ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode.
*Ina fatan yadda na fara lafiya, Allah ya sanya na gama lafiya. Ƙirƙirarren labari ne, idan akwai abin da ya yi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata arashi ne*
Page1
Bismillahirahmanirrahim
Daji Ajiyar Allah! La'asar sakaliya, a lokacin da hasken rana ya fara disashewa, ta doshi yamma za ta faɗi, duhun magariba na ƙoƙarin shigowa ya maye ragowar hasken da ranar ta bari kan ta ƙarasa faɗuwa.
Gamayyar bishiyoyi ne, dogaye da da madaidaita, haɗe da ciyayi da ga mabanbantan tushe, suka haɗu suka yiwa dajin ƙawanya. Zai iya kasancewa abin sha'awa ga wanda ya zo yawon buɗe ido, idan har bai san mai dajin ya ƙunsa ba.
Ga wanda ya san abin da ya ƙunsa kuwa, zai kasance wuri mafi razani, firgici da kuma tashin hankali.
Gudu take yi a tsakanin rayuwa da mutuwa, tana rungume da wani zani a ƙirjinta, babu yadda za ayi daga nesa ka gane me ta rungumo haka take wannan uban gudun.
Ƙafafuwanta babu takalmi, jikinta babu mayafi, duk da yanayin garin babu zafi, amma laɓɓanta sun bushe tamkar dutsen da ya shekara ruwa bai zuba a kansa ba, babu alamar tana gane in da take jefa ƙafarta. Duk da wannan mawuyacin hali da take ciki, ta bawa abin da take rungume da shi muhimmanci sosai da sosai.
Cikin rashin sani, tayi karo da wani abu da ita kanta ba ta kai ga tantance ko meye ba, sai dai ƙarfi da nauyin abun ya sanya ta faɗi ƙasa, take ta saki wani marayan kuka, a lokacin da jini ya fara zuba daga ƙeyarta.
Sai a lokacin abin da take rungume da shi ya tsala kuka, saboda firgitar da ya yi shima.
Jariri ne ɗanyen goyo, cibinsa ko faɗuwa bai yi ba, jikinsa duk busashshen ƙazantar haihuwa da alama yaron ya kwan biyu, amma ko ruwa bai taɓa gani ba balle a wanke wannan ƙazantar!.
**************
Domin sauraron Part 14 Complete Audio gashi nan a Ƙasa 👇 👇 👇
Cikin garin Kano, unguwar ɗorayi tinga, misalin ƙarfe huɗu na yammacin ranar Alhamis, wani matsakaicin gida ne, cikin rukunin gidajen dake ɗan ƙaramin layin, kallo ɗaya zaka yi wa gidajen, ka san na masu ƙaramin ƙarfi ne, duba da yanayin kwatoci da kuma kasancewar gidajen awon igiya, ba magudanan ruwa, babu layuka masu kyau, kowa da in da fuskar gidansa ta kalla, haka zalika kowa in da ya ga dama yake sako kwatar gidansa, wasu da gyara wasu babu, ga gidajen 'yan ƙanana tamkar wani zai hau kan wani.
"Wai ba zaki fito ki je mini aiken ba, har sai gawayin ya ƙare tukuna?" Cewar wata matashiyar dattijuwa, da take zaune a gaban kurfoti, hannunta riƙe da mafici tana firfitawa, gefe ga farantin silba ɗauke da garin tuwon masara a kai.
Wata yarinya ce ta fito daga wani ɗakin da yake bayan matar, hannunta ɗaya riƙe da hijjabinta, ɗaya kuma sai matsar hawaye take yi.
Matar ta kalleta ta ce "Kukan me ki ke yi?"
Aikuwa kamar mai jiran ƙiris, cikin sangarta yarinyar ta ce "Ba Huzaifa bane ba ya....
"Ni yi mini shiru, haka dai kuka iya faɗa kamar kuna ganin hanjin junanku, idan na hana ki zuwa in da yake ai ba zaki hanu ba, maza ki ɗau kuɗin nan ki je mini gidan Laure, ta baki kuka ta sittin, daddawa ta arba'in sai manja na naira ɗari ki kawo mini canjin, na yi maza in kaɗa miyar nan kan magariba".
Kwaɓe fuska yarinyar ta yi ta ce "Wai yau ma miyar kuka za ayi Innalillahi wa innalillahi raji'un"
Baki buɗe ta bi Yarinyar da kallo, cikin hasala ta ce "Idan na kaɗa kukar kar ki sha, zaki ɗau kuɗin ki fita ko sai na yi fatali da kanki a wurin?"
Ta durƙusa ta ɗau kuɗin, ta zura hijjabinta ta nufi hanyar fita, a ranta tana jin gara ace yau babu abin da zasu ci, da wannan tuwon kamar na ibada.
Cike da kashedi matar ta ce "Idan kin ga dama kuma ki je ki zauna, kar ki yi sauri kiga yadda zan yi da ke, ko ki biyewa yara ki tsaya shashanci a hanya"
Ba to ko waiwayo ba, ta yi gaba abinta tana kalle-kalle.
Gidansu ƙawarta Habiba ta fara biyawa, ta tarar da maman Habiba a tsakar gida ana yi mata kitso, ta durƙusa ta gaida Maman Habiba, sannan ta ce mata wurin Habiba ta zo.
Habiba ta fito daga ɗakinsu tana kallonta tana murmushi, ta ƙaraso in da take tsaye ta ce "Ruma ina zuwa ne?"
Cikin muryar Raɗa Ruma ta ce "Dan Allah Habiba aron tayar Sani zaki bani, Mama ce ta aikeni so nake nayi sauri na je na dawo".
Habiba ta ce "Kaii, Ruma kin san Sani yafi kashi ɗoyi, kar na baki ki je ki salwantar da ita, daga ni har ke mu shiga uku".
Ruma cikin ƙwarin gwiwa ta ce "Wallahi ba zata salwanta ba, ke dai ki aramini, so nake na yi gudu na ne na dawo".
Habiba ta ja Ruma soron gidansu, ta duba saman kejin kajin da ke cikin ɗan tsukakken zauren gidan, ta ɗaukowa Ruma tayar Sani ta bata ta ce "Dan Allah Ruma ki kula, kar wani abu ya samu tayar nan, ki yi maza mi garata ki je ki dawo"
Ruma tayi murmushi ta ce "Kar ki damu, yanzu zan fyalla naje na dawo, ina son tayar nan ta sani dama ya bar mini, 'yar dandaɓasa da ita, yanzu zaki ga naje na dawo".
Habiba tayi murmushi ta ce "To shikenan, yi sauri kafin ya dawo".
Ruma ta dafe kan taya, ta garata ta dinga zura gudu ta lunguna kamar wata namiji ba mace, ba ta tsaya da gara tayar ba har sai da ta isa gidan Laure.
Ta yo sayayyarta ta gama, ta fito ta kuma garo taya zata tafi gida, can ta hango wasu 'yan makarantar allonsu, a ƙofar gidan Hanne mai markaɗe suna 'yanta, ba tare da ta tuna da kashedin Mama ba, ta ajiye kayan aiken da canjin haɗi da tayar da ta aro, ta shiga aka hau 'yanta da ita.
Kasancewar ƙwararriya ce a harkar shagala da iya rinto, nan da nan wasa ya ɗau zafi, ganin tana ta cinyesu a 'yantar ta hanyar rinto, sai wasa ya koma faɗa, daga nan aka hau dambe, a wurin Ruma ta kifar wa da wata markaɗenta ga ta da ƙarfi kamar doki. Da ƙyar wani mutum ya raba faɗan, Ruma ta haɗa yaran mutane ta zane musu jiki, sai da mutumin yayi mata barazanar zai gayawa yayanta, sannan ta haƙura da damben.
Yarinyar da suka yi damben, ganin an musu asarar markaɗe, an kifar ga duka, ya sanya ita da ƙannenta suka fasawa Ruma Manjan da ta sayo wa Mama, suka kwashe canjin aiken, suka farke ledar aiken suka gudu, daddawar ma sai da ƙyar ta tsinto wasu, an fasa ledar kuka duk ta watse.
Ta kwashi sauran kayan, ta tafi gida, tana tafe tana tunanin wace ƙaryar za ta jirgawa Mama, dan ta kaucewa faɗanta, dan a duniya ba ta son faɗan Mama, gefe guda kuma tana tunanin irin dukan da zata naɗawa Safiya idan suka haɗu a makaranta allo, saboda abin da suka yi mta.
Lokacin da Ruma ta isa gida tuni an fara kiraye-kirayen sallar magariba, domin wasu masallatan har sun tayar, sai a lokacin ta sake shan jinin jikinta, tsoro ya ziyarce ta.
A soro ta rakuɓe tana leƙa cikin gidan, ta hango Mama a gindin rariya tana alwala, Mama ta ɗaga ido tayi mata kallo ɗaya, ta mayar da kai ta cigaba da alwalarta.
Cikin sanɗa Ruma ta shiga tana satar kallon Mama, ta ji mai Maman za tace mata, amma ta ji ba tace mata komai ba.
Ta lallaɓa ta ajiye abin da yayi saura na aiken, ita ma ta faɗa banɗaki tayi alwala.
Ta lallaɓo falo, ta tsaya a bayan Mama ta tayar da sallar ita ma.
Mama ta idar, ta tashi ta fita tsakar gida, ta duba abin da Ruma ta kawo mata na aiken, taga irin aika aikar da Ruman ta yo.
Ta dawo falon tana jiran Ruma ta idar da salla ta dirar amata, amma Ruma ta ƙi idarwa, ta hau nafifilin babu gaira babu dalili, matar da wataran sallar ma sai Mama ta haɗa .mata da duka take yi, amma yau sai gashi har da nafila.
Can da Mama taga abin nata bana ƙare bane ba, sallar taƙi ƙarewa, ta damƙo wuyanta ta baya ta zaunar da ita, ta kalleta cikin haɗe fuska ta ce "Gidan uban wa ki ka je dana aike ki?"
Cikin tsoro Ruma ta girgiza kai ta ce "Ba ko ina Mama"
"Ƙarya kike yi, zaki gaya mini ko sai na murɗe miki wuya, tun la'asar na aike ki amma sai magariba kika shigo mini, gidan uban wa kika je?"
Cikin zazzare ido Ruma take jujjya kai tana rantse-rantsen rashin gaskiya, "Wallahi Mama ban je ko ina ba"
Cikin tsananin Fushi, Mama ta ce "Ba zaki gaya mini ba!"
"Mama wallahi dagaske nake"
"Assalamu alaikum" aka yi sallama a tsakar gida.
Mama ta amsa sallamar tana huci, wani matashin saurayi ne ya shigo ɗakin, yana faɗin Mama na dawo".
Mama ta ce "Sannu da zuwa"
Ya amsa da yauwa, ya dubi Mama dake tsaye a kan Ruma, Ruma sai wulƙita ido take, kamar ta zagi sarki.
"Mama meyafaru ne?" Yayi Maganar yana son jin ba'asi.
Cikin ɗacin rai Mama ta ce "Saboda tsabar iskanci na yarinyar nan, nan da gidan Laure, ta je ta sayo mini kayan miya, tun bayan la'asar sai yanzu ta shigo mini gida, babu aiken babu dalilinsa, kuma babu canjina, nayi-nayi ta gaya mini in da ta tsaya amma taƙi faɗa sai rantse-rantse take yi".
Ya kalli Ruma ya ce "Ba zaki faɗi inda kika tsaya ba, kuma ina canjin? Ko zuwa ki ka yi ki ka kashe mata kuɗi tunda kin saba"
Cikin tsiwa da rashin kunya, Ruma ta ce "Ban sani ba, kai kuma waye ya saka da kai, zaƙin zaƙafere mai gida feraye kabewa, ai ba da kai ake yi.....
Kan ta ƙarasa Mama ta rufe bakin nata da duka, da sai da tayi zaton bakinta ya fashe.
Ja da baya tayi da sauri, ta dafe bakinta tana yarfe hannu, saboda ta ji zafin dukan nan sosai da sosai.
Ya jinjina kai ya ce "Mama ƙyaleta, ba dai bata da kunya ba, kar ki wahalar da kanki, ki bari mai sunan Baba ko Haidar su shigo, sai su tuhumar miki ita".
Jin abin da ya faɗa ya sanya Ruma ta yi wata irin zabura, ta ce "wallahi Mama gaskiya na gaya miki, dan girman Allah kar ki gaya musu, canjin ne suka zube a hanya, na faɗi ƙasa man jan ya fashe dan Allah kar ki gaya musu".
"Wallahi Mama ƙarya take yi, kin san dai ƙaryarta ba ta salla, ki tuhumeta bari mai sunan Baban ya dawo zaki ci ubanki".
Cike da gamsuwa Mama ta ce "Ai hakan za ayi tun da ba ta da mutunci"
Ya fakaici idon Mama ya yiwa Ruma gwalo.
"Mama kin ganshi ko yana mini dariya, dan Allah kiyi haƙuri"
Banza Mama tayi da ita, ta bawa Huzaifa kuɗi ya kuma yi mata wani cefanen.
Rumaisa ta koma gefe tayi tagumi, zuciyarta na ta zullumin halin da zata iya shiga, idan har aka sanarwa da Mai sunan Baba ko Haidar abin da ta yi, gashi ko giyar wake ta sha ta san ba zata iya gayawa Mama haƙiƙanin abin da ya faru ba.
Salati kawai take yi, tana roƙon Allah ya rufa mata asiri, kar Mama ta gaya musu, ƙasan zuciyarta kuma tana yi wa Huzaifa Allah ya isa da ya bawa Mama shawarar ta haɗata da su Haidar.
Ta na tsaka da tunanin, ta jiyo Mama da Huzaifa suna hirarsu a tsakar gida, kamar ba ita ta gama faɗa ba.
Suna yi mama tana ƙarasa aikin miyarta.
Sallama aka yi a tsakar gida, Ruma ta rikice, dan kusan muryoyinsu duk kusan iri ɗaya ne, ta ɗan nutsu ne da ta tuna mai sallamar muryarsa ba ta kai ta su Haidar fashewa ba, kuma shi dama sanyin hali ne da shi.
Jiyo Mama tayi tana faɗin "Fodiyo, an dawo"
"Eh Mama, ya gidan?"
"Alhamdilillah, sannu ka je ka watsa ruwa kafin nan na gama miya"
Usman da Mama ke kira da Fodiyo ya ce "To Mama, ga wannan" yayi maganar yana ajiye mata leda.
Miƙewa Ruma tayi tana leƙa window, tana son gane me ye a cikin ledar da Fodiyo ya kawo.
A ranta ta ce "Allah ya sa kifi ya kawo, idan kifi ne a bani kasona, dan idan aka saka a wannan baƙar miyar ban sha.
Ba ta kai ga gano meye a ledar ba, idanunta suka sauka a cikin na dodonta, da ya shigo gidan ko sallama bai yi ba, gani tayi tamkar yayi mata wani irin mugun kallo, ko dan dai a tsorace take ne oho.
Mai sunan Baban Mama kenan, Umar faruk.
Cikin takunsa na ƙasaita ya ƙaraso tsakiyar tsakar gidan, sannan ya yi sallama.
Hannu Ruma ta ɗora a ka, muryarta ƙasa_ƙasa ta ce "Na shiga uku, yau kashina ya bushe ƙayau idan ya san me nayi".
Tun daga sallamar da ya yi, bai cewa kowa komai ba, shi ma ya ajiyewa Mama ledar da ke nasa hannunsa, ya wuce ɗakinsu.
Bai jima ba ya fito tsakar gida, ya ɗau buta zai yi alwala.
Ruma ce ta fito kamar munafuka, ta ɗan risuna ta ce "Yaya Faruk sannu da zuwa"
Ɗaga ido ya yi ya kalleta, bai amsa ba ya mayar da kansa ya cigaba da alwala.
Cikinta ya ɗuri ruwa, ta ɗau tsintsiya ta tafi falon Mama ta hau shara a daren, kai da gani ka san sharar ba ta domin Allah bace ba.
Huzaifa ya faki Idon Mama ya bi Rumaisa falon, ya dinga leƙata yana tuntsura mata dariya.
Ba dan tana cikin yanayi na tashin hankali ba, babu abin da zai hana su kafsa faɗa da Huzaifa a daren nan, amma ta san biyewa Huzaifa su yi faɗa alhalin Faruk yana gidan nan, wata babbar matsalar ce, mai zaman kanta, dan ƙarshe sai tayi kuka.
