Ramin Kura Page 3&4 Complete

 

Shafin Abokiyar Hira

*༺❥𝙍𝘼𝙈𝙄𝙉 𝙆𝙐𝙍𝘼༻*

  # 𖢧ᑋᕪ ᵗᕪᐢˢᑊᐤᐢ ꕯᐢ 𖢧ᑋᑊˢ Sᑦᕪᐢᕪ

https://whatsapp.com/channel/0029Vb4EHwq6LwHgpTokZA3D

Na Maryam Naseer Mirrah

𝘼𝙈𝙈𝙀𝙔 𝙇𝘼𝙔𝙇𝙀𝙍𝙃 ✍️

Book One paid 

       ♡

Page 3&4

𝙔𝙊𝙐𝙉𝙂 𝙏𝘼𝙇𝙀𝙉𝙏𝙀𝘿 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍'𝙎 𝘼𝙎𝙎. 

_NA'EEMA SULAIMAN SARAUTA *NIMCY LUV* har abada ƙaunarki ɗaya ce a gareni my Role model,  me zuciyar lu'ulu'u da Zinare domin duk inda akaje aka zo ke ce AMMEY LAYLERH 💐. Na sadaukar miki da wanan littafin, this novel is for you my humy darling princess tawa, my support system, my Role Model I love you_


*Zuciyarki fara Aniyarki fara, kyautatawa Halinkine, Mutunci da karamci duk a tare suke dake,MAMAN IHSAN  tawa har gaban abada ke kaunar AMMEY LAYLERH ce, Ina Sonki da yawa da yawa ina matuƙar godiya gareki tare da sake jaddada ƙaunarki gareni*



 _Special Thanks to Masoya masu bibiyana, ina alfahari daku a ko ina a kowacce duniya kuke Love you all 💞💖💘💗_


     ♡_Capricorn season_


# THE POWER IN ROCKET 💪~

    

# DEEP ASSUMING FOV

# Boms squad

# A TAITOR's

#  ROMANCE

#  BLOCKBUSTER

#  A SOLDIER's 

# Courage

# Hop0

# Is Crime 

# Destiny

# Betray

# HotLove

# His love towards


    ♡♡♡♡♡♡♡♡

Mai martaba Sarki *ASHFUD KAMAALA RAHEEM DAWOOD* shi ne sarki na goma sha biyar a masarautar *UMMUL YOODA* dake cikin garin _Adafan ta tsakiya dake  Nahiyar Chadi da Sudan maso  Arewa cin Sudan ɗin_  jika ne wajan Mai martaba sarkin Ummulyooda  RAMEEM DAWOOD. Sarki na goma sha huɗu a wancan zamanin, wan Mahaifin sa Sarki Ashud wanda mahaifinsa ya masa takwara dashi a yankin Chadi ta tsakiya. shi ne sarki na goma sha uku, Mahaifinsa KAMAALA RAHEEM DAWOOD Yana da tarin ƴan uwa da dama wanda suka haɗa da uwa ɗaya uba da ɗaya, da kuma wanda suke  uba ɗaya, shi kaɗai ALLAH ya zaɓa a cikin su ya baima sarautar Ummulyooda duk da tarin ƴan uwa manya da yake da. Duk kuwa da kasancewar masarautar, Babbar Masarauta ce ta asalin larabawa, Masarautar ta samu asali ne  tun iyaye da kuma kakan ni, Wanda a kowanne ƙarni ake sake gyareta haɗi da sanja wasu tsarin abubuwan ma na daga gine ginen ta.... Tamkar a yanzu da take hannun margayi ASHFUD KAMAALA RAHEEM DAWOOD. Wanda masarautar ta samu haɗaɗɗen  gini  irin na masarautun nan da sukayi zarra sukayi fice a cikin manyan masarautu. Yana yin tsarin ginin kawai  abin a tsaya a kalla ne, domin kuwa tsaf zaka ɗauka hotel ne ma saboda tsananin yadda yake da kyawu, da kuma passes daban daban dake cikin emirated ɗin, banda wasu shegun benaye iyaka ganinka wanda aka tsarasu da iyaka zallar gilashi. 

