. Jafar ya rufe ta sa fuskar, dan in dai aka gansa an ga Rehaan, tun suna yara a haka suke har kawo gobe. Sai da ya gama reserving rooms sannan ya dawo suka shiga tare.
Yana shiga ya cire facemask da glasses ɗin, ya kalli agogo a lokacin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, ya ɗan yi shiru yana kallon waje ɗaya. Jazy ya taɓe baki ya fita daga ɗakin zuwa na sa.
Daƙyar ya samu ya miƙe tsaye ya yi wanka ya canja kaya ya kwanta, yana tunanin abinda shi kansa bai dai meye ba.
Ya rasa wanne irin tunani ma ya kamata ace ya yi, yana son ganin Mamynsa amma baya son zuwa gidan, yana son ganin Abba da Riyya da Banisha amma ba ya son zuwa gidan ko kaɗan.
Ya miƙe zaune ya kunna bedside lamp ya harɗe hannu a ƙirji ya yi shiru. Whatsapp call ne ya shigo wayarsa da number nigeria, ya duba ya ga Alma ce, ya ɗan yi tsaki ya kashe power wayar ya yi shiru.
Buɗe kofar aka yi ya ɗaga kai suka haɗa ido da Jazy ya shirya cikin night wear shima, ya ƙaraso ya ce, "baka kwanta ba?."
Ya girgiza kai ya ce, "ban sani ba Jazy, bana jin daɗi gabaaɗaya. Ina so in ga Mamy, amma bana son zuwa gidan kwata-kwata."
Jazy ya ce, "ka dinga addu'a Ray."
"Ina yi Jazy."
"To ka kwanta."
Ya ɗan dafe kai ya ce, "kaina yana ciwo, ina son shan tea Jazy."
Jazy ya gyaɗa kai yana harararsa ya ce, "sai ka sha ai, malam ni ba yaron ka bane, ka yi abinda ka ke so da kanka."
Ray bai ce komai ba, ya ɗauke kai bai sake kallonsa ba.
Har Jazy sai fita sai kuma ya kasa, jin ya ce kansa yana ciwo sai ya waiwayo ya ce, "in kawo maka tea ɗin?."
Ya ɗan murmusa ya ce, "Ka gaji kaima, ka dawo nan mu kwanta, ina jin kamar ana ganina."
Ya zauna a kusa dashi ya ce, "Don Allah ka nutsu, ko yaushe in ka zo ƙasar nan halin da ka ke shiga kenan."
Shiru ya yi baice komai ba yana sauke numfashi, Jay ya ce, "ka nutsu ka dinga addu'a, komai zai zo ya wuce ya zama labari, kamar bai faru ba."
Ya gyaɗa kai bai ce komai ba. Ya ce, "zan je entry na samo maka tea ɗin."
"Ka bar sa kawai, zan kwanta" ya faɗa yana kwanciya tare da rufe ido.
Jazy ya miƙe ya kashe masa hasken ɗakin ya fita cike da tausayinsa a wannan yanayin. Indai zai zo gida haka ake fama, ya dinga ɗarare jikinsa kenan, yana jinsa kamar baƙo, yana ji kamar akwai abinda zai same shi.
Wani lokacin ya dinga mafarkai marasa daɗi, ko ya ce yana ji kamar ana bin bayansa. Ko da ya zo ƙasar kasuwancinsa ya tsaya cak, sai dai Jazy ya cigaba da kula masa. Ga yawan ciwon cikin da aka kasa maganinsa, ga ciwon kai da yawan zazzaɓi.
Rehaan yana bashi tausayi sosai, dan ya san duk ɗaukaka ce take jawo masa haka, duk da wani lokacin yana sane yake wani abun, shiyasa yake share shi.
******
Ƙarfe biyu na dare wayar Islaha ta yi ƙara, ta buɗe ido cike da bacci ta kalli wayar ta ga number Chairman.
Ta goge idonta ta miƙe zaune sosai, a bayyane ta ce, "Chairman kuma! Anya lafiya?." Ta furta kafin ta ɗauka wayar ta yanke.
Aka sake kira ta tsaya tana kallo cike da mamaki, kafin ta ɗauka ta saka a kunne.
Daga can ɓangaren ya ce, "Sorry Islaha, na tashe ki daga bacci ko?."
Mamaki ya hanata magana, dan ta yi tunanin mistake ya yi. Ta ce, "Chairman lafiya?."