"Ba zaki fito ki ɗebi Abinci ki ci ba?" Mama tayi maganar cikin ɗaga murya, yadda za ta jiyota.
Daga ɗaki Ruma ta ce 'Mama na ƙoshi"
A ƙufule Mama ta ce "To uban me ki ka ajiye da zaki ci, ba zaki fito ki ci Abinci ba?"
Ruma ta ɗan tura baki tayi shiru.
Usman ya ce "Ai kin san kin yi maƙiyin nata tuwo, mussaman miyar kuka da ma wata miyar ce ba wannan ba, ƙila ta ci"
Mama ta ce "Abin da nake da shi ba shi zan dafa na bata ba, zan fasa girki ne dan ba ta cin tuwon?".
Cikin kakkausar muryarsa Umar ya ce "Ki ƙyaleta, tun da a cikinta zata zuba, ta kwana da yunwa mana".
Mama ta gyaɗa kai ta ce "Ai shikenan"
Muryarsa kawai da ta jiyo, sai da ta sake shiga cikin tashin hankali, tsananta addurta ta yi, a kan Allah ya rufa mata asiri kar Mama ta gaya masa ta yi mata laifi.
'yan mazan nan suka kewaye Mama, suna ta hira kowa da abin da yake ce mata, banda mai sunan Baba, da yake duba wayarsa, ba tare da ya tanka musu ba.
Jin suna ta hira, Mama ba ta gaya masa tayi laifi ba, ya sanya take ta murna, tayi maza ta yi sallar isha'i ta shimfiɗa katifar ta ta kwanta.
Ta cigaba da Addu'a a cikin zuciyarta.
"Assalamu alaikum" aka yi sallama a tsakar gidan.
Suka amsa baki ɗaya, Suka zubawa yaran da suka shigo ido mace da namiji.
Duk da akwai wutar lantarki da fari Mama ba ta gane yaran ba sai daga baya.
Suka gaida Mama da su Umar, Mama ta kallesu ta ce "Habiba ya aka yi me?"
Habiba ta ce "Ruma tana nan?"
Umar yayi caraf ya ce "Yaya aka yi?"
Kasancewar sa mutum mai tsanain kwarjini, sai da Habiba ta ɗan ruɗe sannan ta ce "Dama ɗazu ne da aka aiketa ta zo ta ce na bata aron taya, zata jewa Mama aike, to tayar ta Sani ce, ta ce zata dawo da ita kuma haryanzu shiru".
Mama cikin mamaki ta ce "Taya kuma?"
Habiba ta jinjina mata kai.
Gaba ɗaya Ruma ta manta da ta je ta aro taya, sai yanzu da ta ji maganar Habiba, dan tun da aka kwashi damben nan a nan ta yasar da tayar ta yo gida.
Ɗora hannu tayi a ka ta ce "Na shiga uku, Habiba shikenan kin kasheni".
Mama ta ce "Kina ina zo nan, mara kan gado, babu yadda ban yi dake ba a kan ki gaya mini in da kika tsaya, amma kika ce ke baki tsaya ko ina ba, ashe yawon aron taya kika tafi ko, ko ina sai kin nuna hali ƘANWAR MAZA, ina ke ina taya ban da hauka, zaki fito ki basu abarsu ko kuwa?"
Jikinta na tsuma ta fito ta tsaya daga bakin ƙofar falon Mama, tana satar kallon Umar, amma taga kamar ma bai san me ake yi ba.
"Ma.m.maama.. wallahi dan nayi sauri ne, ya sanya na aro tayar, kuma wallahi na manta na barota a wajen gidan Hanne mai markaɗe".
Mama ta riƙe haɓa kawai, tama rasa me zata ce gaba ɗaya.
Huzaifa ya ce "Wannan yarinyar idan kina da rabon yin hankali Allah ya shiryeki, ina ke ina taya kina mace?"
Mama ta kalli in da Habiba take tsaye ita da ƙaninta ta ce "Dan Allah ku yi haƙuri, tun da ta fita nima nake zaman jiranta, ban aiketa ta je ta karɓi kayan kowa ba, da safe in Allah ya yarda zan turata ta je ta dubo muku" Mama tayi ta basu haƙuri, suka juya suka tafi.
Mama ta zauna ta dasa mita, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, su Usman na tayata, ita kuwa Ruma da ta san ba ta da gaskiya, sai ta ƙule a kan katifarta, zuciyarta sai bugawa take tana jiran jin me Yaya Umar zai ce, amma shiru bai ce komai ba.
Har suka watse daga tsakar gida, Mama ta shigo ɗakin, ta sameta ta rufe ido tana baccin ƙarya, still Mama ta cigaba da mita, sai da Ruma ta ji kamar ta tashi ta barwa Mama ɗakin ta huta, saboda Mama mitarta ba ta ƙarewa sam, gefe guda tana yiwa Allah godiya da Dodonta bai yi magana ba.
Wani irin bacci ne mai daɗin gaske yayi awon gaba da ita. A cikin baccin nata babu zato babu tsammani sai ji tayi an yi sama da ita da hannu ɗaya.
"Wayyo Allana, Innalillahi wa innalillahi raji'un, warin hannuna na hagu zai karye Mama!" Sai da ya dungurar da ita a tsakar gida, suka yi ido huɗu, ta ga wanda yayi mata wannan aikin.
Jikinta ne ya hau kyarma, dan idonsa kawai idan ransa a ɓace yake abin tsoro ne.
A ƙasan zuciyarta ta ce 'Shikenan tawa ta ƙare, Allah ya sa na cika da kyau da imani!.
Ayshercool
08081012243
[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin mu, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724
P2
Kasa ɗauke idanunta tayi daga kallonsa, saboda azabar firgici da razanar da ta yi.
Ya janyo kujera ya zauna a gabanta, ya ɗan ƙura mata ido, sannan cikin kaushin murya ya ce "Gidan uban wa kika tafi da ta aikeki, tun la'asar ba ki dawo ba sai magariba?" Yayi Maganar yana tsareta da ido.
Kasancewar akwai wutar lantarki, ya sanya fes take kallon fuskarsa da idonsa.
"Ba magana nake yi miki ba, ki ka tsare ni da ido?" Ya daka mata tsawa.
Zabura tayi ta yinƙura za ta yi magana,amma ya sake cewa "Kuma wallahi kika yi mini ƙarya sai na ci ubanki a daren nan"
Jiki na rawa ta fara zayyane masa yadda aka yi tun bayan fitarta.
Huzaifa tun da yaga Yaya Umar ya shiga ɗakin Mama ya jiyo kukan Rumaisa, ya sha jinin jikinsa, dan ya san yau sai yadda Allah ya yi.
Mama kuwa girgiza kai kawai ta yi, jin Yadda Ruma take faɗar gaskiya saɓanin ɗazu da ta yi mata ƙarya.
Umar ya ce "Namiji ce ke da zaki tafi aron taya?" Ta sunkuyar da kai tayi shiru.
"Kuma me nace miki a kan dambe a hanya, karya ce ke?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
Ya ɗora da cewa "Wato ke duk wani abu da za'a gaya miki sai dai ya shiga ta kunnenki na dama, ya fita ta hagu ko?"
Ita dai tayi shiru tana rarraba ido.
"Kyaci ubanki, tashi ki kama kunnenki tun da ba zaki yi hankali ba".
Maraicewa tayi zata fara yi masa magiya, amma da yayi mata wani mugun kallo, ba shiri ta miƙe ta durƙusa ta hau kamun kunne.
Gaba ɗaya Huzaifa ji yayi bai ji daɗi ba, maimakon a hukuntata tun a lokacin amma sai da aka bari ta fara bacci, za a sakata kamun kunne, ya tsaya ta ƙofa yana leƙen tsakar gidan ya san yanzu zata galabaita, gashi babu wanda ya isa ya hana Yaya Umar abin da yayi niyya sai Hassan ɗin sa wato Abubakar Sadik, shi kuma baya nan.
Umar ya nutsu yana duba litattafansa, Rumaisa kuwa sai tangaɗi take tana neman ta faɗi, amma yayi banza da ita, dan ta san idan ta faɗi ko ta tashi ba zata iya ɗaukar wani hukuncin ba.
Tun tana kuka ƙasa-ƙasa har ta fara yi da ƙarfi, saboda azabar gajiyar da ta yi.
"Tashi" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. Ta ɗago duk ta haɗa uban gumi, ga hawaye da majina duk a fuskarta.
"Kukan uban me kike yi?"
Cikin kuka ta ce 'Yaya na gaji ne, dan Allah kayi haƙuri ba zan sake ba, na tuba"
"Da alama haryanzu baki yi laushi ba, yi zaman babur tun da kin gaji da kamun kunne"
Babu kalar izayar da Yaya Umar bai yi mata ba a daren, har Sai da Mama ta ji babu daɗi a ranta, amma tuna cewar yarinyar ba 'yar goyo bace ba, ya sanya tayi banza ta cigaba da laziminta.
Aliyu ne ya fito daga ɗakinsu, cikin damuwa ya ce "Dan Allah Yaya kayi haƙuri ka ƙyaleta haka ta je ta kwanta dare yayi, wallahi ta horu, kuma ga gobe in Allah ya kaimu da makaranta".
A fusace Umar ya kalleshi ya ce "Ka ɓace mini daga gabana ko sai na haɗa da kai?" Ran Aliyu ba ƙaramin ɓaci yayi ba, kawai ya girgiza kai ya shiga banɗaki.
Sai da ya tabbatar da ta galabaita sannan ya ce ta zauna ta huta, shi kuma ya tashi ya fita.
Ta dinga kuka kamar ranta zai fita, saboda jin cinyoyinta take kamar babu nama a cikinsu sai rodi, saboda azabar sagewa da suka yi, ƙashin bayanta ma ban da azabar ciwo babu abin da yake yi mata.
Yaya Umar na fita, Huzaifa ya ƙaraso in da take yana mata sannu cikin tausayawa kamar ba shi ne ya gama bawa Mama shawarar ta haɗata da Yaya Umar ba.
Ya je ya ɗebo ruwa ya bata, ta karɓa ta kafa kai tana sha tana kuka. Ta gama sha, ya karɓi kofin ya ajiye yana goge mata hawayen fuskarta.
"Uban me kake a nan wurin?" Basu ji dawowar Yaya Umar ba, sai maganarsa kawai suka ji, suka yi tsuru-tsuru.
"Zaka tashi ko sai na haɗa da kai?" Jiki na rawa Huzaifa ya tashi, ya koma ɗakinsu.
Ya kalli Ruma da ke ta ajiyar zuciya, ya tabbatar ta galabaita, ya san yanzu haka jikinta na ciwo, ya jefa mata leda a jikinta ya ce "Maza ɗauki ki shanye"
Jiki na rawa ta ɗau ledar, doguwar jarka ce cike da youghurt mai sanyi a ciki, ta ɗaga kai ta sha rabi, yana tsaye yana kallonta, ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Na ƙoshi".
Jin bai ce komai ba ne ya sanya ta ɗago ta kalleshi, ganin yana mata wani irin kallo ne, ya sanya ta cigaba da sha tana yamutsa fuska, da ƙyar ta shanye, ta ajiye robar tana jiran umarni na gaba.
"wuce ki je ki kwanta"
Da ƙyar da yinƙura ta tashi, ƙafafuwanta na ta rawa saboda ciwo, ta shiga ɗaki.
Tana shiga ta tarar da Mama na salla, ta faɗa kan katifa tana kuka.
Mama har ta idar da sallar ba tace mata komai ba, ta cigaba da kukanta har bacci ya ɗauke ta.
Cikin bacci ta ji Mama na ɗala mata duka a cinyarta "Tashi" duk da yadda ta ji zafin dukan, amma ta buɗe idonta a hankali ta kalli Mama, ba tare da ta ce komai ba.
"Saboda tsabar rashin hankali, ki kwanta ki yi fitsari a kwance, ke ba jaririya ba ba 'yar yaye ba" jin abin da Mama ta faɗa ne ya sanya ta miƙe zumbur, ta ganta luntsum a cikin fitsari.
Waro ido ta yi ta ce "Na shiga uku, wallahi na zata a mafarki ne, dan Allah kiyi haƙuri"
Mama cikin ɓacin rai ta girgiza kai ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, zaki tashi ki fita kije ki gyara jikinki ko kuwa?"
Sannu a hankali ta sauka daga kan katifar, saboda yadda jikinta ko ina yake yi mata ciwo, saboda punishment ɗin da Yaya Umar ya sanya ta.
Da ta fita tsakar gida da rarrafe ta ƙarasa banɗaki, ta wanke jikinta ta dawo ta canza kaya, ta jingine katifar tayi kwanciyarta a ƙasa.
Har ga Allah, tana jin yadda fitsarin ya matseta, amma ta ji gandar tashi, saboda bacci take ji sosai, ga kuma ciwo da jikinta yake yi, dan haka ta cigaba da baccinta, da ta ganta a banɗaki ta zaci a gaskene ta saki fitsarinta.
Tana jin yadda Mama ke ta mita, amma ita ko a jikinta, wani nannauyan baccin ne ma yayi awon gaba da ita.
Da Asuba ma an kai ruwa rana kan Mama ta samu Rumaisa ta tashi ta yi salla, dan sai da ta yi iƙirarin haɗata da Yaya Umar sannan ta tashi ta yi sallar.
Ta idar da salla Mama tayi mata maganar shirin makaranta, amma ta tura baki ta ce "Ai kina gani jiya mai sunan Baba yana azabtar da ni baki hana shi, ni bani da lafiya, ba zani ba cinyata kamar an mini ɗorin karaya haka nake ji na"
Mama ta yi mata shiru ta cigaba da laziminta, Huzaifa ne ya fara shigowa ɗakin Mama ya gaisheta, suka gaisa ya tambayi Mama mai za'a ɗora na karin kumallo?.
Mama ta ce "Bari gari yayi haske, sai a sayo gasara, ka cewa Yasir ya feraye maka dankali, sai a soya"
Huzaifa ya jinjina kai ya miƙe, har zai fita idonsa ya sauka a kan katifar Rumaisa, ya ɗan yi turus ya dubi Mama ya ce "Mama ba dai fitsarin kwance yarinyar nan tayi ba?"
"Gashi kuwa kana gani, ai Yarinyar nan sai addu'a kawai".
"Innalillahi wa innalillahi raji'un, su Balama an yi asarar kunnuwa, ba sai ki saka ta fitar miki da ita daga ɗaki ba, sai ɗakin ya fara wari tukuna, abinka da fitsarin gardiya bana jariri ba, tashi shashasha" ya ƙarasa maganar yana zuba wa Rumaisa duka a ƙafa.
A gigice ta tashi zaune ta raba ido, tayi zaton Mama ce ta daketa, amma taga Huzaifa a kanta.
"Me nayi maka zaka dakeni?" Tayi maganar a ƙule.
"An dake ki ɗin, tashi ki fitar mata da wannan katifar daga ɗaki, mai abin kunya ƙatuwa da ke kina fitsarin kwance"
"Ba zan fita da ita ɗin ba, uban shishshigi ko ina ruwanka, tun da ba a kan ka nayi ba, kuma ruwa ne ya zube ba fitsari nayi ba".
"Au Mama ƙarya take yi miki kenan, ba zaki tashi ba?"
Cikin tsiwa ta ce "Ba zan tashi ba"
miƙa hannu yayi, ya janyota ya ɗagata, ya ce "Wallahi sai kin fita da katifar nan kin wanke kayan da kika yi tsiyar a kan su". Idan da sabo Mama ta saba da wannan halin nasu na faɗace-faɗace, gashi Huzaifa ya bawa Rumaisa kusan shekaru shida, amma faɗa kamar suna ganin hanjin junansu.
Mama ta sharesu ta ƙi ko kallon in da suke, Rumaisa ta dinga turjewa tana kwarara ihu.
Basu yi aune ba suka ga Yaya Umar a tsakiyar ɗakin, take suka yi cirko-cirko suna kallonsa.
Cikin kaushin murya ya ce "Meye haka karnuka ne ku?"
Suka girgiza kai a tare.
"Me kai mata take wannan ihun, da idon Mama bai sanya kun daina ba?".
"Fitsari ta yi a kwance, shi ne nace ta fita da kayan"
Cikin mamaki Umar ya kalleta ya ce "Fitsarin kwance kuma? Kina me kika yi fitsari?"
Cikin rauni ta ce "Wallahi Yaya tsautsayi ne, kasa tashi nayi"
"Tsautsayin uban wa? Kwashe kayan ki fita ki wanke ƙazamar banza kawai".