    Masarautar Ummulyooda kenan! Masarautace me cikakken iko wacce take taƙama da Al'adarta da kuma Addininta. Masarautar  _UMMULYOODA_  ginanniyar masarautace wacce take tsaye da ƙafafunta tun iyaye da kakanni, tun a wajen masarautar zaka fahimci ba ƙaramin Mutum ne ke mulkar Masarautar ta UMMULYOODA ba cikin cikakken iko da kuma ginshira haɗi da wani  irin kwarjinin daya ma duk wani family daya dangaci duk wani family dake cikin masarautar Ummulyooda. Bare kuma azo kan uwa uba me mulkartar baki ɗaya kaima me karatu ai kasan babu ƙarin bayani domin ɓatama kai loƙacine domin magana ake ta sarkin sarakan masarautun duniya. Sarki ASHFUD KAMAALA sarki ne mai cikakke ilimi da kuma wayewa, Inda a matakin boko yana da matakin PHD. A ɓangaren ilimin addini kuwa ba'a cewa komai domin yafi zurfi a wannan ɓangaren ma fiye da komai, shugaba ne shi me tarin ilimi da kuma adalci da sanin ya kamata da tausayin talakawan sa ta ko wacce fuska, baya lamuntar zalunci ta ko wanne ɓangaren ko waye kai ko kuma ɗan waye yayi ba dai-dai ba masarauta zata hukunta. 

  Yana da yawan taimako da sadaka musmaman ga wanda basu dashi, baya jurar ganin talaka wan ƙasar sa cikin ƙunci da ƙasƙanci, don haka ya tamkar waliyyi a gare su. Wannan tarin alkhairan nashi ya sanya kowa dake cikin fada ya tsane shi, ciki kuwa harda iyaye da kakanni, domin anyi yaƙinin cewa tinda ake sarakuna a masarautar ba'a taɓa adalin shugaba irin sa ba, duk da kasancewar mahaifinsa ba haka ya taka irin wannan muhimmi yar rawar a nasa lokacin. Sedai daya tashi nashi mulkin seya zarce na mahaifin nashi, sunan shi kuwa ya jima da cika da timbatsa ta kowacce kusurwa da kewayen duniyar ma. 

 Sarki ASHFUD yana Matan sa uku. Yayin da da babbar cikin su itace Fulani RUMAANA, itace uwar gidan sa auren saurayi da BUDURWA suna da yara biyar duk mata ne. Mace ce makira a ɓoye, a bayyane kuwa  zata nuna maka duk duniya babu wanda take so sama dakai amma a ɓoye tafi kowa cin dunduniyar ka. haka zata yi ruwa ruwa mayi mayi gabanka ita nan game ƙaunar ka,  Se Matar sa ta biyu itace Fulani Mardiyya itama ƴar sarkin Junayna ce wacce ta gaji duk wani irin makirci da kulla kulla irin na mahaifiyarta, bayan nan ita Mace ce mai izza da ƙasaita da nuna zallar iko a kan komai, itama tana da yara shida domin haihuwar kwanika take yi, shekarar data haife ka shekarar zata dire maka ƙanwa ko ƙani. Maza huɗu ne yaran nata babban shi ne Zayed su kuma sauran duka ƙananune, inda daga nan tasa aka cire mata mahaifarta gaba ɗaya domin a ganin ta da tunanin ta haihuwar ƴaƴa  maza a gidan sarauta shi ne riba. Kuma ta haifa don haka ta cire duka mahaifar nata. Tin da yaran nata sune dai mazan, kuma  sune manyan maza a kaf gidan sarautar kasancewar  sune kan gaba a komai za'a yi na sarauta tabbas dasu ake damawa. Babban burin Fulani Mardiyya a duniya shi ne yaranta su gaji sarautar UMMUL YOODA, data kasance tsarkakkiyar masarauta.  Se matarsa ta uku wato ADEENEERH EL_ HASSAN KUWAIT. Ita ɗin cikakkiyar Ƴar sarki al_hassan ce Babbar yaya ga AK EAGLE, tana da wani irin kwarjinin data gata daga mahaifin nata, kai da ganin   yanayin maganar ta da yanayin takun ta kaɗai  kasan cewar yeah ita ɗin  jinin sarauta ce gaba da baya, domin kuwa shi ne  yake yawo a jikin ta gaba da baya. Fara ce tass kyakykyawa domin ta ɓangaren mahaifiyar kyawawa ne sosai. Ta jima bata Haihu ba ku san shekarar ta goma sha biyar da aure kenan tare da sarki ashfud, se  a wannan lokacin ALLAH ya bata cikin data kusan haife sa bata cikakken hayyacinta. Kusan lokaci ɗaya Fulani RUMAANA tare da QUEEN OUMMEY (ADEENEERH) Suka fara laulayin ciki. Inda ita ta haihu lafiya yaranta biyu mace da namiji, Sedai macen bata zo da rai ba, a yanzun haka tana nan tare da kyakkyawaan yaronta, wanda kowa yake mamakin kyawun nashi, domin kuwa kyan harya zarce misali da tunanin me karatu..... 