"Lafiya. Na samu labarin Rehaan ya shigo garin nan yau ɗin nan, kuma ya sauka a diamond hotel. Babu ɓata lokaci Islaha, zan turo Saleem da Muslim ƙarfe huɗu da rabi na dare, zaku tafi hotel ɗin, sai ki yi magana dashi koda bayan sallar aduba ne."
Islaha ta ƙwalalo ido waje cikin mamaki ta ce, "Ƙarfe huɗu fa Chairman! Kana nufin kafin ayi sallah kenan?."
"Eh Islaha, hakan za a yi, sai ku tattauna dashi in ya fito sallah. Yawanci suna fitowa shiga masallaci, kin ga sai ku haɗu a wajen."
"Amma Chairam cewa ka yi yau ya shigo garin nan, kana ganin ya dace mu je a yanzu? Ni sai nake ganin zai fi a basa lokaci, kar mu je ya ga haukan mu akan hakan."
"Ko ya ga haukanmu ɗin babu komai, mu ne muke nema Islaha, wannan dama ce mai kyau mu ka samu, dan haka bazan yi wasa da ita ba. Ki ɗauki iv nan da na ba ki, sannan ki shirya, ki saka id card ɗinki ku tafi. Saleem da Muslim zasu zo ku tafi. Bana so a samu matsala Islaha, i trust you, shiyasa na zaɓe ki. Don Allah kar ki bani kunya."
Islaha ta ce, "Amma Chairman abin ya yi wuri, a ganina a bashi lokaci ya huta sai mu je a same shi. Ka ce yau ya dawo, kuma mu je yau?."
"Gobe zaku je ba yau ba, tunda na tabbatar baza ku samu ganinsa ba sai zuwa safiya."
"Meyasa baza a bari sai bayan sallar asuba mu tafi ba?."
"Islaha in baza ki iya aikin nan ba na bawa wani, ya ina yi magana kina katse ni kamar wani yaron ki?."
"Sorry Chairman, ba haka nake nufi ba. Allah ya kaimu lafiya."
"Ki shirya da wuri, zasu zo ku tafi. Kar a samu matsala Islaha" yana faɗa ya yanke wayar ta bi wayar da kallo.
Islaha ta ajjiye wayar a gefe ta ce, "Ikon Allah, ko meyasa Chairman ya dage akan interview da mutumin nan oho. A kansa zan fita kafin sallar asuba, kuma in na je babu tabbacin zan gansa. Kuma ai sai ya ga shirmen mu, a ce mutum ya dawo yau kuma mu je masa ko hutawa bai yi?. Mtsw! Chairman yana da matsala wallahi" ta faɗa tana sauka daga kan katifar.
Ta miƙe tsaye ta riƙe ƙugu ta ce, "wai ƙarfe huɗu, ai gwara kar na koma in yi alwala na yi sallah. In lokacin ya kusa na yi wanka. Amma bara na faɗawa Hamma" ta faɗa tana ɗaukar waya ta kirasa.
Abin mamaki call waiting alamun waya yake yi, ta cire wayar daga kunnenta, ta duba ta ga dai da gaske shi ta kira, kuma waya yake yi.
Mamaki ya cika mata zuciya, ta tafi tunanin da wa yake waya a tsakiyar daren nan? Ta san shi ba ma'abocin waya bane, ya fi son chat akan waya amsa waya, dan ko ita sai su kwashe awa biyu suna chatting amma wayar minti talatin ta gagare sa.
Shiru ta yi alamun tunani, ta zubawa wayar ido tana jira ya kira ta shiru bai kira ta ba, dan ta sna ya ga shigowar kiran ta.
Sai can kusan minitina goma sannan kiransa ya shigo, ta ɗauka ta saka a kunne.
Kafin ta yi maganaya ce, "Matar Hamma lafiya? Wani abun ne ya same ki?" Ya tambaya a ruɗe yana jiran amsa.
Maimakon ta amsa sai ta ce, "da wa ka ke yin waya a tsakiyar daren nan?."
"Boss ne fa, kin san yana china, shi a can ba dare bane."
Ta yi shiru bata amsa ba alamun bata yarda ba. Saheer ya ce, "ba ki yarda ba?." Nan ma bata amsa ba ta yi masa shiru.
"Zan yi screenshot na tura miki ki gani, kar ki yi zargin da wata nake waya" ya faɗa yana ƴar dariya dan ya san Islaha akwai kishi mai yawa.
Saheer ya kuma cewa, "Islaha ki amsa min, lafiya kuwa?."