Haka ta ja katifar ta fita da ita tsakar gida, ta kwaso kayan da ta yi wa fitsari ta hau wanki.
Huzaifa ya faki idon Yaya Umar ya dinga yi mata dariya.
Duk wanda ya fito tsakar gida ya ga katifar Rumaisa sai ya ce me ya fito da katifar, Huzaifa sai yayi farat ya gaya musu ai fitsarin kwance ta yi.
Tausayinta ne ya kama Usman, ganin yadda take kuka, kuma ba ta saba yin fitsarin kwance ba, ya je ya karɓi kayan ya tayata.
Kowa da abin da yake faɗa a kan Ruma, wasu na mata Addu'a shiriya wasu kuma na yi mata faɗa har da zagi.
Tamkar gidan 'yan mata, haka zaratan samarin nan suka kama aikin gida, wasu na wanke-wanke, wasu shara da Abin karyawa, kan gari ya ƙarasa haske, hatta ruwan da Rumaisa zata yi wanka, an dafa ta haɗa ta yi wanka.
Haka suka jeru a tsakar gida, tare da Mama suna karyawa, Rumaisa kuwa sai shan kunun take da ƙyar tana yamutsa fuska.
Can ta kalli Mama ta ce "Mama Kununa bai ji suga ba, yayi tsami da yawa".
Haushi ya kama Mama ta ce "Amma a gabanki aka zazzage sugan kowa ya ɗiba ko? Kuma kin san ya ƙare"
Ta ture kofin kunun ta ce "Nifa dama kunun nan gudawa yake sani, gashi bai ji suga ba, ni cikina ma har ya fara ciwo"
Umar kawai ya girgiza kai, Rumaisa ba zata taɓa zaman mintuna goma lafiya ba, ba tare da tayi abin da za a yi mata magana ba.
Haidar ya kalleta, ya zura hannu a Aljihunsa ya ɗauko ɗari biyu ya bata ya ce "Jeki wurin Mamuda ya baki buredi da suga, akwai ruwan zafi sai ki haɗa shayi ki sha"
Washe baki tayi, ta ce "Allah dai ya biya da aljanna, gadanga na Mama" ta ɗau kofin kununta ta turawa Mama kunun ta ce "Mama ki shanye kunun na bar miki" tayi waje.
***
Da ƙyar ta ƙarasa makaranta yau, saboda ciwon cinyoyi da take yi, sakamakon horon da Yaya Umar ya bata a daren jiya.
"Ruma hatsari kika yi ne?" Cewar wata matashiyar yarinya sa'ar Ruman, gannin yadda take tafiya da ƙyar.
Ta haɗe rai ta ce "Me kika gani?"
"Gani nayi kina tafiya da ƙyar, kamar wadda ta warke daga karaya"
Cikin gatse Ruma ta ce "Eh, tirela ce tabi ta kaina, da ta wuce na taso na taho"
"A'a Allah ya baki haƙuri"
Duk da yadda jikinta babu daɗi, hakan bai hanata faɗace-faɗace da neman rigima ba, dan idan ba tayi hakan ba ace lafiyarta ƙalau ba.
Bayan an tashi ba ta tsaya ko ina ba ta tafi gida, tana zuwa ta tarar da katifarta a tsakar gida kamar yadda ta barta.
"Mama yanzu dan Allah a nan aka bar mini katifata, sai anyi baƙi sun tambayi ba'asi ace fitsarin kwance nayi?"
"Au ba ke kika yi ba, ni nayi kenan?"
Ta ƙarasa ta zauna a kusa da Mama ta ce "Haba Mama, kema fa kin san tsautsayi ne, rabona da fitsarin kwance tun ina jairiya, tun ban fi wata huɗu ba na daina fitsarin kwance" wani irin kallo Mama tayi mata, jin uwar ƙaryar da ta saki.
Mama ta ce "Tashi ki cire Uniform, kiyi wanka ki zo kiyi salla, ki tsefe wannan kan naki, ƙazamar banza da yake ban yi magana ba, baki ga dama kin mayar da kai kin tsefe ba, kuma wallahi ya kai gobe in Allah ya kaimu baki gama tsifar nan ba, sai na zaneki".
Hannu ta saka ta shafa kanta, ƙanann kitso ne a kanta, a ƙalla guda arba'in da ɗoriya, Mama ta bata kuɗi ta je ayi mata kitson hannu guda biyar, saboda ba ta son tsifa, amma ta karɓi kuɗi a wurin Yaya Usman ta je aka yi mata ƙanana.
Ta san yau ko Mama zata kwaɗanta ta ta cinye ba zata iya gama wannan tsifar ba, haka nan ta tashi ta je ta yi wanka, ta yi alwala ta saka wasu kayan. Ganin Mama ta tada salla, ta leƙa Window ta ga Usman da sallaya a hannu zai tafi masallacin juma'a, ta ɗau hijjabinta ta bi bayansa.
Sai da ta fito ƙofar gida sannan ya kalleta ya ce "Ina zaki?"
"Masallaci mana" ta bashi amsa.
"Kin tambayi Mama?"
Ta gyaɗa masa kai alamar eh.
Ya ce "Shikenan muje" ya sanyata a gaba suka tafi masallaci.
Mama ta daɗe tana yiwa Rumaisa Addu'a bayan ta idar da salla, kullum cikin Addu'a take yi mata, amma tana girma tamkar ana sake turata, ko alamar hankali babu a tare da Rumaisa.
Da suka dawo daga masallaci tana kallon Rumaisa, ba ta ce mata uffan ba, Rumaisa sai raragefe take yi, tana sauraron ko Mama zata yi mata magana amma taga ta shareta.
Ba tare da ta yi tsifar ba, ta ci Abincin ranarta tare da Yaya Aliyu, ya siyo kifi ɗauri biyu, ya bawa Mama ɗaya ya ce gashi nan duka gidan, ɗauri ɗaya kuma suka ci shi da Rumaisa.
Bayan sallar la'asar, ta ɗau allonta ta tafi makarantar allo.
Tana zuwa Habiba ta tare ta da harara, tare da sheda mata cewar Sani ya ce sai ya yi mata dukan tsiya, idan ba ta biya shi tayarsa ba.
Tsaki Rumaisa tayi ta ce "To, ya kasheni ya huta mana, tayar banza da ta wofi, shi bai san tsautsayi ba"
A ƙufule Habiba ta ce "Au hakama zaki ce? Ki zo girma da arziki na ara miki tayar, amma ki je ki ɓatar ko a jikinki?"
"To tayar da kuɗi ya saya? Idan da kuɗi ya saya ya faɗi kuɗinta, yayyena su biya shi"
Habiba da ta gama fusata ta ce "Dalla can, uwar meye a gidan naku, banda gayyar maza da tsiya, sai ka ce wata uwar kuka ajiye, har kike a faɗi kuɗin tayar a biya"
"Ku kun ajiye wata uwar ɗin ne, da kuna da wani abun ai babarku ba zata sayar da fanke da safe ba" Tayi maganar tana murguɗa baki.
Cikin rawar murya Habiba ta ce "Kar ki sake ki zagar mana uwa"
"Ni ban zagi babarku ba, ni dai na san fanke take sayarwa, fanken naku ma mai Shegiyar tsada, ƙanana kamar ƙuli-ƙuli, dan ranar Yasir ya ce har kiyashi ya gani a cikin fanken" kan Rumaisa ta rufe bakinta, tuni Habiba ta shaƙo hijjabinta, zata rufeta da duka.
Abinka dai mai nema a duhu, balle ya samu a sarari, nan Rumaisa ta zage ƙwanji ta tabattarwa da Habiba ita ɗin ƘANWAR MAZA ce.
Abin takaici da malami a gefe yana biyawa wasu allo suka harƙe da dambe.
A fusace ya miƙe ya saka bulala ya zane musu jiki, musamman Rumaisa, tsabar masifarta ya sanya baya son ta a ajinsa, kullum cikin rigima take, ga allonta sai yayi wata ba tayi wani rubutun ba, ga daƙiƙanci da surutu.
Idan da abin da Rumaisa ta tsana bai wuce duka ba, ta ji zafin dukan bulalar da Malam Ashiru yayi mata ba kaɗan ba, dan haka ta koma gefe tayi shiru tana kuka. Ta rasa meya sanya ya tsaneta haka.
Habiba kuwa da ƙawayenta, suka ƙudiri aniyar idan aka tashi sai sun naɗawa Rumaisa duka saboda suna jin haushinta suma, a kan damben da aka yi a ƙofar gidan mai markaɗe ranar Alhamis, gashi ta zagi fanken babar ƙawarsu.
Ana tashi cike da takaicin dukan da Malam yayi musu, Rumaisa ta ɗau allonta ta nufi gida, sai share hawaye take. Sai dai yau babu tsokana a hanya, babu neman magana saboda bayanta sai raɗaɗi yake na dukan da malam yayi mata, gashi ba ta warke daga ciwon jikin punishment ɗin Yaya Umar ba.
Babu tsammani ta tarar da su Habiba a wani lungu suna jiran isowarta.
Turus tayi tana binsu da kallo kamar ba ta sansu ba.
Babu ko ɗar ta cigaba da tafiya tana yinƙurin ratse su ta wuce.
Shan gabanta Habiba ta yi ta ce "Ke kin isa ki tafi, ba dai ni kika zaga ba, kika kuma zagi babarmu ba, wallahi yau sai kin gane kuskurenki, kuma wallahi Sani ma ya ce sai kin biya shi tayarsa.
Ɗaya daga cikin yaran ta ce "Ai wallahi yau sai kin daku, haka nima ranar kika zubar mini da markaɗe, zaki gane baki da wayo".
Bin su Rumaisa take da ido, sai kurari suke amma an rasa wadda zata kaiwa Rumaisa duka.
Sake yinƙurin wucewa tayi, amma Habiba ta janyo Rumaisa ta baya, yaran suka fara kai mata duka.
Tayi kukan kura, ta ɗaga allonta saukewa Habiba allonta a fuska, wani uban ihu Habiba ta kurma, jin danshi a hancinta.
Tamkar namiji a filin dambe, haka Rumaisa ta zage ita kaɗai ta dinga dukan yaran nan, yadda ta dunƙule hannu tana kai naushi, kai ba ka ce 'ya mace bace.
Da ƙyar da siɗin goshi wani mutum ya rabasu, saboda Rumaisa akwai taurin kai, zuciyarta a bushe ana rabasu tana cigaba da kai duka.
Ta ɗau allonta ta nufi gida, tana ta huci, duk da dukan da tayi musu sai dai jikinta duk yayi tsami ita ma. Dama ga jikin nata babu daɗi ji
Sai dai kash, tuni wasu daga cikin yayyen yaran maza suka samu labari, suka yi gaba zasu datse Rumaisa a hanya, su zaneta.
Ayshercool
08081012143
[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin mu, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
Page3
'yan matasan yaran maza sun girmi Rumaisa, kuma duk da haka ƙarfin namiji da na mace ba ɗaya bane ba.
Tana cikin tafiya ta ji ana ke!ke! Ta tsaya waiwaya ta ga da wa ake.
tawagar yara ta gani sun nufota gadan-gadan, tana ganinsu ta san masu dukanta ne, sam bata karaya ba, maimakon ta gudu sai ta durƙusa ta fara kwasar duwatsu, ta shirya duk wanda ya kawo kai, sai ta ƙwale masa kai da dutse.
Amma a haka sai da wasu daga cikin su suka cim mata.
Sani Yayan Habiba, ya na zuwa ya kwarfeta da ƙafarsa ta faɗi ƙasa, wani danƙo ya ɗauko a aljihunsa, ya fara dukanta da shi, duka take kai masa ko ta ina da allonta har ta samu ta tashi tsaye da ƙyar a kan ƙafafuwanta.
Ta yi kukan kura ta kafa masa haƙora a kafaɗarsa, tsananin azabar zafi ya sanya ya kurma wani uban ihu ya ja da baya, dan har ƙashinsa ya ji haƙoram Ruma, sai ka ce mayya.
Ganin ta gigita Sani, wasu daga abokan nasa kuma suna fama da raɗaɗin jifan da suka sha, ya sanya ta durƙusa ta ɗauki takalminta da hijjabinta a hannu, ta tsula da gudun tsiya.
Rufa mata baya yaran suka yi, suna a taro ta, amma kamar walƙiya haka take sheƙa da gudu, ba ta tsaya a ko ina ba sai da ta kai filin ball ɗin su Yaya Aliyu. Suna tsaka da ball, sai ratsa cikin ƙartin mazan nan take sai gata a tsakiyar filin da maza ke uban gudu suna ball, ta cinma Aliyu a tsakiyar filin ƙwallon ta rirriƙe shi.
Mamaki ne ya kama shi, ganin hijjabinta a hannu, kanta sai hula idanunta duk sun yo waje, tana ta haki tana waige-waige.
Riƙeta yayi yana tanbayarta lafiya? Wasu daga cikin abokansa suma suka tsaya suna tambayarta ko lafiya, amma taƙi magana sai ajiyar zuciya take yi.
Aliyu ya ja ta gefe, ya sanya mata hijjabinta, ya kalleta a tsanake ya ce 'Menene?" Shiru ta yi bata yi magana ba sai sauke numfashi take.
Haushi ne ya fara kama shi ya ce "Dan ubanki menene, me aka yi miki kika biyoni nan cikin maza?" Yayi mata maganar a hasale.
Fara gaya masa abin da ya faru tayi, kuka ya ƙwace mata.
Ɗan shiru yayi sannan ya ce "Amma ina fatan baki yi kukan a gaban yaran ba?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
"Kin taimaki kanki, dan da kin yi musu kuka wallahi sai na ƙara miki".
Cikin shesheƙa ta ce "Ban yi ba"
Aliyu ya ce "Bari na canza kayana muje, ɗaya bayan ɗaya ki rakani gidajensu sai naci uban yaran nan, dani suke zancen"
Ya zaunar da ita a gefe, aka cigaba da tambayarsa meya sami Rumaisa ya ce musu babu komai, su cigaba da ball ɗin su, shi zai tafi.
Su Sani kuwa tun da Allah ya sanya Ruma ta ɓace musu, suka haƙura da binta, amma suka yi alwashin sai sun kuma saka ranar da zasu naɗa mata duka, dan tayi musu ɓarna sosai.
Suna tafe a hanya, Aliyu ya ce "Ke amma ba a banza zan je rama miki ba, sai idan ki yadda zaki wanke mini kayan ball ɗina da takalmina".
Cikin hanzari ta ce "Eh na yadda, zan wanke maka"
ya ce "To shikenan"
Ya sakata a gaba har ƙofar gidan su Habiba, Aliyu ya aika yaro yace a kira masa Sani.
Sani ya zata a cikin abokansa ne wani yake nemansa, yana ta fama da kafaɗarsa saboda cizon da Rumaisa tayi masa, sai ka ce an sare shi da manjagara a wurin ba haƙorin ɗan Adam ba, ga Habiba ita ma sai kuka take, leɓe yayi suntum ya kusa haɗewa da hancinta, bakin yaƙi rufuwa saboda dukan da ta sha da allo a fuska, sai da bakin ya fashe, banda dukan da ta yi mata a ka da allon, da take jin tamkar an mata rawani da tukunyar ƙarfe saboda nauyin da kanta zuwa fuskarta yayi mata, ba ta iya banbance a wani sashi na fuskarta hancinta da bakinta suke.
Sani ne ya fito yana waige-waige, yana neman wanda ya aiko a kirashi, Aliyu yayi caraf ya danƙe shi.
Zazzare ido Sani ya hau yi, Aliyu ya ce "Kai, kaine ka tattaro abokan ka ka daki Ruma ko?"
Cikin fitsara Sani ya ce "Nima ƙanwata ta daka, kuma ta ɓatar mini da tayata".
"Kuma saboda kai mahaukaci ne, sai ka tattaro abokan ka maza su daketa, saboda baka da tarbiyya ko? Meyasa ba ka bari ƙanwarta ka ta rama da kanta ba?".
Fizge-fizge Sani ya fara, yana yiwa Aliyu rashin kunya, aikuwa Aliyu ya dinga kifa masa mari, har sai da bakin Sani ya mutu, fuskarsa duk tayi ja. Ya saka shi a gaba zuwa gidan abokansa da suka yi yinƙurin dukan Rumaisa.
Duk da irin ɓarnar da Ruman ta musu da duwatsu, hakan bai hana Aliyu kama yaran ɗaya bayan ɗaya ya zane musu jikinsu ba, sannan ya saka Ruma a gaba yana rarrashinta suka tafi gida.