Duniyarta ta mata ƙunci a sanda ta buɗi ido ta ganta se ita kaɗai ɗinta, wani kalar nauyi da ƙunci ne suka haɗu suka daskarar mata da zuciyar ta nan take, Ta nemi adalin mijin ta ta rasa, ta nemi Abinda ta haifa shima ta rasa walau mace ce ko namiji ne, wanda hakan shi ne yay sanadiyyar bar bata wani ƙatoton tabon da take jin har ƙarshen numfashi da wahala ta manta da hakan,Lallai tabbas da ace ƙarfin iko a hanun kowanne ruhi yake a zahirin rayuwa, da ita ce zata zama mace ta farko a duniya mai ƙarfin ikon da zai girgiza zukatan kowaɗanne irin azzalumai. Kafin shuɗewar wannan al'amari ma su ɗauke da kundun baƙin ciki rayuwar rayuwar da aka jefa ta, ita da adalin mijin ta, jinsu suke tamkar dutsen lu'u-lu'u ne su a cikin tsakiyar zinarai. Domin magana ake ta laylerh da majnun.  Don  matuƙar ƙaunar juna zunzurutu mara algus ɗin da suke ma juna, mara gauraye da suke ma junansu. Masu kuka a yayin zubar hawayen ɗayansu, masu dariya a yayin farin cikin ɗayansu, masu jinya  a yayin da ɗayansu ya kwanta jinya. Masu shiga matuƙar damuwa a yayin da suka kalla wani nasu yana cikin damuwa, Sarki ashdud kenan me zuciyar lu'ulu'u da zinare. Wanda zuciyar sa take a wanke tsafff domin UBANGIJI madaukaki ya riga da ya gyare mishi ita tsafff, yana son ƙasar sa da mutanen dake cikin ta, yana son masarautarsa da mutanen dake kewaye da ita. Yana ƙaunar duk wani abu daze kawo ci gaba wa ƙasar sa, yana ɗauke damuwar wasu koda hakan yana nufin shi ze kwana cikin damuwar yana ɗaukar hakan ba a bakin komai ba, muddin mutum ze samu farin ciki a cikin tashi duniyar            

        ☆

Ɗagowa tayi ta kalli Afud Kamaal  da  idanuwanta da suka canza 

zuwa kalar ja sosai ta zuba masa jajayen idanunta. Kafin idnonta su zubo da wasu kwallar zafin da zuciyarta ke mata, na  tsananin tausayin  kanta da kanta, yau ina yaran ta biyu data haifa?, domin kuwa ta san yara biyu ta haifa duk da kasancewar bata wani cikakken hayyacinta. Amma tasan da cewar yara biyu ta haifa, tin da watan haihuwarta ya kama dama take a cikin zullumi, domin kuwa duk wata kulla kulla ta gidan sarauta babu wacce bata sani ba. Don haka kullum take cikin faɗuwar gaba, domin ita tata uwar tin ba tafi shekara 7 da haibarta ba aka kashe ta, aka kuma kashe musu kakan su ASHAAN   A MASARAUTAR SU TA EMAAR's. Babu kalan kulla kullar da bata kalla ba.  Maganar Afud ne ya dawo da ita daga duniyar data ɗan Lula. "Duba da idanuwanki ki kalla ADEENERH  yadda daraja da Martaba da kima yanda take ƙaruwa da kuma dukiya"  

  Kanta ta sake ɗagowa a karo na biyu  tana kallarshi da jajayen idanuwanta. Dakatar dashi tayi ta hanyar furta. 

  "Ai ita kwaryar kirki a ragaya take, darajar kanwa kuma se cikin miya.....