Daƙyar ta ce, "Lafiya lau. Dama Chairman ne ya kira ni yana faɗa min Mr Ray ya shigo gari."
"Shine me? A daren nan zai katse miki bacci ya ce miki Rehaan ya shigo ƙasar nan?."
"Yana so mu je diamond hotel mu same shi, zai turo da mota ƙarfe huɗu da rabi za mu tafi. In an yi sallar asuba sai mu samu ganinsa."
"What! Ƙarfe huɗu da rabi fa ki ka ce? Wacece zata fita a wannan lokacin?."
Ta ɗan sauke numfashi ta ce, "ni mana."
"Ke da wa?."
"Ni da Salim da Muslim."
"Wannan shegen Muslim ɗin mai kallonki ɗin nan ko?."
Ba ta amsa ba, ya ce, "Baza ki je ba Islaha, babu inda zan bari ki fita a wannan lokacin."
Ta ɗan rufe ido ta buɗe ta ce, "Hamma ya zama dole in je, tafiyar aiki ce."
A fusace ya ce, "Tafiyar aikin tafiya neman rahama ce? Dan shi Chairman ɗin bashi da hankali, ƙarfe huɗu na dare zan sallama ki ki fita keda wasu mazan da ba ƴan uwanki ba?."
Jin ya fusata sai ta sassauta murya ta ce, "ba wannan tunanin zaka yi ba Hamma, kai ka faɗa min in na samu damar ganin Mr Ray har na yi interview dashi nasara ce a gare ni, kuma ga lokacin ya zo na ji ka fusata kana ta faɗa."
Saheer ya ce, "rainin hankali ne bana so, dan hauka irin na Chairman ɗin kawai sai in barki ki fita da daddare?."
Ta ce, "babu abinda zai same ni, daman na kira na faɗa maka ne."
"Mtsw! Allah ya kaimu, in lokacin ya yi ki kirani, zan faɗawa Baffa sannan zan fito." Ta ɗaga kai ta kashe wayar tana sauke ajiyar zuciya.
Alwala ta yi ta shinfiɗa sallaya ta tayar da sallah, bayan ta idar da adadin yadda take so ta yi karatun alkur'ani ta cigaba da lazumi har ƙarfe uku da rabi ta yi.
A lokacin ta tashi ta fita zuwa kitchen ta ɗan dafa ruwa ta zo ta yi wanka, ta shirya cikin abayar da Hamma ya siya mata a sallar da ta wuce.
Ta ɗauki facemask ta saka saboda sanyi da ƙura, saka facemask har ya zamar mata jiki, in ta fita babu shi tana samun matsala. Ta ɗauki wayarta da handbag ta saka iv a ciki, ta zauna tana jiransu kira ta a waya.
Ƙarfe huɗu da rabi daidai Saleem ya kira ta, ta ɗauka ya shaida mata suna ƙofar gidansu.
Ta yi ajiyar zuciya ta kira Hamma, bugu ɗaya ya ɗauka alamun jiran kiran yake yi, ta ce, "sun zo." Ya amsa ta kashe wayar ta fito falo.
Gab da zata fita daga falon ta ji muryar Mama tana cewa, "aje a dawo, a taho da kuɗi masu yawa, dan wannan fitar da alama ta musamman ce, tunda bata tashi yi ba sai tsakiyar dare. Maza aje a dawo, ina nan ina jira, saura a dawo ace min babu kuɗi, a kyauta aka bayar."
Islaha ta ɗan runtse ido ta buɗe, ta kalli Mama ta ce, "Kirana aka yi daga wajan aiki, na ɗauka kina bacci ne shiyasa ban faɗa miki ba."
Ta zabga mata harara ta ce, "ko ba wajan aiki ba? Ko da yake wajan sana'a ai wajan aiki ne. Sai kin dawo." Islaha bata ce komai ba ta fita daga falon.
Tana fitowa ta ga Hamma a tsaye yana jiranta, ta ƙaraso tana kallonsa kamar yadda yake kallon ta.
Kafin ta yi magana ya ce, "sai wani ƙhamshi ki ke yi, bayan da wasu mazan za ki fita bani ba" ya faɗa fuska a ɗaure.
Ta yi murmushi tana sunkuyar da kanta ƙasa, ita bata ji ƙhamshin ba amma shi ya ji. Bata saka turare mai ƙarfi, saboda yanayin da take fama dashi.