Ko da suka je gida, yanayin Ruman Mama ta kalla ta ga kamar ba ta da gaskiya, amma ta share ba ta kula ta ba, dan idan ta biye wa halin Rumaisa kullum sai ta daketa.
Da daddare bayan sallar isha'i duk suna zaune a tsakar gida, Rumaisa na ta tunanin me zata ci yau, dan yau ma maƙiyin na ta Mama tayi, wato tuwo, Allah ya sani yau ba ta jin za ta iya cin wannan tuwon, gashi haryanzu ranta a ɓace yake a kan abin da ya faru, dan marin da Yaya Aliyu ya yiwa Sani bai gamsar da ita ba, ji take ba zata huce ba sai ta fasa masa kai, ko ta hankaɗa shi kwata, ga kuma tuwon nan da Mama tayi ya sake ƙara mata ɓacin rai.
Yasir ne yayi sallama, hannunsa riƙe da leda, duk suka amsa masa, banda Rumaisa da ta yi zurfi a tunani.
In da Rumaisa take ya ƙarasa, ya jijjiga kanta ya ce "Ke tunanin me kike?"
Haɗe rai ta yi ta ce "Meye kuma na dakar mini kai?"
Yasir ya ce "To kwalba uwar sharri, ni ban dakar miki kai ba"
Tsaki ta yi ta ce "Ai na saba in dai ƙarya ce"
Dire mata baƙar ledar yayi a cinyarta, ya wuce ɗakinsu.
Buɗe ledar tayi ta kwance, gurasa ce fal ta masu tsire a ciki.
Murmushi ta yi ta ɗaga murya ta ce "Na gode rabin ran"
Daga ɗaki ya ce "Ko ba rabin rai ba, tun da na baki abin duniya ba, uwar son zuciya"
Rumaisa ta ce "kai dai Allah yayi maka albarka, kamar ka san ba son wannan tuwon nake ba, tunani kawai nake me zan ci? Wannan tuwon ne yake toshe mini kai bana gane karatu sosai, Allah dai ya biyaka rabin raina "
Murmushi Yasir yayi ba tare da ya kuma cewa komai ba.
Ya gama abin da yake ya fito tsakar gida, zamansa yayi dai-dai da shigowar dodonsu, wato Yaya Umar.
Cikin muryarsa ta ƙasaita yayi sallama.
Duk suka amsa masa, ba tare da ya kula kowa ba, ya ajiyewa Rumaisa leda da indomie ya ce "Tashi ki dafa mini" tabbas ba dan Mai sunan Baba ne ba ba zata yi ba, ita a rayuwarta tana son ko aiki zaka sanyata, ka lallaɓata shi kuwa mai sunan Baba bai san wannan ba, ya bada umarni a bi kawai ya sani mutum ya ƙi kuma jikinsa ya gaya masa.
Haka ta tashi ta je ta kunna wuta ta ɗora masa.
Rumaisa na tsaka da aiki, suka ji sallama, kai da jin yadda aka yi sallamar, ka san babu alheri a tare da mai sallamar.
Mama ta amsa tana faɗin maraba.
Jin yanayin yadda aka yi sallamar ne ya sanya Rumaisa faɗuwar gaba, ta tsaya cak tana sauraron abin da zai biyo baya, dan ta san babu wanda zai aikata abin da za a zo ana musu wannan sallamar a daren nan idan ba ita ba.
Mama tayi wa matar nuni da tabarma dan ta zauna, amma matar ta ce "A'a ba ma sai ma zauna ba, ai abin bana zama bane na"
Ɗan zuro kai Ruma tayi daga Kitchen, domin taga wacece, tozali tayi da Habiba da ƙaninta Sani.
Ita ba zuwansu ne ya ɗaga mata hankali ba, babu tantama ta san ƙararta aka kawo, amma tashin hankalin ta, Mai sunan Baba yana nan.
"Ban sani ba ko ke ce ki ka sanya 'yar ki ta dinga abin da ta ga dama a cikin unguwar nan, saboda tsabar rashin mutunci da rashin ta ido, ta kama mini 'ya ta daka, kalli fuskar Habiba, kuma duk da haka bai isheta ba, ta ɗauko yayanta suka biyo Sani gida shima suka daka, haka ake yi fisabilillahi wallahi sai da na biya na kai ta chemist aka yi mata allura.
Dawowata gida kenan bana nan kawai na tarar da yarinya baki ya haye, ya fashe ta riƙe kai sai kuka take, shima Sani kalli fuskarsa duk shatin mari tsakani da Allah Wannan adalci ne?" Ta ƙarasa maganar tana haska fuskar Habiba. Fuska ta kumbura suntum, bakin ko rufuwa baya yi, leɓen sama ya ɗage ya kusa danganawa da hancinta, duk dadashi a waje.
Duk da halin da Rumaisa take ciki na fargaba, amma sai da ta ƙunshe baki tayi dariya ƙasa-ƙasa, saboda yadda fuskar Habiba ta koma kamar an naushi fura.
Jiki a sanyaye Mama ta ce "Dan Allah dan annabi kiyi haƙuri, yaran yanzu ne sai addu'a kawai, kin ga ni ban ma san tayi ba, daga ita har yayan nata babu wanda ya zo ya gaya mini, ban ma san waye ba a cikin yayyan nata ba, amma kiyi haƙuri".
Haidar yayi gyaran murya ya ce "Mama nine, su meyasa yaran ba a tambayesu me suka yi mata ba, hijjabi a hannu suka biyota da bulalai zasu daka.....
"Rufe mini baki ban tambayeka ba" Mama ta dakatar da haidar cikin tsawa.
Mama tayi ta bawa Babar su Habiba haƙuri, amma ba kunya babarsu Habiba ta ce "An bar yara babu tarbiyya su yi ta abin da suka ga dama, saboda tana taƙamar ita ƙanwar maza ce, sai tayi ta isakancin da ta ga dama, sai ta kashewa yarinyar fuska ta cuceni, wallahi ban da ana maƙota da sai na kai maganar wurin hukuma, dan ba zan yadda ba, ita ta dakar mini 'ya, shi kuma ya zo ya zage ƙwanji a kan ɗana".
Cikin muryarsa mai ban tsoro da babu alamar wasa a cikinta ya ce "Ke ya isheki haka malama, ke kamar ba uwa ba, kawai ki zo gaban mace kina cewa 'ya'yanta basu da tarbiyya, tana baki haƙuri kina cigaba da ƙanan maganganu, kar Allah ya sanya ki haƙura ɗin, ki kai duk in da zaki kai ki je ki faɗa, kuma ko yau wani ya kuma yinƙurin taɓa Rumaisa a unguwar nan, sai mun nuna wa duniya ƙanwar maza ce, fice ki bawa mutane wuri"
Mama zata yi magana, amma mai sunan Baba ya haɗe rai, ya girgiza mata kai, tare da nunawa Babarsu Habiba hanyar fita.
Jiki na rawa ta saka su Sani a gaba suka fice, duk girma da ƙanƙantar mutum, babu wanda Umar baya yi masa kwarjini.
Sai da ya tabattar sun tafi, sannan ya dubi ƙofar Kitchen ɗin ya ce "Ke kuma fito nan munafuka" aikuwa kamar munafukar ta fito tana sunkuyar da kai ƙasa.
Ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Muna zaman zamanmu lafiya aka haifeki, shegiya kamar rainon iblis, duk gidan nan babu mai fita ya ɗauko magana sai ke, tana zaman zamanta kin saka an zo har cikin gida ana gaya mata maganganun banza saboda ke, kai ma saboda hauka dan me zaka biye mata ku je kuna dukan 'ya'yan mutane? Waye ya aiketa ta tsokane su?".
Ran Aliyu ya ɓaci, ya harzuƙa ya ce "Bafa maganar hauka a nan, yarinyar nan hijjabi a hannu suka biyota, ba dan filin ball ɗin mu na hanya ba, haka zasu haɗu su yi mata duka, yara maza ba mata ba, har sun fara dukanta baiwarsu ce ita, ko kuma ce musu aka yi ba ta da gata?.
"Shut up! Ita ka san me tayi musu, wannan Yarinyar da rashin jin tsiya, ai gara su zane ta gobe ba ta kuma ba, ki cigaba da zuwa ki na janyo mata magana, wallahi ba zaki ɗora mata hawan jini a banza ba, da ki cigaba da ɗauko mata magana ana zuwa ana gaya mata maganar banza, gara na takeki na murɗe miki wuya ki mutu kowa ma ya huta".
Tun da Mai sunan Baba ya fara sababi, Sentence ɗinsa na ƙarshe ne ya baƙanta mata rai, wai ya murɗe mata wuya ta mutu su huta. Ta yi shiru ya gama bala'insa ya ce ta wuce ta cigaba da yi masa aikinsa, ya fice.
Rumaisa tana aikin tana kuka, wato ma ba'a sonta, wai da suna zaman zamansu aka haifeta, ta hana mahaifiyarsu kwanciyar hankali.
Usman ne yayi tsaki ya ce "Wallahi Mama ɗan nan naki yana da matsala, na yi shiru ne kar na tanka masa yayi mini tijara, amma ba damar yarinya ta motsa sai faɗa, ke Ruma" ya kirata.
Ta goge hawayenta, ta fito daga Kitchen ɗin.
Ya kalleta ya ce "Duk shegen da ya takaleki kar ki raga masa, ki ci uabnsa idan yafi ƙarfin ki muna nan, yaran unguwar nan marasa mutunci, ki ka zama nusara raina ki zasu yi, duk ɗan da ya miki ki ci ubansa ko mace ko namiji mun tsaya miki".
Mama ta ce "Zinnuraini, kai ne kake zigata ta ɗauko magana?".
"A'a Mama bance ta ɗauko magana ba, amma duk wanda yayi mata, ta rama babu nusari a cikinmu, ƙanwarmu ba zata zama nusara ba, mu ci uban mutum ya zo kawo ƙara mu ƙara masa"
Martanin Yaya Usman ne ya ɗan sanya hankalin Rumaisa ya kwanta, ta kammala yiwa Yaya Umar aikinsa ta je ta nemi wuri ta kwanta, ko gurasar da Yasir ya bata ba ta ci ba.
Tana kwance lamo a kan katifarta, ta ji muryar Huzaifa a kanta yana cewa ki cigaba da ɗauko magana, ai gara ya murɗe miki wuyan ki mutu kowa ma ya huta da tijararki da rashin hankali.
Banza ta yi masa, kamar ba da ita yake ba, dan idan ta ce zata biyewa Huzaifa faɗa za suyi, kuma a kowane lokaci mai sunan Baba na iya shigowa, yadda yake a ƙule da ita ta san sai jikinta ya gaya mata, idan ya dawo ya tarar suna faɗa da Huzaifa.
Da safe bayan gaisuwa ba abin da ya haɗata da mutan gidan, tana kwamce a ɗaki, 'yan mazan suka gyara komai na gidan, suka ɗora abin kari. Ko ta kan abincin safen ba ta bi ba, ta saye gurasarta a hijjabi, ta ɗau allonta ta tafi makarantar allo.
Sai dai ashe tuni labari ya iske shugaban makarantar su, a kan faɗan da suka yi jiya, malam babba ya tara su ya ce sai ya zane su.
Idon Rumaisa yayi tsilli-tsilli, dan kusa bulalar malam Babba akwai ɗan karen zafi.
Kan Malam Babba ya kai ga zuwa ya yanke musu hukunci, ta zari allonta ta kwasa da gudu, ya tsaya yana ƙwala mata kira, amma tayi burus ta bar makarantar ta kama hanyar komawa gida, dan a rayuwar Rumaisa ba ta ƙaunar duka ko kaɗan.
A soro suka yi karo da Yaya Usman zai fita, ya tsaya yana kallonta, har zata wuce ya ce "Wai me kika dawo yi ne gidan nan yanzu, ina Makarantar kuma?"
Ta tura baki ta ce "Kashi nake ji shine na dawo gida"
Tsaki yayi ya ce "Haka dai kika iya, wannan uban cin da kike yi, ba dole kullum ki kasance cikin zawo ba, baki da aiki sai kashi da tusar tsiya" banza tayi masa ta raɓe shi ta wuce tana murguɗa masa baki, ba tare da ya sani ba.
Ta shiga cikin gidan tana ciccin magani, ihuu tayi, tare da tsalle ta nufi in da wani dogon matashi ke zaune, mai tsananin kama da Yaya Umar, sai dai banbancinsu, Yaya Umar fari ne shi kuma bai kai shi haske ba, sannan shi wannan fuskarsa ɗauke take da murmushi saɓanin fuskar Yaya Umar.
Babu tunanin komai, ta faɗa jikinsa tana murmushi.
Shima rungumeta yayi yana murmushi ya ce "Autar Mama, tun ɗazu zaman jiran dawowarki nake yi".
"Babban Yaya, yaushe ka dawo?"
"Tun ɗazu na dawo, nace kina ina aka ce kin tafi makarantar allo".
"Wayyo daɗi, yaushe rabon da na ganka, gaba ɗaya gidan babu daɗi, kowa ya tsane ni, har da cewa na ishesu wai kamar su murɗe mini kai su huta".
Waro ido yayi ya ce "Wane mara ta idon ne yayi wannan iƙrarin a gidan nan?" Ta waiwaya sannan a hankali cikin raɗa ta ce "Waye banda ƙaninka, ya tsaneni wallahi".
Yayi murmushi ya ce "Ai ba wanda ya isa ya taɓa mini auta ina raye, ai gani a gidan na dawo".
Wani matashin ne ya sake fitowa, yana faɗin "Iya rigima, ya halinki?"
Sake waro ido ta yi ta ce "Yaya Abdallah".
Ya amsa da "Na'am uwar rikici".
"Haɗa baki kuka yi duk kuka dawo yau kenan?"
Abdallah ya ce "Eh haka ne, su Baba Atine suna ta gaisheki, sun ce ke ba kya zumunci"
Ta taɓe baki ta ce "Waye zai barni na je garin, ai ni ina son zumunci kai ni ne ba ayi" Gaba ɗaya sai ta manta da damuwarta, ta shantake suna hira.
Sai da aka jima sannan ta shiga ɗaki ta ajiye allonta.
Sabgoginta ta shiga yi, ta zage ta ce ita zata yi wa su Babban Yaya girki, abincinta zasu ci.
Aikuwa faɗa ya kaure, Huzaifa ya ce ba zasu ci jagwalgwalonta ba su zasu yi girkinsu, ƙarshe Yaya Sadik ya ce na Rumaisa zai ci.
Zuwa Azahar gida ya ɗinke kowa ya hallara a falon Mama suna cin Abincin rana, Sadik sai jinjinawa ƙoƙarin Rumaisa yake ta yadda ta iya girki mai yawa haka, Huzaifa da Yasir kuwa sai kushewa suke yi.
Zaratan maza ne su bakwai sai Rumaisa, Mama a hankali take binsu ɗaya bayan ɗaya da kallo, tana tuna baya.
Hadiza shine sunan Mama na gaskiya, haifaffiyar garin Kano ce, unguwar mandawari. A nan ta taso tayi karatun boko da islamiyya, sai dai tana aji uku na Sakandire, ta haɗu da mahaifinsu Rumaisa, Muhammad Aminu a nan unguwar sabon sara, amma asalinsa ɗan garin Katsina ne, yana zuwa gidan wan mahaifinsa ne a Kano yana koyan harkar kasuwanci, a nan suka haɗu suka yi aure, kan Hadiza ta gama makarantar sakandare.
Haihuwar fari Mama ta haifi tagwaye Abubakar Sadik da Umar faruk sune 'ya'yanta na fari, Sai ta kuma haihuwar Usman, sai Aliyu, Abdallah da Huzaifa, Yasir ne kawai ba ɗan ta ba, ɗan ƙanwar mahaifinsu Rumaisa ne, ta haife shi da kwana kaɗan Allah ya yi mata rasuwa, a lokacin Mama tana shayar da Huzaifa sai ta haɗa su ta shayar da su tare, ba zaka taɓa cewa ba 'yan biyu bane ba, ko ba ita ce ta haifesu ba.
Mama gaba ɗaya tayi tunanin ta daina haihuwa, saboda galibi bai fin shekara biyu uku a tsakanin yaran take haihuwa, amma bayan haihuwar Huzaifa sai da ya shekara takwas, kawai ta daina ganin al'ada, sai ga cikin Rumaisa.
Tun da Allah ya sa ta haifi Rumaisa, kowa ya ɗauki soyayya ya ɗora mata, kasancewarta kallabi a tsakanin rawuna, kowa babban burinsa ya faranta mata.