   Numfashinta ya tarya shima, wanda ya sanya oummey buga masa wata uwar tsawa, domin ita ɗin dakakkiyar mace ce da sam bata da tsoro ko shakkun wani abu. " Ka gimtse min bakin ka anan Afud!, idan ina yiwa mutum bayani baya gimtseni. Ko kana nufin harka manta da wannan ƙa'idar da nake da?, ka sani cewar tarin dukiya ba shi ne karfin ikon mutum ko kuma kima da darajarsa ba, ka gina zuciyar ka akan gaskiya tsayayya shi ake kira da hasalin ƙarfin zuciya afu......"

   Wata kafurar dariya yayi yana me furta." To yanzu shi mijin ki da yay gaskiyar yana ina?, Matsalar shi ne tausayin da yake da yayi  sanadiyyar wargajewarsa tare da daular sa a cikin wannan masarauta..... A yanzun wannan masarauta ta wace!, kuma zataci gaba da tafiya ne bisa ƙarfin ikon da nake da A kuma tsarina ADEENERH, Idan kuma zaki iya Dakatar dani Bismillahhhhhhhhh....... Ni kuwa ina nan zaman tsimayinki....... "

   Dubanshi tayi duba irin na kai ɗin zuciyar ka baƙa ce bame kyau bace, tare da furta. " Ka tuna cewar duk abin da ka aikata cin amana ne Afud!, kuma shi addininmu be ko yar damu cin amanar kowa ba, duk kuma wanda yaci amana to kuwa tabbas yana haɗuwa ne, Da mummunar ƙarshe bame kyau ba, kuma kana ƙarfin ikon da kake jin kana da UBANGIJI se ya kawo wanda zai yi maganin ka, Ka da kayi tunanin wannan tsoratarwace, ƙa'idace ta wannan rayuwa, domin UBANGIJI ya daɗe da ƙadarta hakan. Domin Kuwa duk abinda ka shuka to ka tabbatar da cewar shi ne wanda zaka girba ko ba jima Afud.... " wata mahaukaciyar dariya ya fashe da ita tare da sanya ƙafarsa ɗaya ya to kare inda take zaune, kafin ya dubeta tare da furta. 