Ya ɗan yi tsaki ya ce, "ki jira ni na je na shirya na zo na bi ki, bazan iya barin ki tafiya ke kaɗai ba."
Zai wuce da niyar zuwa ya shirya ɗin, ta yi sauri cewa, "Hamma baka yarda dani bane?."
Ya juyo ya ce, "ba rashin yarda bane ba Islaha, bazan iya haɗa ki da mazan da ba ƴan uwanki ba, ku yi tafiya a cikin wannan daren. Gashi ke kuma kin je kin yi kwalliya, sai ƙhamshi ki ke yi kamar zaki je biki. Bazan iya ba, kafin ki dawo zuciyata zata iya bindiga, gwara mu je a yi komai a kan idona."
"In kana cewa haka sai naga kamar akwai rashin yarda a tsakanina da kai. Me zai same ni har da zaka so ayi komai a kan idonka Hamma? Me zan ka ke tunanin zan aikata wanda bazan iya yinsa a gabana idonka ba?."
Ya ɗan sauke numfashi ya ce , "kishi nake da hakan, musamman da ki ka ce min da wannan Muslim ɗin, in iya Saleem ne da sauƙi, amma Muslim ɗin nan ba ƙaunarsa nake yi ba."
Ta ɗan yi murmushi ta ce, "ka yi haƙuri, zuwa nan da anjima zan dawo. Ka ga suna yi min waya" ta faɗa jin wayarta tana ƙara.
Ya ɗan sauke numfashi ya ce, "zan yi magana da Chairman ɗin, wallahi in muka yi aure bazan lamunci wannan shirmen ba."
"An gama ranka ya ɗaɗe."
"Kuma hotel ɗin za ku je?."
"Eh."
"Bana so wallahi."
Ta kalle sa ta ce, "kar dai kaima kana cikin masu cewa in aka ga mace a hotel abu ɗaya ne ya kai ta? Kar ka zama ɗaya daga cikin masu ɗabi'ar ƴan arewa, musamman hausawa da fulani. Mace aiki baya kaita hotel, sai abu ɗaya."
"Ba haka bane, ni fitar ce bana so." Bata ce komai ba ta yi shiru. Ya bita da kallo sannan ya ce,
"Ban da rashin kunya, don Allah ki yi haƙuri. Kar ki je a ɓata miki rai ki ta faɗa ana kallon ki. Na san halinki, koda an yi miki ba daidai ba ki daure."
"in sha Allah, bazan yi ba."
"Mu je in raka ki."
Ta yi dariya suka jero shida ita har ƙofar gidan.
A nan ya ga mota ajjiye tana jiranta, ya ƙarasa har bakin motar. Saleem da yake ciki ya ce, "ni na san Hamma bazai bar Islaha ta fito ita kaɗai ba, dole ne ya zamar mata escort."
Saheer ya murmusa ya basa hannu suka gaisa, suka gaisa da Muslim da yake zaune a gaba sannan ya ce, "kawai dan babu yadda zan ne, shiyasa har na barta ta fito yanzu. Kuma zan samu Chairman ɗin na ku, haka kawai tsakiyar dare a ce fito aiki, kawai saboda gayyatar wani interview?. Yanzu in interview ɗin ce ina jin kwana zata yi kenan ko?."
Saleem ya ce, "to ya za a yi? Abinda aka jima ana nema ne bai samu ba sai yanzu. In Chairman ya rasa damar hira da wannan bawan Allah ai zai iya yin zazzaɓi. Ga shi Islaha tana da sa a sosai, in dai ta yi invinting sai an yi accepting."
"Bazai dinga takura min mata ba wallahi, sai a canja mata waje ta koma bayan camera."
"Haƙuri za a yi Hamma" ya faɗa yana dariya ya kalli islaha ya ce, "Islaha shiga mu tafi."
Islaha ta shiga baya, Saheer ya kalle ta ya ce, "ki kula da kanki, kin ji?." Ta ɗaga kai tana murmushi.
Saheer ya ce, "Safeera fa? Ba tare za ku je ba?."
Saleem ya ce, "ka san ita a ɓangaren record ta ke, irin wannan tafiyar ba a cika yi da ita ba."
Saheet ya ce, "nima ɓangaren zan saka ta koma, bazai yu ta dinga fita ko ina ba." Saleem ya yi murmushi ya ja motar suka tafi.