Mahaifinsu Rumaisa, mutum ne mai matuƙar kulawa da son iyalinsa, kasancewar Ruma ce kaɗai 'yar sa mace yafi kowa ji da ita, ba shi da magana sai ta Rumaisa, Akwai tsananin ƙauna da shaƙuwa a tsakanin Ruma da mahaifinsu, dan kusan tafi son sa a kan Mama, saboda Mama akwai faɗa, Abba kuwa lallaɓata yake. kwatsam Allah ya yi masa rasuwa tana da shekaru uku kacal a duniya, bayan yayi gajeriyar rashin lafiya.
Bayan rasuwar sa sai da Rumaisa tayi cuta kamar ba zata rayu ba, saboda alhini. Dangin mahaifin su Rumaisa suna da zumunci sosai, sun so a rarraba musu yaran su riƙe su, amma Mama ta ce ba ta son a raba nata kan yaranta, dan haka ta ce su ƙyale mata su.
Haka tayi ta ɗawainiya, 'yan uwa da abokan arziki suna taimaka mata da abin da zasu iya
Tasowar Rumaisa a cikin 'yan mazan nan, wannan ya ɗauka wannan ya sauke ya sanya ta taso tamkar namijin ita ma. Ba ta jin magana ga rashin tsoro, ga tsiwa da ɗan karen surutu da iyayi, gashi lokacin da take tasowa girma ya fara kama Mama duk tayi sanyi, dan haka ta mayar da Mama kamar wata kakarta ba uwa ba.
Mutum ɗaya take tsoro shi ne Baban Mama, Yaya umar mai sunan baban Mama, Allah yayi masa kwarjini shi ko irin wasan nan na yarinta baya yi, ba shi da abokai, ga tsare gida ba shi da fara'a ko walwala baya son shiga mutane sam, idan kaga an taka masa burki kai tsaye to Yaya Sadik ne. Mama tana matukar girmama shi saboda sunan mahaifinta da yake da shi.
Yanzu Rumaisa tana aji huɗu na Firamare, Abubakar yana Dutse yana karatu, babu wanda yake da cikakken ƙarfin ɗaukar ɗawainiyar gidan gaba ɗaya, amma kowa babban burinsa ya nemo ya kai gida, komai suka samu mahaifiyarsu da ƙanwarsu kawai suke tunani.
"Hajiya Mama, ya naga kina ta kallonmu ne kamar da baƙo a cikinmu".
Mama tayi murmushi ta ce "Allah nake yiwa godiya, da ya sanya duk ku ɗin nan nawa ne, Allah ya dafa muku ya ƙara haɗa mini kanku"
Suka amsa da "Amin"
Yasir ya ce "Mamanmu, maganin kukanmu Allah ya ƙara hore mana, mu gantataki fiye da kowace irin uwa a duniya"
Huzaifa ya ce "Hmm kamar gaske, nan fa kake zuwa da abin duniyarka ka hanata, ka hana kowa ka bawa waccan yarinyar mai kama da Akushin"
Murguɗa baki tayi tana fari da ido ta ce "Tubarkallah zuƙul-zuƙul maye ya ci kansa da kansa, wallahi ni bana kama da Akushi, son kowa ƙin wanda ya rasa"
"Ke dalla ware, meye son kowa ƙin wanda ya rasa, aba Kamar gurguwar akuya" Yasir yayi maganar yana dariya.
Haushi ne ya kamata ta buɗe baki za tayi rashin mutunci, ta sanya idonta a cikin na Umar, ta haɗa maganar da zata yi, da lomar abincin ta haɗiye.
Suka gama cin abincin, Yasir ya kwashe kwanuka, ya fara ƙoƙarin wankewa, Huzaifa ya shigo da tsintsiya zai share ɗakin, Umar ya ce ya ajiye tsintsiyar ya bawa Rumaisa ta share.
Haushi ne Yakamata ta lura tun da aka kawo ƙararta ya tsaneta, dama can ba wani shiga shirginta yake yi ba.
Bayan ta kammala sharar ta nemi wuri za ta kwanta Mama ta kalli kan Rumaisa, da ta fara tsifa, tayi rabi ta bar rabi ta ce "Fita ki bar mini ɗaki, karki sake shigowa sai kin gama wannan tsifar.
Fitowa ta yi ta na tura baki, tana nema ta yi kuka.
"Autar Mama, meya ɓata miki rai ne?" Cewar Yaya Abubakar da yake ƙoƙarin shiga ɗaki.
Dama ƙiris ta ke jira, dan haka ta fara kuka "Ba mama ce ta koreni daga ɗakinta ba, wai sai na gama tsefe kaina ba, ni mama ta tsaneni".
Girgiza kai ya yi ya ce "Yi haƙuri ki daina kukan, bari na zo na tayaki tsifar"
Haka suka zauna ya samu kibiya ya tsefe mata kan tsaf, suka wanke gashin, ya ce da safe zai bata kuɗin kitso.
Mama ta na kallonsu ba ta kula su ba, ta cigaba da sabgoginta.
Abdallah yana ta dube-dube a kitchen, ya ci karo da allon Rumaisa, duk gefensa ya karye, ga rubutun jiki yayi baƙi ƙirin, ba ta sake wani ba.
Ya fito da allon a hannunsa ya ce "Ruma, wannan allon naki yaushe zaki yi wani rubutun?" Ta haɗe rai ta ce "To ban iya ba, sai na iya zan wanke".
"Haka dai, ba kya ja a ko ina, daga arabin har bokon, Allah ya sa su zaneki idan ki ka je sati mai zuwa, baki wanke allon kin yi wani rubutun ba, gandamemiya da ke amma haryanzu a izifi biyu ki ke"
Sai da yayi wannan maganar ta tuna yadda malam Babba ya dinga ƙwala mata kira amma ta gudo gida, yanzu sati mai zuwa ta yaya zata je makarantar allon? Kuma muddin abin da ta yiwa malam ya zo gidan nan, ta san ta kaɗe".
"Astagfrillah, ni 'ya su meyasa haka ne, garin in gujewa wani hukuncin sai na faɗa wani tarkon, ya zan yi da raina?.
Ayshercool
08081012143
Kar a manta ayi subscribing YouTube channel ɗina na Cool hausa tv
[18/06, 2:35 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin mu, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
p 4
Ko da sati ya zagayo, Mama tana sa ran ta ga Ruma ta shirya ta tafi makarantar allo, amma ta ga bata da niyyar yin hakan.
Sai ma aiki take a tsakar gida, wanda ba ta saba ba, tana naɗe yayyenta je komai.
Aliyu ne ya fito daga banɗaki, hannunsa riƙe da buta ya kalli Ruma ya ce "Ke ina makarantar allon?"
Ta ɗan ɓata fuska ta ce "Ni na cire kaina na daina zuwa".
"Saboda ke ki ka saka kanki, shine sama ta ka ki ka cire kan ki ko? Da alama baki da gaskiya"
Mama ta fito tsakar gida ta ce "Ali ajiye butar nan ka je mini makarantar allon ka ji me ta aikata, dan ban yadda da ita ba" dan jikinta ya bata Ruma wani laifin tayi.
"Wallahi Mama ba abin da na yi, ba sai ya je makarantar ba, idan ya je ma sharri za su yi mini, ba sa sona malaman"
Mama ta ce "Au malaman ne suke miki ƙarya Rumaisa, ai ko me za ace mini kin aikata ba zan musa ba"
Huzaifa daga cikin ɗaki ya ce "Dama saboda ƙawayenta ya sa ta ce ita ma a sakata a makarantar, ba dan Allah take zuwa makarantar ba ".
Aliyu ya saka jallabiyarsa ya tafi makarantar allon.
Bayan fitarsa rantse-rantse take ta yiwa Mama, akan ita fa ba abin da ta aikata a makarantar nan, amma Mama ta shareta.
"Ruma!"
"Na'am Yaya Sadik "
"Zo ki sayo mana ƙwai ki soya mana mu karya"
Kasancewar Ruma akwai kwaɗayi, ya sanya ta daina fargabar zuwan Aliyu makarantar su, ta karɓi kuɗi ta tafi aiken da Abubakar ya yi mata.
**********
A kashingiɗe take a kan kujera, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, ta tattara dukkan wata nutsuwarta a kan ƙatuwar wayar hannunta, da alama ko me take kallo mai muhimmanci ne.
"Samha me ki ke wa wannan kallon ƙurillar ne?"
Wadda aka kira da Samhan ba ta motsa ba, balle ta daina abin da take yi.
Hannu ɗayar ta saka, ta zare wayar daga hannun Samhan, tana dubawa.
Har a wannan karon, Samha ba ta yi motsi ba, balle ta karɓi wayarta ta ba.
"Samha kina da hankali kuwa? Wai dan Allah da gaske ki ke dama?"
Samha ta ja ajiyar zuciya ta ce "Nusaiba, ke da kin ɗauka da wasa nake yi dama?"
Nusaiba ta jinjina kai ta ce "Eh, ni ban san abin da ki ke faɗa har zuciyarki ba"
Samha ta gyara zamanta ta kalli Nusaiba, cike da son tabattar mata abin da take faɗa ta ce "Nusaiba, ban fara dan na daina ba, ko zan tafi tsirara zan mallaki abin da zuciyata take muradi"
Nusaiba ta ɗan jinjina kai ta ce "Amma ya batun alaƙa fa, ko kin manta?".
"Alaƙa bata gabana, na san a yadda zan yi wasana. Kar ki manta anjima akwai walima a gidan Shamaki"
"Hmmm Allah ya kaimu, Allah ya sa ba wani banzan abun zaki yi ba".
Wani ɗan guntun murmushi Samha tayi, ta ce "Koma dai menene, we should see"
********
Ko da Runaisa ta dawo gida daga aiken Yaya Sadik, tana daga tsakar 6 tarar da Yaya Aliyu a falo yana wassafawa Mama abin da aka gaya masa a makarantar allonsu, ga Yaya Umar a zaune.
"Wallahi mama ba ki ji yadda ake complain a kan yarinyar nan ba, malaminsu ya ce dama ko ta dawo korarta za su yi, ba karatun take yi ba, sai tsokana da fitsara, da damben da yaran mutane, wai sam ba ta da nutsuwa da ɗa'a, malam Babba ya tara su zai hukunta su sun yi laifi ta ɗau allonta ta gudu, yana kiranta amma tayi masa banza".
Cike da fushi Umar ya ce "Ba kune kuke goya mata baya take wani rashin mutuncin ba, tun da ta san ko me ta ɗauko zaku tare mata ba, ku bari ta tsokano waɗanda zasu nakasata yadda gobe ba zata ƙara ba. Babu wanda yake faɗar alkhairi a kan ta sai sharri" ya ƙarasa maganar yana fitowa tsakar gida cike da fushi.suna yin ido huɗu da Rumaisa ta saki ƙwan hannunta a ƙasa ta na ja da baya, saboda tsoro da fargaba.
Taku biyu ya yi ya danƙota, ya sanya hannunsa ya riƙe kunnenta ɗaya da ƙarfi.
Wani irin ihu ta kurma tana riƙe hannunsa, saboda ji tayi kamar zata ɗaga kai ta ga kunnen a hannunsa, saboda azabar zafi.
"Dan ubanki idan har ba zaki canza hali ba, makarantar kwana zan kai ki, tunda ba ki in da yake miki ciwo ba, ko mu mayar da ke can ƙauye, su miki aure"
Usman ya ce 'Ai Rumaisa sai ka ce wadda ta sha nonon aljana, hatsabibancin ta yayi yawa, ba ta jin magana sam"
Abubakar ne ya fito daga ɗakinsu a fusace, ya ƙaraso ya riƙe hannun Rumaisa, ya kalli Yaya Umar ya ce "Sakar mata kunne" Umar ya ɗan yi turus yana kallon Sadik.
"Baka ji bane?"
Sadik ya maimaita masa. Yaya Faruk ya saki kunnen Rumaisa, da idanunta tuni suka yi ja saboda kuka.
Ya janyota ya zaunar da ita a kan tabarma, ya dinga share mata hawayen fuskarta.
Cikin ɓacin rai ya ce "Yakamata ku dinga yiwa kan ku adalci a kan yarinyar nan, ita kaɗai ta tashi a cikinmu mace, tayaya zaku ce sai kun tanƙwarata yadda ku ke so? Tayi laifi kowa yayo kanta, ba mai yi mata nasiha, daga mai ce mata munafuka sai me ce mata aljana haka ake rayuwa?"
Yasir ya ce "Wallahi Yaya Sadik, duk ranar da yarinyar nan ta kwaikwaya maka rashin mutuncin da take aikatawa zaka gane ba tsanarta aka yi ba"
"Koma dai yane, a dinga barin yarinya ta huta a daina takura mata haka "
Guntun tsaki Umar ya ja, ya fice daga gidan gaba daya, suna zaman zamansu Mama ta haifo wannan 'yar kalen hanjin da ta gallabi rayuwarsu.
Yau cikin dare, Mama ta tashi tana ibada, kamar yadda ta saba domin a cewarta wanda duk ya tara zuriya yake neman kuma dacewa, bai ga ta bacci ba.
Fitilar ɗakinta ta kunna, haske ya gauraye ko ina, Rumaisa tayi rashe-rashe a kan katifa, zaninta daban ita daban daga ita sai wando, kanta ko ɗan kwali babu.
Mama ta girgiza kai, ta janyo zanin ta ɗaura mata, ta saka mata hula ta lulluɓeta, sannan ta fice ta ɗauro alwala ta zo ta tayar da salla. Sai dai sam Ruma ba ta san an yi bama, tana ta fama da bacci.
Can Mama ta kuma juyawa, amma ta ga Rumisa ta kuma yada zanin, ƙafafuwanta duk suna ƙasan katifar, ta kuma tumɓur tana bacci.
Haushi ne ya kama Mama, ta ƙarasa in da take, ta ɗala mata duka a cinya. Amma maimakon ta tashi, sai ta sake dunƙulewa tana bacci.
"Ke Ruma, ba zaki tashi ba sai na saka miki bulala?" Da ƙyar ta tashi tana murza ido tana kalle-kalle.
'tashi ki ɗauki rigarki ki saka, ki ɗaure kanki ki je ki yo alwala ki salla".
"Wai har asubar ta yi ne?"
Mama ta ce "Wato ke idan ba sallar farilla ba, baki san ki yi nafila ba, sai dai ki saki leɓe kina bacci. Ki je kiyi alwala ki zo ki yi salla ki roƙi Allah ya yaye miki wannan wautar da rashin hankali da kike fama da shi" kafin Mama ta gama maganar, Rumaisa ta sake ɓingirewa ta kwanta.
Aikuwa mama ta ƙule, ta janyo mafici ta shiga rafka mata a cinyoyinta, a razane ta miƙe tana sosh-soshe.
Mama ta bata riga da ɗan kwali ta ɗaura, ta korata tayo alwala.
Mama ta koma kan tata sallayar ta cigaba da salla.
Kusan mintuna arba'in, Mama ta manta ta tura Rumaisa tayi alwala, ta kalli shimfiɗarta taga bata wurin.
Da sauri ta tashi ta fita tsakar gida tana dubawa, sai dai babu Rumaisa babu dalilinta.
Lelleƙawa Mama ta hau yi, tana nemanta a cikin gidan amma bata nan.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ina yarinyar nan ta shiga ne haka?" Tayi maganar lokacin da ta ƙarasa soro tana haska fitila, amma taga ƙofar gidan a rufe.
Ƙofar ɗakin samarin gidan ta tsaya tana bubbugawa da ɗan ƙarfi.
Usman ne ya taso cikin yanayi ya bacci, ya kalli Mama ya ce 'Mama lafiya kuwa?".
Cikin tashin hankali ta ce "Ruma na tasa tayi sallar dare, daga ta fito tayi alwala, na nemeta na rasa".
Ƙwalalo ido waje yayi, ya ce "Ruman? To ina ta tafi?"
Mama ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, na duba ƙofar gida tana rufe da sakata ba a buɗe ba"
Mamaki duk ya cika Usman ya ce "To in ta shiga a tsohon daren nan, bari na sako rigata a buɗe gidan a dudduba".
Ya shiga cikin ɗakin, ya kunna wutar lantarkin ɗakinsu, sai ga Ruma a tsakiyar su Yasir tana bacci.
Kunna fitilar ne ya sanya Huzaifa ƙoƙarin yin juyi, amma ya ji mutum a kusa da shi, yayi zaton Yasir ne, dan haka ya dage ya hankaɗa Rumaisa, ta kifa kan Yasir amma ba ta farka ba.