  "To yanzu faɗamin abinda mijin ki ya shuka ya kuma girba?, To ni neeeeee, Ni ne wanda ya shuka ya kuma ni ne wanda ya girba ADEENERH AL_HASSAN EMAAR's KUWAIT....." Wani kyakkyawan mari ta sauƙe masa wanda ya zo masa a bazata, don haka ta sama damar tunkuɗeshi, tana yin cikin fadar da mugun gudun da yafi kama dana waɗanda suka taɓa samar taɓin hankali. Duk inda ta wuce se kaga kowa na ranta wa ana kare domin bama kansa kariya, domin ita ɗin mahaukaci yace wacce ta sheƙe mijinta da hannuwanta, ta kuma jefa jaririn data haifa cikin rijiya. Duk wanda yayi ƙoƙorin dakatar da ita kuwa tureshi take yi da ƙarfin tsiya ta wuce. Haka harta isa mahaukacin parlourn da duk waɗan da suka dace ne a cike, Kowan ta shiga bi da ido tin daga kan fadawan fada har ƙarshen su. Se take kallar tamkar an sanja komai, domin kuwa kowa da komai sun sha ban ban, har zuwa kan Parlour dake da wani irin girma da tsari dayaji adon royal chairs gold and golden tamkar  zinarai sai kyal ƙyali suke da ɗaukar ido. sai komai daya kawata parlourn  yazamto shima gold and golden colour ɗin ne, har zuwa kan splits aircon kusan guda goma da suke bama parlourn sanyi,Ko ina na  parlourn taci gaba da bi da kalla tako ta  ina sabida wata irin dukiyace ta musamman da aka sake  narkarwa a parlourn. Wanda tsabar haɗuwa da girman parlourn yasan ya sammm alkalamina yayi ƙanƙantan daya kamata in rubutawa masoya irin kayatuwar parlourn kawai, Wani irin tsayawa cak tayi tare da sauƙe wata nannauyar ijiyar zuciya akaro na babu. Wani irin kallo ta kaima inda Sarki Afud da aka bama riƙon ƙwarya tayi,  Tana jin wani abu daya tsayar mata a  maƙoshinta, kafin kuma ta tattaro duka jarumta da karfin gwiwanta. Tana ratsa dogon parlourn kai tsaye zuwa inda yake zaunen, Zaune yake cikin shiga ta alfarma shiga kuma irin ta sarakuna, ɗago da kansa yayi yana mata kallo ɗaya, wanda ya sanya shi saurin yin ƙasa da idanuwansa sakamakon  idanuwanta daya kalla  masu tsananin kwarjini da firgitarwa. Duk da yaso ruɗewa amma yayi saurin daidaita kansa yana  tattaro nutsuwa da karfin halinsa baki ɗaya. Duk da kasancewarta mace amma ba ƙaramin kwarjini take masa ba, shi yasa ma ya sanya ake buga mata allurar mahaukata,  kasancewar kwarjin mahaifinta ne ta ɗauka reality tare dasu AK EAGLE da ZAYD EMAAR'S. Karasowa tayi kuma cikin sanyin jiki da fargaba ta masa kallo ɗaya kafin ta rufe idanuwanta da suka fara canza wa, tana kaiwa ɗurkushe  gaban Afud ɗin. murya na rawa tace  "Me martaba! Ina twin nawa dana haifa?, don ALLAH ko ba za ku bani komai ba amma ku bani Abu KAMAALA, ku bani shi ina son sa karku rabani dashi!, ku bani da yara na zamuyi nesa can daku, nesan da ba zamu sake koda waiwayar inda kuke ba" Idanuwan daya  watso matane yasan ya jikinta ɗaukar  mazari a matakin farko, ga shirun da duka jama'ar fadar suka ɗauka shi ne babban tashin hankali da azabtarwa wa tata zuciyarta. Sake duƙar da kanta tayi domin rayuwar ta da kuma duniyar ta take da buƙata. Wani  irin rushewa da kuka tayi,  domin ita wllh tsoro take! Tsoron rasa miji da kuma twins ɗin ta take yi, domin gani take shirunsu kawai zai iya sanya zuciyarta bugawar lokaci guda.  A ƙalla sai da ta ɗauki tsawan wani lokaci me ɗan yawa tana rairai kukan ta, Tamkar kuma daga sama taji dakakkiyar muryarsa cikin ikon mulki da bada umarnin cewa. A mata allurar ta domin ciwon haukarta ya motsa, Tin har take tambayar mijin da ita ce ta sheƙe da hannuwanta, tare da jaririn data haifa, amma kuma wai tana ƙiran twins, ai ko daga haka ya sake tabbatar musu da cewar tabbas ta gamu da taɓin hankali.  Wani irin miƙewa tsaye Adeenerh tayi cikin  fusatar zuciya da ɗacin murya ta furta. "Waɗan nan kalaman  marasa kan gado fa Afud!, Kodai duk a cikin giyar mulkince?, To gaba ɗayanku ina son ku  sani cewar gudun hatsaniya ne ya sanya mutanen da suka kasance mugwaye a cikin zuriyarku ne yake  sanya mutumin daya kasance shiru shiru yake fusata!. Inason ku dukanku ku sanarma azzaluman cikinku cewar idan har akaci gaba da buga irin wannan game ɗin akwai masu  tarwatsa masarautar, domin kuwa don su yi gyara aka haife su zasuyi hakan zasuyi  hakan za su yi ?. Uwa uba kuma ta tsatson Zakin da kuke tunanin kun kayar, ko shi ya kayu ku sani mu jinin EMAAR's da kuma ASH ba masu kayu bane, domin jinin mu ya kasance tafasa yake a kowacce  daƙiƙar da zata shuɗeee sake tafasa da fusata yake...yake...yakeeeeee........


   Haka taci gaba da faɗin tana kuma tafiya baya luuuuuu sakamakon allurar da wata nurse dake kula da ita tabi ta bayan ta tana soka mata.... 


MAFARIN buɗewar ƙaddarar kenan...... 



*TOUCH* 

      *ME* 

          *NOT*


*33yrs Later*

 *BAYAN SHEKARU TALATIN DA UKU *

_ABUJA NIGERIAN_

 Chat mee or call🤙 

  08104493215

Hhhhhhhhhh to ai shikenan 😅🥰 

A gimtse 🫰 🙃♥️✅


Haka ɗanɗanonsa yazo🤗🤗 🤗 🤗🤗  🤗  🤗 .. 


*BY AMMEY LAYLERH ✍️ ✅*

Post a Comment

Previous Post Next Post