Sai bayan motar ta tafi sannan ta gaisa dasu, Saleem ya ce, "an taso ki babu shiri ko?." Ta
ɗan yi murmushi ta ce, "ni da na ji kiransa wallahi tsoro ne ya kamani. Gaskiya Chairman yana son gayyato mutumin nan, ban taɓa ganin guest ɗin da ya mayar da hankali akan nemansa kamar wannan ba."
Saleem ya ce, "To ba gama garin baƙo bane, kowa zai zo ace shine na farko da ya fara hira dashi a channel ɗinsu da yaren hausa."
"Allah ya bamu sa a a kansa."
Ya amsa da amin suna cigaba da tafiya. Ba jimawa suka ƙaraso bakin hotel ɗin, aka buɗe musu gate suka shiga suka yi parking.
Sai a sannan Muslim ya ce, "To a nan zamu tsaya ko zamu shiga ciki?."
"Zamu shiga mu yi reserving room Islaha ta zauna, babu daɗi a barta a reception a zaune kowa yana ganinta. Daman ya ce a kama ɗaki ɗaya a zauna saboda bamu san lokacin barin mu nan ba, tunda lokacin sallah ya kusa sai mu shiga masallaci, ita sai ta shiga ciki ta zauna."
Islaha da mamaki ta ce, "wai a taƙaice a ina Mr Ray ɗin yake? A ina zamu gansa?."
"Waye ya sani Isalaha? Abinda na sani kawai tabbas yana cikin hotel ɗin nan. Amma floor ɗin da yake da room number ba mu sani ba. Amma Chairman ya ce zai turo mana."
"Ikon Allah, wannan shine zuwa gona babu fatanya" Muslim ya faɗa yana kallon Saleem.
Saleem ya ce, "mu je mu kama ɗakin, in mun kama sai ta je ta zauna, in fito daga sallah sai mu je mu same ta."
Muslim ya ce, "ɗaki a nan fa yana da tsada, haka ya bada kuɗi a kama?."
"To ba so yake yi ba? Mu je" ya basa amsa yana fita itama ta fito tana gyara zaman id card ɗinta a wuyanta.
A hankali suke takawa zuwa ciki, Saleem ya ƙarasa ya karɓi ɗaki ya dawo wajan ya bata card key ɗin ya ce, "key ɗin ƴan gayu ne, ba a haɗa sa da waya, in ba haka ba bazai buɗe ba sai kin dawo."
Ta yi dariya ta karɓa ta ce, "tare zamu je?."
"A'a ki je kawai, in an idar da sallah sai mu zo mu san abinda za a yi."
Ta girgiza kai ta nufi elevetor ta shiga zuwa floor ɗin da room ɗin yake.
A lokacin Rehaan ya fito daga ɗakin yana tsaye a ƙofar room ɗin sanye cikin kayan bacci ya ɗora rigar sanyi mai hula a kai, ya saka hular ya rufe kansa har kusan rabin fuskarsa ya rufe.
Neman ɗakin da Jazy yake yi, dan shi bai san a wanne ɗaki yake ba ga shi ya kira sa yana bacci.
Ɗakinsa yana kallon elevetor, tana buɗewa ya kalli wajan a tunaninsa Jazy ne. Suka haɗa ido da Islaha da ta fito daga elevetor tana kalle kalle, tana so ta ga room ɗin da zata shiga.
Islaha ta ɗauke idonta daga kansa tana kalle-kalle har ta gano ɗakin.
Ta gabansa ta wuce ta buɗe ɗakin ta shiga ba tare da ta sake kallon sa ba. Shima tunda ya kalle ta sau ɗaya bai kuma kallo ba, daman ya yi tunanin Jazy ne shiyasa ya kalle ta. Bai jima a tsaye ba ya koma ɗaki.
Islaha tana shiga ta ƙarewa ɗakin kallo, ta yi ajiyar zuciya ta cire facemask ɗin ta zauna tana kallon ɗakin. Kiran sallah ta ji ana yi, ta shiga banɗaki ta yi alawala ta fito ta tayar da sallah har aka yi asuba.
Tunawa ta yi ta bar handbag ɗin a mota, kuma a ciki iv card ɗin yake, ko yaushe zasu iya ganin Ray, da buƙatar riƙe iv card ɗin a kusa, yadda da an haɗu a miƙa. Ta ɗan yi tsaki ta miƙe ta fito daga ɗakin da hanzari.