Usman Ya ce "mama leƙo kiga"
Jiki na rawa mama ta shiga ɗakin, daidai lokacin da Yasir ya ji nauyi a kansa shi ma ya dage ya hankaɗata gefe guda.
Mama ta shiga tafa hannuwa tana salati, a irin magagin bacci, da shirme na Rumaisa tsaf za a saceta tana wannan baccin na asara.
A ƙufule Huzaifa ya tashi yana zage-zage ya zata Yasir ne yake damne shi, amma ya ga Ruma a tsakiyar su, ga su Mama a tsaye.
"Ke uban me ki ke yi a ɗakinmu, mama meyafaru?"
Jin hayaniya ya sanya Sadik ma farkawa, ya dinga kallonsu ɗaya bayan ɗaya 'mama lafiya kuwa'.
'lafiya lau, kai Huzaifa taso mini ita'
Abubakar ya kalli in da Rumaisa ke ta more laushin katifa tana barci.
"Wai me ya kawo yarinyar nan ɗakin nan?"
Usman yayu masa bayani kamar yadda Mama tayi masa.
Sadik ya ce "Kai Huzaifa, kai da Yasir ku sauko ku bar mata katifar dan Allah, wannan ba tashi zata yi ba"
Yasir ya ce "Kaii, Yaya haryanzu fa yarinyar nan tana fitsarin kwance, kawai a tasheta ta fita, kar ta tsula mana fitsari dan katifar nan wuyar bushewa za ta yi".
Yaya Umar kuwa tun shigowar Rumaisa yana kallonta, lokacin bai daɗe da kwanciya ba, ya ganta ta shigo tana tangal tangal, ta nemi wuri ta kwanta, tun da ta shigo yana kallonta.
Mama ta ce "Ba zata kwana a nan ba, taso mini ita ta wuce mu tafi".
Yasir ya daddaki Rumaisa a kafaɗa, amma ta hau surutai da irin faɗace-faɗacen da suke yi da yara a makaranta.
Ƙarshe haushi ya ƙule, Umar ya tashi danƙo Ruma ya hankaɗowa Mama ita tsakar gida, ya rufe musu ƙofa.
Mama har mamakin wannan magagi da kuma suratan baccin da Rumaisa take yi, ita duk wani da mutane suke yi, nata ya zarta ƙa'ida.
Har mama ta kama hannunta zuwa ɗaki, magagin bacci take yi.
******
Sassanyar iskar da bishiyoyin ke bayarwa ne ya haɗu da ƙamshin furanni, tare da samar wani kyakkyawan yanayi mai sanyawa zukata nutsuwa da annashuwa.
Duk da wannan tarin ni'ima, gaba ɗaya Samha ba ta jin dadin yanayin sam.
Wayar hannunta ce ta fara ringing, wadda ta katse mata dogon tunanin da take yi, ɗagawa tayi ta kara wayar a kunneta ba tare da ta ce komai ba.
"Ki fito mu tafi, ina haraba".
"Ok, ya maganar mu? Kun yi magana da ita, zasu zo ne".
Nusaiba ta ce "Hmm, Samha kenan ke meya hana ki tambayeta?"
"Nusaiba bana son wasa, am serious about it".
Nusaiba ta ɗan taɓe baki ta ce "Eh, za su zo" Ta sauke wayar daga kunnenta, ta nufi hanyar fita daga lambun.
***
Mama tana yawan yin istigfari da nemawa Rumaisa shiriya, musamman yadda bakin mutane yayi yawa a kanta, duk wani rashin ji irin na ɗa namiji shi take yi, bama irin na mata sa'aninta ba, duk sa'aninta ta kere su a rashin ji. Babu yadda Mama ba tayi ba a kan aje a bawa malaman makarantar allon su haƙuri, ta koma amma mirsisi Yaya Umar ya ce sai dai a sauya mata makaranta, in da zata fi mayar da hankali, amma a ƙasan zuciyarsa zafin maganganun da malaman suka yi a kan Rumaisa ne ya fi ɓata masa rai har ya sanya ya ce ba zata koma ba.
Ita kuwa Rumaisa ganin Yaya Umar ya hana a mayar da ita makarantar allon Malam Babba, tayi ta murna a ganinta ta huta da zuwa makarantar nan mai cike da takurar tsiya, Allah ya sa makarantar bokon ma a cireta, ta dawo gida Mama ta bata jari ta dinga sayar da wainar fulawa a ƙofar gida. Murmushi ta yi bayan wannan tunanin ya zo ranta.
Ta dubi Abdallah da yake ninke kayan da ya wanke ta ce "Yaya Abdallah, dan zaka gayawa abokananka zan fara sayar da wainar fulawa, naga kai ne me abokai masu kuɗi, ka talatta musu su zo su dinga saya, ba irin abokan su Huzaifa ba gayyar ƙolawa da tsamaye ba"
Saroro ya kalleta ya ce "wace irin wainar fulawa kuma?"
"Eh tun da na daina zuwa makarantar allon, sai Mama ta bani jari na diga sayar da wainar fulawa a ƙofar gida".
Huzaifa ya ce "Eh dama kin yi kalar sayar da wainar fulawar ai, ai ni da kai na zan din ga yi miki ciniki, ai suyar wainar ce ta dace da le delu"
Murguɗa baki tayi ta ce "Da dai ban san halinka bane, ci ka tsere ka rusa mini jari, kama kar ka sake ce mini wata deluna gaya maka.
Ta mayar da hankalinta kan Abdallah ta ce "Dan Allah Yaya Abdallah ka yi magana mana".
"To ai Ruma na rasa me zance miki ne, wace irin wainar fulawa ana zaman lafiya".
"To Yaya ba gara ace ina sana'a ba, kuma ku huta ba, ana ta shelar mata su kama sana'a, Mama ai zaki bani jari ki saka mini albarka ko?"
Mama ta ce "kada Allah ya nuna mini wannan rana, kuma kar ki sake sakoni a cikin shirmenki, idan kuma ki ka sake sai na ci ubanki ke da soya wainar fulawa a ƙofar gidan, tun da ke dai Allah bai sa an raba hankali kin samu ba" ɓata fuska tayi a ranta ta ce 'sai na tambayi Yaya Abubakar, na san shi ba zai hana ni ba ai, tun tuni ake cewa mata su kama sana'a ni kuma zan yi ana hanani'.
Umar yana ɗaki yana jin shirmen da Ruma take, ji yake kamar ya ɗauketa ya kai ta boarding kowa ya huta, amma ya san Mama ba zata taɓa amincewa ba.
Wayewar garin Allah, wurin ƙarfe sha ɗaya na safe, mama na shirin fita, telar da take yiwa Mama ɗinki ta aiko da ɗinkin da Mama ta kai mata, bayan mama ta karɓi ɗinkin ta sallami yaron, ta kalli Ruma ta miƙa mata ledar ta ce "gashi nan kayanki ne".
Da murna ta karɓi ledar ta buɗe, cike da son ganin menene a ciki.
Tana buɗewa tayi karo da wata atamfa koriya da yellow, ta kalli Mama ta kalli atamfar sannan ta ce "Wallahi Mama wannan Salamatu mai kayan ba ta kyauta mini ba, sai da nace ba na son atamfar nan, amma dan taga ba na nan shine ta liƙa miki, ki ka saya amma shikenan na gode, amma dai ba dan an ɗinka ba sai na mayar mata" ba ta gama rufe baki ba, ta buɗe kayan taga riga da zani jaka a tsaye, da wata uwar bunjumemiyar riga kamar zata tashi sama.
"Ta kalli mama ta ce "Mama wai wannan kayan nawa ne ko kuma naki?" Ruma tayi maganar a rikice.
Mama ta ce "Ni ce zan saka wannan kayan? Naki ne mana"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu mama wannan ne kayan salla na, dan Allah kalli rigar tsaf sai an saka irina sittin a ciki, mama ko gwada ni fa ba ayi ba aka ɗinka kayan"
A fusace Mama ta ce "Naji na gode, ki ajiye mini kayana tunda ba ayi miki gwaninta".
Yasir ne ya dubi Ruma ya ce "Amma Ruma baki da kirki, yanzu mama ta sai miki kaya ta bayar a ɗinka miki, amma ƙiri-ƙiri ki nuna ba kya so".
Mama ta ce "Rabu da ita, ta je ta ƙarata".
"Mama kiyi haƙuri, ba cewa nayi bana so ba, amma dan Allah kalli rigar nan, ni ba tattabara ba ina zani da wannan rigar kalli hannun kamar fuka fukai, ba irin wannan rigar na gani a jikinku a wannan tsohon hoton naku ba?"
Yasir ya karɓi rigar yana dubawa, ƙunshe dariyarsa yayi ya ce "To dan ubanki maje gaba aka yi miki, tun kina yarinyarki da ke, wato kin fi son matsatsun kaya ko, to baki isa ba, wannan rigar da ita zaki yi wankan idi mu je masallaci, maje gaba ce "
Haushi ne ya gama cika Ruma, ta tura baki tana jin kamar ta yi ihu.
"Wace irin maje gaba, ai sai a bari nayi gaban tukuna, sai a ɗin ka mini daidai ni, idan ban je gaban ba fa?"
Mama ta ce "Rabu da ita, ta gama rashin mutuncinta tun da abin nata haka ne, daga wannan ba zan ɗinka mata wasu ba, da su zata yi sallar, dama ba jin maganata take yi ba, nima an zo wurin da zan fanshe, bana ba kayan salla sai kala ɗaya".
Yasir ya ce "Wallahi mama hakan ma ta gode sosai Allah ya saka da alkhairi, ya ƙara buɗi, ai kin yi ƙoƙari, ke Ruma wannan rigar idan ki ka sakata ai ba sai kin ɗaura zanin ba, kaɗan ya rage ta zama doguwar riga, idan kuwa zaki ɗaura zanin sai ki ɗaura shi a kam rigar, ki yi ɗaurin barmana coge wallahi kyau zaki yi"
Gaba daya ta fuskanci Yasir rashin mutunci kawai yake yi mata, kamar zata fashe haka ta tattare kayan ta kai ɗaki ta zubewa Mama a kan kujera, ta barwa ranta cewa gara tayi zamanta a gida da salla, da ta saka wannan zulumbuwar rigar a matsayin kayanta na salla ta fita ayi mata dariya.
Mama ta fita yin barka a maƙwabta, hakan ya bawa Yasir damar zama ya sanya Ruma a gaba ya dinga tuntsira mata dariya, duk wanda ya shigo sai ya ɗauko masa kayan ya nuna masa, daga atamfar har ɗinkin irin na zamanin su Mama ne.
Huzaifa ya fi kowa ƙyaƙyatawa, ya ce "Lallai mama ta iya punishment, ai ni ta biyani da aka miki wannan ɗinki, kamar yadda Yasir ya faɗa, idan ki ka saka kayan nan, ki ka kafa ɗauri irin na barmana mu samo ƙorrai, da sallar nan mu baza kiɗan ƙwarya a cikin unguwa, wallahi kuɗi zamu samu, dan dama mutane duk sun watsar da al'ada".
Abdallah har da yi mata magiya a kan ta gwada kayan yanzu, ya ga yadda za su yi mata. Tayi musu banza ta koma gefe ta ci magani.
Yaya Usman ne ya zare mata ido, wai sai ta gwada kayan sun ga yadda za suyi mata, kasancewar tana shakkarsa shima, haka ta je ta saka kayan ta fito tana danne kukan da yake ƙoƙarin ƙwace mata.
Tana fitowa tsakar gidan Huazaifa ya bushe da dariya ya ce "Waya ga babba da jaka".
Abdallah ya ce "Allah ya bar mana Delun mu, wallahi dama delun aka saka miki, kin yi kyau".
Usman Ya ce "Abdallah, yi mata ɗaurin barmana cogen, mu gani, zan mata video"
Duk yadda ta so haɗiye kukan sai ta kasa, sun kewayeta sai dariya suke kamar sun ga mahaukaciya, ga Usman yana yi mata video da wayarsa suna dariya.
Huzaifa sai kifawa yake, kamar wanda ya zare, yana cewa Usman"Ka yi mata hoton da Black and white mu ce ga kakar su Mama 1940"
Babu tsammani Umar ya shigo, ya tarar da Rumaisa a tsaye kamar an dasa ta, ga uban ɗauri a ka, ta ɗaura zani a kan riga, tana tsaye tana kuka su kuma sun kewayeta suna dariya.
"Meye haka?" Yayi maganar a kausashe.
Usman ya ce "kayan sallarata ne, aka kawo take ta rashin mutunci wai bata son kayan, shine nake punishing ɗinta, nan gaba ta koyi godiya ga Allah a kan duk abin da ya bata, sannan ta godewa wanda ya batan".
Shi kansa Yaya Umar ji yayi kamar ya yi dariya, saboda yadda Ruman tayi a kayan, kai da gani ka san sun yi mata yawa, sai tayi kamar wadda ta kawo tallan kalwa birni.
Gimtse dariyarsa yayi ya wuce ɗakinsu, suka gama yi mata rashin mutunci sannan suka sallameta.
Da ta koma ɗakin ma, sai da ta sha uban kukanta, ta cire kayan ta ajiye tana jin yadda ranta yayi mugun ɓaci a kan abinda suka yi mata.
Kasancewar yau ba tuwo mama tayi da daddare ba, ya sanya ruma zaman cin abincin dare ba tare da mita ko ƙunƙuni ba, ga kuma uwa uba a ƙule take da rashin mutuncin da su Yaya Abdallah suka yi mata. Tana ta lissafa yadda zata rama abin da suka yi matan ta huce.
Duk da yadda yau tayi shiru, babu wanda ya kula da shirun nata, dama mama na jin haushin tayi mata abu ta kushe, mama ta mayar da hankalinta kan 'yan mazanta suna ta hira.
"Mama ina da tambaya" duk suka waiwayo suka kalleta.
mama ta ce "To ina jinki, Allah ya sa na sani"
"Wallahi na san ƙarshenta banzayen tambayoyinta ne marasa kan gado, dan Allah mama kar ki saurareta" Huzaifa yayi maganar yana kallon Ruma.
Cikin tsiwa ta ce "Ban kasa da kai ba, dan haka babu ruwanka da ni".
Mama ta ce "Yi tambayarki ina jin ki"
"Yauwa, dan Allah kar na tambayeki kuma kice mini sai an kwana biyu, menene Janaba, kuma meye fyaɗe!!!"
Ayshercool
08081012143
Kar a manta ayi subscribing YouTube channel ɗina domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
[20/06, 6:52 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode.
P5
Sak suka yi gaba ɗayansu, lomar da Yaya umar ya haɗiya ya ji taƙi wucewa tana kai komo a wuyansa kamar zata dawo. Amma ya basar kamar bai san me suke faɗa ba.
Huzaifa kuwa tsam ya miƙe yana faɗin "Ai sai da na ce kar ki saurareta ki ka ƙi, sai ku san abin da zaku gaya mata" yana maganar ya bar tsakar gidan.
Mama ta rasa mai zata cewa Ruma da hankalinta zai ɗauka, sam yarinyar bata tunani dai-dai da shekarunta.
"Wai ya na ji kin yi shiru? Me kuma nayi?" Ta yi maganar cikin taɓara.
Cikin ƙarfin hali mama ta ce "Ke a ina ki ka ji wannan kalmomin da ki ka tambayeni?"
"Mama ya kuma ki ke tambayata bayan nima tambayarki nayi"
"Ki amsa mini dan ubanki" mama tayi maganar a hasale.
Ta ɗan cuna baki sannan ta ce "Ba wani ne ya gaya mini ba, kece ki ke jin radiyo ranar, na ji ana cewa ayi wankan janaba idan aka yi ko me? Oho na manta shi ne nake son na san meye janaban, kuma meye wankan. Shi kuma fayɗe idan aka faɗa a radiyo sai na ga hankalinki ya tashi kina girgiza kai kina Allah ya tsare zuriyar musulmi baki ɗaya, shine nake son na san menene?"
"Tirƙashi, aiki ga mai ƙareka mama Allah ya bamu alkhairi " Yaya Aliyu ya faɗa yana ƙoƙarin shigewa ɗaki.
Yaya Usman ya ce "Kuma duk abin da ake faɗa a radion babu wanda ki ka riƙe sai wannan?"
Ruma ta ce "To ai akwai wasu ma, mantawa nake yi ne sai yanzu na tuna"
Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Kina jina ko Ruma?"
"Eh ina jinki"
"Yauwwa, zan gaya miki zan miki bayani, amma ba yanzu ba sai an kwana biyu, yanzu ko na yi miki bayani ba zaki gane ba, kuma nan gaba ko ba a gaya miki ba ma, zaki gane da kan ki".
Cike da yarinta ta ce "Nan da kwana biyu ranar asabar kenan, in Allah ya yarda zan tuna miki ki gaya mini"
"Ba wanna kwana biyun nake nufi ba hansai, sai kin ƙara girma da hankali"
Cikin mamaki Ruma ta ce "Yaushe kuma zan ƙara girman da hankali, wancan karon ma fa na taɓa tambayarki menene MATA MAZA, ki ka ce mini sai na girma, na tambayeki menene haila ki ka ce mini ba yanzu ba, amma da zan yi wani abun sai ki ce ina girma amma bana hankali wane irin girma ki ke son nayi to?"
"Ke tashi ki wuce ki kwanta dan uwarki, kawai kin saka mutane a gaba da tambayoyinki na shirme, ko a gidan uban wa ki ke jiyo wannan manyan maganganun oho miki, wuce kan na karya ki biyu, ba zaki tambayi abu daidai da hankalinki ba sai wanda ya fi ƙarfin kanki" sai da ta kalli in da Yake zaune yana bata umarni, bayan da fari yayi kamar bai san me suke yi ba.
A hankali ta tashi ta nufi ɗaki, tana tunanin menene aibun tambayarta?.
Tafiya ta yi ɗaki, ta gyara shimfiɗarta ta kwanta, tana tunanin meyasa kullum tayi tambaya sai ace mata ba yanzu ba sai an kwana biyu, ko ace wai tana tambayoyin da suka fi ƙarfin ƙwaƙwalwarta me hakan yake nufi kenan?. Da wannan tunane-tunanen bacci yayi awon gaba da ita.
Da safe tana kwance tana baccinta, duk samarin gidan sun gama komai, har abin karyawa, Kasancewar Asabar ce Ruma tana ta baccin asara, ba aikin fari balle na baƙi, har ƙasan ranta tana matuƙar jin daɗin rashin zuwa makarantar allo da ba ta yi, saboda tana samun isasshen lokacin bacci.
Ji take ina ma ace bokon ma ta daina zuwa, idan tayi baccinta ta ƙoshi da yamma ta kfa suyar wainar fulawa a ƙofar gida ta tara 'yan kuɗaɗenta.
Baccin yayi mata daɗi, tayi nisa sosai a duniyar mafarkai kala-kala, ta ji kamar daga sama ana taka mata ƙafa.
Buɗe ido tayi a hankali, amma taƙi motsawa, tana son ta tabbatar da a zahiri ne ko duk cikin mafarkin ne.
Ji tayi an kuma zungurarta da ƙafa, ba tare da ta waiwayo ba ta ce "Wallahi Huzaifa zan maka rashin mutuncin da baka taɓa tunani ba, kar ka sake takani"
Bai ji kashedin ba, ya sake haurinta da ƙafa, "Allah ya isa wallahi, kuma ba zan tashi ba" tayi maganar tana sake dunƙulewa a wuri guda.
Ƙashin bayanta ya kuma daka da ƙafarsa, ta yinƙuro a matuƙar zafafe, da nufin ta kafa masa haƙora ko a ina ne, amma me tayi tozali da Umar a tsaye a kanta.
Jikinta ne ya hau tsuma, ta ma rasa me za ta yi, ko ta ce.
Shiru yayi yana nazartarta, daga bisani ya ce "Ki tashi ki je ki ki yi wanka ki karya ina jiranki, kuma idan ki ka ɓata mini lokaci kin san sauran"
Saroro tayi tana kallonsa, da ba ta gama fahimtar me yake nufi ba.
"Za ki tashi ko sai na yi ball dake?" Cikin hanzari ta tashi, ta ɗauke katifarta ta nufi banɗaki tana mamakin to ina zasu je, kar dai boarding ɗin zai kaita kamar yadda ya ce. Gabanta ne ya faɗi ta fara tunanin ko ta gudu.
Kai tsaye ta nufi banɗaki, tana shiga ta tarrar da an haɗa ruwan wanka, ba tayi tunanin ko ruwan waye ba, ta rufe ƙofa ta hau wanka da shi.
Yasir ne ya nufo banɗakin da sauri, wuyansa ɗauke da soson wankansa, zai shiga banɗaki saboda ya kai ruwan wankansa, amma yana zuwa ya ga ƙofar a rufe.
Iya ƙarfinsa ya hau dukan ƙofar yana faɗin "wani ɗan rainin hankalin ne ya shiga bayan na kai ruwa?"
Gyran murya tayi masa, tsaki ya ja ya ce "Ki hanzarta zan yi wanka na fita na kusa makara.
Tun yana saka ran zata fito har ya tashi ya fara zaginta yana bugun ƙofar.
Ba ta da tabbacin wankan da tayi ta fita, ta buɗe ƙofar banɗakin, zagi ya dinga surfa mata, bai kai ga rufe baki ba, idonsa ya sauke a kan bokitin da ya haɗa ruwa, Ruma ta zubar da komai.
A hasale ya zura hannu ya janyota tsakar gida ya ce "Wallahi yau mai ƙwatarki sai Allah, na zuba ruwa na kai zan fita makaranta kina can kina bacci, amma ki zubar mini".
Babu alamar nadama ta tsuke fuska ta ce "To ba Yaya Umar ne ya ce nayi wanka ba"
Wani ranƙwashi ya yi mata a tsakiyar ka, da azabar zafinsa ya sanya ta durƙusa a kan gwiwoyinta, tana sakin wani irin kuka mai sauti.
Yaya Umar ya ɗaga labulen taga ya leƙo ya ce "Ƙyaleta tun da ka daketa" ba ƙaramin ɓaci ran Yasir yayi ba, dan niyyarsa sai ya yiwa Ruma dukan da duk taurin kanta sai ta bashi haƙuri.
Kasa karyawa tayi saboda kuka, tana tsaye tana duru-durunta, Umar ya shigo hannunsa riƙe da leda ya miƙa mata ya ce "Maza ki shirya ki wuce mu tafi"
Karɓar ledar tayi tana duddubawa, uniform ne na islamiyyar su Huzaifa, makarantar da ta ce ko aljanna ake rabawa a cikinta ba zata yi ta ba, saboda azabar tsaurinsu, asabar da lahadi tun tara sai biyar ake tashi, ba a fashi balle makara, ga haddar Alqur'ani ake yi da gaske ba wasa ba.
Saroro tayi tana kallon Yaya Umar, cike da rashin fahimta amma ta kasa yi masa Magana.
Wata uwar harara da ya yi mata ne, ya sanya ta shiga ɗakin Mama, ta saka uniform ɗin jikinta sai tsuma yake yi, ita ta san har ga Allah ba zata iya zaman makarantar nan ba.
Mama dai ba ta ce musu kanzil ba, ya tasa ta a gaba suka tafi.
A zuciyarta tana ta addur Allah ya sa makarantar suce ba zasu karɓeta ba, bata tunanin ko su Huzaifa sun san za a sakata a makarantar su, dan da sun sani cewa zasu yi basu yadda ba.
Tun da suka shiga makarantar, tashin karatun Alqur'ani kawai ka ke ji, daga kowacce kusurwa, kuma da alama ɗaliban makarantar a nutse suke.
A ofishin shugaban makarantar aka titsiye Ruma ana yi mata interview, amma ba abin da ta iya, izifi biyun da aka yi mata tambayoyi da ƙyar ta kai.
Umar ya shiga tunanin tsawon lokacin da Ruma ta shafe tana zuwa makarantar allon nan, me take yi da ta kasa izifi biyu.
Ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, ya hau ta da faɗa a gaban mutane.
Cikin kuka ta ce "Wallahi yaya na iya karatu"
"To uwar me ki ka iya, kin kasa izifi biyu"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Eh na iya, amma ba a allona na rubuta na iya ba, na allon wani almajirin malam babba ne, idan aka ƙara masa nake iyawa, ni kuma sai na kasa nawa"
Murmushi malamin yayi ya ce to biya mu ji "Tiryan-tiryan da ƙira'ar warsh, take karanta suratul Yusuf, ko tuntuɓe babu"
Shugaban makarantar yayi mata kabbara ya ce "Ahh gaskiya 'yar baiwa ce, zamu san a in da yakamata mu sanyata, daga islamiyyar har tahfiz ɗin, zaku ga sauyi in sha Allah zata yi karatu"
Yaya Umar ya ce "To masha Allah, haka muke so" aka saka wani malami ya kai Rumaisa aji.
Tare suka fito da Yaya Umar, ya dubi Ruma ya ce "Ga makaranta nan na kawo ki, idan kin ga dama kiyi karatu, idan baki ga dama ba nan ma ki yi musu halin naki, kiga abin da zai biyo baya" ta sunkuyar da kai kamar ta Allah, yayi faɗansa ya gama ya tafi.
Gaba ɗaya ba tayi murna da zuwa makarantar nan ba, haka aka kai ta aji ta nemi wuri ta zauna.
Gaba ɗaya ɗaliban sun mayar da hankali, suna ta zuba karatu, Ruma kuwa sanyin fanka ne ke nema ya sanyata bacci.
"Ke ya ba kya karatun?" Cewar malamin da yake kula da karatun nasu.
Kallonsa ruma tayi, shima uniform ne a jikinsa na ɗalibai, amma ya tsaya zai yi mata iyayi.
"Sabuwar zuwa ce ni, ban iya wurin ba" ta bashi amsa kanta tsaye.
Bai kuma saurararta ba, ya cigaba da tilawar tare da sauran ɗaliban.
Ta dubi wata ɗaliba ta ce "Ke, dan Allah nan aji nawa ne?"
Ɗalibar ta kalli Ruma sannan ta ce "Aji ɗaya ne"
"Kutmar, ban gane aji ɗaya ba, kina nufin aji ɗaya aka kawo ni?"
"Eh mana" yarinyar ta bata amsa.
Ruma ta jinjina kai ta ce "Lallai ma an raina mini hankali, wallahi ba zan zauna a aji ɗaya ba".
Ɗaliban suna ta tilawarsu, yayin da malamin yake jin haddar wasu, amma Ruma hankalinta na kan yadda zata fita daga ajin, dan zaman ajin ya isheta.
Daga bisani ta koma gefe ta hau gyangyaɗi.
Lokacin da aka fita break, yunwa ta saka Ruma a gaba, dan ba ta karya ba Yaya Umar ya taso ta a gaba.
Ɗalibai ne masu yawa sosai a makarantar, dan makarantar sananniya ce sosai a unguwar, dan kusan babu ta biyunta. Daga yanayin mayar da hankalin su Huzaifa da yadda suke bayar da labarin tsananin makarantar ya sanya ta ji ba ta son makarantar sam.
Tun da aka fita break da salla, wuri ɗaya ta samu tayi zamanta tana bin ko ina da kallo, sai da ta gaji ta tashi ta fara dubawa ko zata ga Yasir ko Huzaifa amma babu wanda ta gani a cikinsu. Haka aka koma aji ba tare da ta samu komai ta saka a cikinta ba.
Aka dawo aji aka ɗora da karatu babu ƙaƙƙautawa, gaba ɗaya Ruma ta gaji da zaman makarantar. Malamin ajinsu ya fara yi musu ƙari, ta buɗe Alqur'anin ta ajiye, ta cigaba da gyangyaɗinta.
Tun da Ruma ta shigo ajin ɗazu yake kallonta, sam ya lura babu alamar son karatun a tare da Ruma, daga hamma sai bacci take yi.
Ƙarshe ta haɗa jakarta ta cewa malamin fitsari take ji, ya ce taje tayi, ta ɗau jakarta ta bar ajin.
Zagayawa take tana lelleƙa azuzuwa ko Allah zai sa taga mutum ɗaya a tsakanin yayyenta, dan har wani irin jiri take ji, dan a duniya ba ta wuce ƙarfe ɗaya ba ta ci abincin rana ba, yau sai ga ta har azahar babu ko karin kumallo.
Ajinsu yayi tsit, sun tattara hankalinsu a kan ƙarin karatun da ake yi musu, kamar daga sama ya jiyo muryarta "Huzaifa, dama nan ne ajinki tun ɗazu nake neman ku" gaba ɗaya ajin aka waiwaya don ganin waye yake wannan wautar.
Kallon da ake yi mata bai sanya ta nutsu ta daina maganar ba "ka ganni a makarantar ku ko? Hmm ɗan zo ka ji wata magana mana".
"Ke wacece haka, baki ga karatu muke yi ba?" Malamin yayi maganar yana kallon tagar da Ruma ke tsaye.
"Yunwa nake ji, shiyasa nake nemansa" ta faɗa tana sake leƙo cikin ajin.
Shi Huzaifa mamaki ne ya cika shi, yaushe aka saka Ruma a makarantar nan bai sani ba?.
Ganin babu komai a kan Ruma sai wauta ya sanya malamin ya kalli Huzaifa ya ce "Je ka ka sallameta"
Cike da jin kunya ya tashi ya fita, yana fitowa ta tare shi da murmushi, shi kuma ya haɗe rai ya ce "Uban waye ya kawo ki makarantar mu?"
Kallonsa tayi ta kalli harabar da suke ta ce "Sai ka ce wata makarantar arziki, nima ban ce a kawoni ba, wayewar garin Allah kawai mai sunan Baba ya bani uniform ya kawoni, ni wallahi gara na koma na bawa malam babba haƙuri, in koma makarantar allon mu ba zan iya wannan jidalin ba".
"Ke dalla rufewa mutane baki, daga zuwanki kin fara nuna hali, kawai ki zo ta window kina kirana saboda hauka, maimakon ki yi sallama ki tambayi malamin, ke Allah sai kin bar makarantar nan, dan ba zaki zubar mana da mutunci ba".
"Saboda gani annoba ko?" Tayi maganar tana hararasa.
"To ba gara annoba ba, idan aka samo maganin ta shikenan ba, ke kuma maganinki sai Allah, yanzu uban me zan miki?"
Ta yatsuna fuska ta ce "Ni yunwa nake ji, kuma wallahi sonake na tafi gida"
Huzaifa ya ce "Lallai baki da hankali, to ke da gida sai ƙarfe biyar, wuce muje ajin su Yasir gara mu raba abin, da ki dinga yi mini ni kaɗai"tura baki tayi, ta rungume jakarta, Huzaifa ya sanyata a gaba yana mita suka nufi ajinsu Yasir.
Ita kuma sai mita take, a kan daga yau ba zata sake zuwa wannan makarantar ba da ake uzzurawa mutane.
Yasir kansa salati ya dinga yi da salallami "Dan girman Allah meyasa mai sunan Baba zai yi mana haka, ya saka yarinyar nan a makarantar nan ba a shawarce mu ba, wallahi mun kaɗe"
"Oho muku, ku kwantar da hankalin ku, ni ba kuma zuwa zan yi ba, kawai ku bani Abinci"
Yasir ya dungure mata kai ya ce "Shegen ci kamar kazar hausa" suka sakata a tsakiya suna tafe suna zaginta, suka saya mata awara da ruwa ta cinye tsaf, sannan suka korata aji.
Ko da ta isa aji, tuni an gama karatun Alqur'ani, ana jiran wani malamin ya shigo.
"Ya aka yi daga zuwa fitsari ki ka daɗe, gashi an gama ƙarin Alqur'ani, sati mai zuwa idan Allah ya kaimu zamu bayar da hadda" cewar yarinyar dake kusa da Ruma.
Ruma ta kalleta ta ce "Ina aka biya ɗin?".
Yarinyar ta buɗe Alqur'anin tana nunawa Ruma ta ce "Rabin shafi aka ƙara, gobe in Allah ya kaimu ma za a ƙara rabi, feji ɗaya kenan sati mai zuwa idan Allah ya kaimu sai ki kawo haddar".
Cikin ko in kula Ruma ta kawar da kanta gefe, alamar zancen yarinyar ma bai shigeta ba.
"Ya na ji kin yi shiru ne? Ki buɗe sai na koya miki, idan fa baki iya ba babu ruwan ya sayyadi da sabuwar zuwa ce ke, zaneki zai yi".
Rumaisa da shishshigin yarinyar ya fara ƙular da ita ta ce "To a kasheni mana kar a barni da rai, ba cewa aka yi nan aji ɗaya bane ba, kuma sai a ƙara mini rabin shafi, kuma wai na haddace yo ta ina zan iya ni, nifa a makarantar da na baro sai nayi wata ina nanata aya biyu nake iyawa, wannan karatun ma na san ba zan iya ba sai dai ayi kwaɗona da mai da yaji a cinye" galala yarinyar ta bi Ruma da kallo ta jinjina kai ba ta sake cewa komai ba.