Tana kulle ƙofar ta juyo ta ji ta yi karo da abu, ta ji saukar abu kamar ruwa a jikinta, ta kalli jikinta ta ga black tea ne ya zube mata a jikinta. Ga paper cup ɗin da tea ɗin yake ciki a ƙasa yana gangawara a ƙasa. Allah ya taimaka babu zafi, amma ya ɓata mata jiki.
Ta ɗago ta kalle kalli abinda ta buge dashi har ya zuba mata tea ɗin hannunsa, ta ga ba ita yake kallo ba wani wajan daban yake kallo kamar ba da ita ya yi karo ba. Ya zagaye ta zai wuce, har yana tsallake cup ɗin bai ce komai ba.
Islaha ta kallesa, ta kalli cup ɗin da jikinta, ta ga in ta yi shiru fa ya raina mata hankali, gwara ta magantu. A nutse ta ce, "excuse me, Didn't you realize you bumped into me?!" ta faɗa tana kallonsa
Rehaan kamar bai ji ba, ya ɗauko waya yana kiran number Jazy.
Islaha ta zuba masa ido cike da takaici da baƙin ciki, ta kalli kanta ta ga yadda ta ɓaci da tea ɗinsa, ta sake kallonsa cikin ɓacin rai da hasala. Duk da bata ganin fuskarsa dan ya ɓoye rabin fuskarsa da hular sanyi, amma zata iya gane kammaninsa, dan ɗazu ta gan shi a tsaye har haɗa idanu sun yi.
Ta zagaya ta tsaya a gabansa, ta yi snapping fingers ɗinsa suka ba da sound, dan ya bata attention ɗinsa sosai. Islaha ta ce, "kurma ne kai? Baka ji ka buge ni bane, ko baka ga ka zuba min da tea ba?."
Ta ƙasan ido Rehaan ya kalle ta, ya sake ɗauke kansa kamar ba ya jin yaren da take magana dashi, kuma yana tsaye bai bar wajan ba, kuma bai kalle ta ba.
Islaha ta ji takaici ya mamaye mata zuciya, ta ji kamar ta yi tsalle ta dinga dukansa har sai ta wuce takaicinta.
A fusace ta ce, "wallahi ba dan sauri nake yi ba, sai na koma na je na siyo tea, na zo na watsa maka a jikinka dan ka ji abinda na ji. Dan wualaƙanci, ka zuba min abu a jikina kuma ka ƙi kallona balle ka bani haƙuri? Waye kai?."
A duk duniya kalmar da take tsayawa Rehaan a rai bata wuce kalmar waye kai ba, yana ganin kamar raini ne a kalle sa a ce waye shi. Yana daga cikin the most popular people a arewa, amma a kalle a ce waye shi, duk sai ya ji kamar an raina masa wayo.
Hakan ya saka ya ɗago fararen idanunsa ya kalle ta. Ita kuma ta nunasa da yatsa ta ce, "Kar ka yi fatan mu sake haɗuwa, in mu ka haɗu abin bazai yi maka kyau ba, dan wallahi ko a ina na ganka sai na ɓata maka rai da lokaci, kamar yadda ka ɓata min yanzu. Bana ɗaukar raini da wulaƙanci, ko waye kai daidai nake da kai. Na ƙyale ka yanzu dan ina sauri, kuma na yiwa Hamma alƙawarin bazan yi faɗa ba, da sai na tara maka jama'a wallahi, sai ka ji ina ma baka zo hotel ɗin nan ba!."
Rehaan kamar ba jinta yake yi ba, hankalinsa yana kan waya ya mayar da ita ƙaramar mahaukaciya. Duk da kalmanata suna shigarsa, amma ba shi da lokacin da zai ɗaga ido ya kalle ta.
Takaici ya sake kamata, ta yi ƙwafa ta bar wajan tana mita.
"Haka kawai an taso ni tun asuba akan inviting wani banza Rehaan Yola, ni ban ga Rehaan ba, a banza da wofi wancan ƙaton banzan ya ɓata min rai. Ko ina Mr Rehaan yolan oho. Mtsww! Shirme!."
Elevetor yana buɗewa Jazy ya fito, ta ɗan kalle sa suka haɗa ido, ta ɗauke kai ta basa hanya ya wuce ita kuma ta shiga.
Tana shiga elevertor aka buɗe wani ɗakin, wani namiji ya leƙo yana dariya ya ce, "Beb you forgot your facemask, me yasa ki ke gudu?. I love you." A tare Jazy da Ray suka kalli wajan, sai aka kulle ƙofar aka koma ciki..
Nana Haleema✍🏻
09030398006