Bayan an kaɗa ƙararrawar tashi, malamin da ya yi mata interview ya kirata ya gaya mata cewar za'a fara karɓar haddarta daga tushe, sannan za ta dinga yi tana haɗawa da wanda ake yi musu a aji.
Da yake ma bata fahimci bayanin da yayi mata ba, hankalinta na kan ta tafi gida, dan ta san ba iyawa za ta yi ba, kuma ta gama yanke shawarar daga ranar ba zata sake zuwa ba sai dai Yaya Umar yayi mata abin da ya ga dama.
Ko su Huzaifa ba ta nema ba, ta nufi gida.
Ɗa da uwa sai Allah, wuni gudan da mama tayi babu Ruma a kusa da ita duk sai ta damu, ta ji gidan babu daɗi, gashi tana ta tunanin ko abinci Ruma bata tafi da shi ba, balle ta samu ta ci haka mama ta wuni sukuku.
Tana tsaka da tunanin Ruman ne, ta ɗaga kai taga Ruman a tsakar gida.
"Meye haka, babu sallama ki shigo ki tsaya?"
Ruma bata amsawa mama ba, sai kumbura baki da take yi, ta cire hijjabinta da jakar makarantar ta dungurar a wurin ta tafi kitchen tana dube-dube.
Ba ta saurari mama ba sai da ta ci ta ƙoshi, Sannan ta dubi mama ta ce "Ni fa mama gaskiya ba zan sake zuwa makarantar nan ba".
"To ai ba ni zaki gayawa ba, wanda ya saka ki a makarantar zaki gayawa".
"Mama kin ga uban dukan da ake yi a makarantar nan kamar an samu bayi, kuma dan rainin hankali wai aka kai ni aji ɗaya ni za a kai aji ɗaya saboda raini, to wallahi makarantar malam babba zan koma ba zan iya ba"
Mama ta girgiza kai kawai, ta cigaba da aikin da take yi, Ruma ta saki baki ta dinga zuba tana cin alwashin ba zata sake zuwa ba.
Huzaifa ne suka yi sallama shi da Yasir, mama ta amsa musu. Basu kai ga zama ba suka hau mita.
"Mama dan Allah meyasa aka saka yarinyar nan a makarantar nan ba tare da shawarar mu ba? Kin san halin yarinyar nan tun a yau ta fara nuna halinta".
Ruma ta ce "Sha kuruminka ni ba komawa zan ba, daga yau ko za ayi ƙuli-ƙulina ba zan koma ba, wai saboda tsabar abu wai ƙari shafi guda, kuma wani satin ka kawo hadda, ni aya biyu nake iyawa waye zai yi wannan karatun taɓ ga uban duka wallahi ba zan sake zuwa ba
Yasir ya ce "Ai makarantar mu ba ta daƙiƙai ba ce ba, ki koma inda ki ka fito ba zaki zubar mana da mutunci a makarantar nan ba".
Ba tare da sun san Umar yana gidan ba, yana ɗaki a kwance suke ta wannan zubar.
Tsuru-tsuru suka yi, musamman ruma da ta fi zaƙewa, sai ganinsa suka yi ya fito tsakar gida.
"To dan ubanki ki daina zuwan kin ji ko, daga yau kar ki sake zuwa ki ga yadda zan yi da ke, kuma na gaya musu ba kya jin magana, idan har ba ki yi karatu ba su kama ki su zane ki"
Ruma a ranta ta ce "Ai wallahi sai na yi abin da za a koreni waye zai zauna ana jibgarsa kamar jaki"
Ya kalli su Yasir ya ce "Ku kuma, kune zaku dinga tsayawa a kan karatunta, ku zaku dinga koya mata dan daƙiƙiya ce, duk daɗewar da ta yi tana zuwa makarantar allo ta kasa kawo izu biyu, sai karatun wani ta je tana iyawa, daƙiƙiya ki yi musu shirme na bayar da damar a zaneki"
Kawar da kai Ruma tayi gefe, Umar ya gama bala'insa ya bar gidan.
Yana ficewa daga gidan, Ruma ta dasa wa mama kuka, a kan lallai sai ta saka Yaya Umar ya cireta daga makarantar, mama ta ce babu ruwanta.
Ko da wasa Ruma ba ta sanya a ranta za ta yi wannan karatu ba, dan idan za a kasheta ba ta ma san in da aka ƙara musu ɗin ba, ta cigaba da sabgoginta.
Da sati ya zagayo zata koma makaranta, sai da a ka kai ruwa rana, tana kuka su Huzaifa suka sanyata a gaba zuwa makaranta, suna tafe suna zaginta suna mita an haɗasu da alaƙaƙai.
Yau mama ta bata kuɗin makaranta, dan haka ta tsaya ta sayi goriba a ƙofar shiga makarantar.
Duk da babu malami a ajinsu, amma kowane ɗalibi ya nutsu sun haɗa baki suna ta tilawa.
Taɓe baki tayi, ta samu lungu ta zauna, ta kashingiɗa tana cin goribar ta a nutse.
Shigowar malamin bai hanata cigaba da hangale baki tana gwaigwayar goribarta ba.
Ba ƙaramin ƙulewa malamin yayi ba, tun a wancan satin ya lura ba ƙaramar gaɓuwa ce ba yarinyar.
Yayi mata alama da hannunsa ta je, ta tashi ta fito da jakarta da goribarta a hannu ta ce "gani"
Ya ce "Yauwwa, ta kan ki zan fara jin karatu yau, ɗauko Alqur'anin ki ki karanta ƙarin da na yi muku, sannan ki bani hadda" ɗan waro masa idanuwanta tayi sannan ta ce "Gaskiya ban iya ba wallahi, karatun yayi yawa ina laifin aya ɗaya ko biyu"
"Koma gefe ki tsaya" babu ban haƙuri babu komai ta koma gefe ta ja ta tsaya.
Ya cigaba da sauraron tilawar 'yan aji, Ruma kuma ta mayar da hankali a kan cin goribarta, ya ɗaga kai ya kalli Ruma, wani irin takaici ya ƙule shi ko a jikinta abin da ya dameta kawai take yi, ya ce "Ke zo nan"
Ta ƙaraso ta tsaya, miƙewa yayi ya ɗaga bulala zai daketa.
Ta ƙwalalo ido ta ce "Kar ka dakeni ba a dukana" bai saurari ruma ba, ya zuba mata a ƙafarta har sau biyu.
Wani uban ihu ta ƙwala, ta zube a kan ƙafarta tana jujjuya kai.
Gaba ɗaya 'yan ajin suka yi shiru suna kallonta, sai a lokacin da ya daketa ya huce sai kuma ya sha jinin jikinsa ganin uban kukan da take yi.
"Wallahi ni sikila ce ba a dukana, shikenan ba zan iya tafiya ba" gaban malamin ne ya faɗi, amma ya maze ya cewa 'yan ajin su cigaba da karatu.
A ƙalla ruma ta shafe awa guda tana kuka babu ƙaƙƙautawa kuma taƙi tashi daga wurin, wai sikilarta ta tashi.
Abu kamar wasa magana har kunnen malamai, kasancewar malamin nasu, ɗan ajin da suka yi sauka ne yake koyar da su, ba cikakken malami bane a makarantar.
Malamai suka taru a kan ruma, amma taƙi tashi wai sikila ce da ita, ba zata iya tashi tsaye ba.
Malamin nasu jikinsa sai rawa yake yana cewa "Wallahi bai san ba ta da lafiya ba"
Malamin da yayi mata interview ya ce "Kuma ni a form ɗinta yayanta bai rubuta tana da wani ciwo ba, ina ne gidanku?"
"Ni ba zan gane hanyar gidan ba, akwai yayyena a makarantar nan ku kira mini su su kai ni gida in ga mama zan mutu"
"Su waye yayyen naki?" Nan gaya musu ajinsu Huzaifa.
Huzaifa yana can yana karatu aka kirashi, yana zuwa ajinsu ruma ya ganta zaman dirshan malamai sun kewayeta.
Nan suka yi masa bayani, turus yayi yana kallon ruma yana son gano ko makircinta ne, dan shi a iya saninsa ruma ba ga da wata sikila, ban da zazzaɓi ba ta ciwon uban komai, amma a ina ta samo wata sikila?.
Ya miƙa mata hannu ya ce "Taso in mayar da ke gida"
"Ni na kasa motss ƙafata ciwo take mini" tayi maganar cikin kuka.
Huzaifa ya durƙusa ya ce "To hau bayana na mayar da ke" aikuwa ta ja jiki, ta hau bayansa ya ɗau jakarta ya ce bari ya kai ta gida.
Sai da suka yi nisa sosai da makarantar sannan ya sauketa, aikuwa ta tsaya cak a kan ƙafafuwanta.
Ya kalleta ya ce "A gidan uban wa ki ke da sikila?"
"To gani nayi za a kasheni da duka, naga a makarantar bokonmu ba a dukan wata me sikila, da na ji zafin dukan sai na ji kamar nima ina da sikilar".
Galala ya bi ruma da kallo, 'yar mitsila da ita amma ta iya makirci haka.
"To mu je ki yiwa Yaya umar abin da ki ka aikata"
Marairaicewa tayi ta ce "Dan Allah kayi haƙuri"
"Wallahi ba zan goyo ki a banza ba, ko ni sai na miki shegen duka yau" yana gama maganar ya danƙeta ya saɓata a kafaɗarsa dan zata iya ƙwacewa ta gudu.
Ayshercool
08081012243
[22/06, 9:49 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode.
*AFUWAN BAN EDITING BA*
P6
Iya ƙarfinta take ihu, tana kiciniyar sai ya sauketa, amma yayi burus da ita, sai da ya je soron gida, sannan ya sauketa ya ja hannunta zuwa cikin gidan.
Aliyu ne a tsakar gida yana yiwa mama wanki, ya ɗago ya kallesu ya ce "Ya dai, ya kake jan ta tana ihu, makarantar fa?"
Hauzaifa bai amsa masa ya tambaye shi"Mama tana nan?"
"Eh tana nan" Aliyu ya bashi amsa.
Jin ihun ruma ne ya sanya mama katse sallar walahar da take yi, ta fito tana tambayar lafiya.
Hakan yayi dai-dai da fitowar Yaya Umar, shi ma ya yi shirin fita. Duk suka zubo musu ido suna jiran jin ba'asi.
"Mama wallahi yarinyar nan ba ta da mutunci, daga sakata a makarantar nan ta fara tayar mana da hankali, yaushe yarinyar take da sikila ban sani ba?".
Mama ta ɗan yi sororo ta ce "Wace irin sikila kuma?"
"To haka ta je ta ce wai sikila ce da ita, ta tashi tsaye ma ta ƙi sai a bayana na goyota"
Yaya Umar ya kalleta ya ce "Ke meya sameki?"
Cikin in da in da ta ce "Dukana aka yi, kuma wallahi na ji zafi sosai shi ne na ce musu sikila ce da ni, na ga wata 'yar makarantar bokonmu ba a dukanta saboda sikila ce ita".
"Shi ne ki ke yiwa kan ki fatan ciwo saboda baki da hankali, ke dama za a zauna da ke baki yi abin da za a dake ki bane ba, me ki ka yi aka dake ki?" Yayi maganar cikin tsare gida.
Cikin kuka ta ɗage ƙafar wandonta, shatin bulala ya kwanta a kan fatarta, ta kalli mama ta ce "Mama kin ga fa, dan Allah a cireni wallahi ni ba zan iya makarantar nan ba, wai ban iya karatu ba shi ne aka yi mini wannan dukan, ni wallahi ba zan iya karatun nan ba, ga duka ga karatu mai yawa, da wanne zan ji?"
Cikin tsawa Yaya Umar ya ce "Wuce mu je makarantar, sai kin ci ubanki yau, ai dama karatu aka turaki ba wasa ba"
A karo na farko ta yi wa yaya Umar gardama tana kuka, ta riƙe hannun Huzaifa, ta ɓuya a bayansa.
"Ni nake miki magana ki ke ɓuya a bayansa, ba zaki fito ki wuce ba"
"Dan girman Allah kayi haƙuri, wallahi idan suka san ƙarya nake, sai sun kusa kashe ni, wallahi duka ake na tashin hankali a makarantar nan" kuka take wiwi kamar wadda aka yiwa mutuwa, mama dai ta kasa magana.
Huzaifa kuwa janyota ya yi daga bayansa, ya ce Wallahi ba zai kareta ba sai dai ayi mata duk abin da za ayi mata.
Yaya Sadik ne ya fito daga ɗakinsu, yana zuwa ya ture Umar, ya kamo hannun Rumaisa, ya wuce da ita ɗakin su.
Suna shiga ya zaunar da ita, shima ya zauna ya ɗan ƙura mata ido sannan ya ce "Auta, meke damunki ne, kullum sai an yi rigima dake an ce ba kya ji, ke ko haushi ba kya ji?"
Ta girgiza kai ta ce "Wallahi ina jin haushin yadda aka tsane ni kullum ace bana ji"
"To yanzu meyafaru, har aka dake ki ki ke cewa sikila ce dake? Kin san sikila kuwa meyasa ki ke fatan wannan ciwon?"
"Gani nayi za a kashe ni da duka, ni bana son a dake ni".
"Gaskiya ba ka kyautawa, dan me yarinya za ta yi laifi ka hana a hukunta ta, me kake ƙoƙarin koya mata ne?" Umar yayi maganar a mugun fusace.
Yaya Sadik ya waiwayo ya kalli Hussainin na sa, ya haɗa hannayensa alamar ban haƙuri ya ce "Tuba muke, zan wa tufkar hanci in sha Allah, on behalf of her, ayi haƙuri gobe in Allah ya kaimu da kaina zan mayar da ita makarantar in basu haƙuri" gajeren tsaki Umar yayi yai waje, babu wanda yake masa katsalandan kamar yadda Abubakar yake yi masa, ya fuskanci idan aka biyewa Yayan nasa ruma tsiyarta zata tsula ba tare da an kwaɓeta ba, da tayi laifi sai ya ce ƙuruciya ce.
Wunin ranar kowa share ruma yayi, yaya Sadik ne kawai yake kulata, Huzaifa da yasir suka ƙare mata zagi tsaf suka tsangwameta.
Ko a jikinta, tun da Allah ya sa ba a mayar da ita makarantar an ce ƙarya take ba, hankalinta ya kwanta.
Washegari Yaya Abubakar da kansa ya rakata makarantar, aka dinga yi mata sannu ana mata ya jiki, ta basar ta dinga amsawa.
************
Sanye yake da fararen kaya ƙal, fuskarsa sanye da fari siririn glashi, taku yake cike da ƙasaita ya biyo wata doguwar baranda.
Sannu a hankali ya ƙarasa gaban wata ƙatuwar ƙofa, ya sa hannu ya murɗata a hankali. A take ta buɗe wani sassanyan ƙamshi ya daki hancinsa.
Da sallama ya shiga ya mayar da ƙofar ya kulle, babu kowa a falon sai wata matashiyar budurwa tana saka turaren wuta.
Amsa masa tayi tare da faɗin "Sannu da zuwa".
"Yauwwa 'yar aikin Ammi, ina ma'aikatan ne ki ke aikin da kan ki?"
Ta ɗan kalle shi sannan ta ce "Nima 'yar aikin ce ai" yayi murmushi ya ce "Sorry idan haushi ki ka ji, ina Ammi?".
"Bacci take" ta bashi amsa lokacin da take cigaba da saka turaren wuta.
"Ba kowa kenan?"
Cikin ƙosawa da tambayoyinsa ta ce "Duk sun tafi makaranta".
"Ke me ya hana ki je makarantar?"
"Ohh God, uncle J am sick shi ya sa ban je ba, Ammi idan kana son ganinta ka dawo an jima, ina fatan zan iya tafiya na gama amsa tambayoyin ka?"
Ya girgiza kai ya ce "No, saura ɗaya ina yayan ku?"
Tayi murmushi ta ce"Wannan tambayar ai kai yakamata a yiwa, i don't know " daga haka ta bi wata hanya ta bar falon.
Ya girgiza kai a hankali ya ce "Wannan yarinyar ta fi mai kora shafawa, izzarki tayi yawa"
Wayarsa ce ta fara ringing, ya zura hannu a aljihunsa ya ciro wayar.
"Ke nifa kin isheni, ni kaina ban san in da yake ba, anjima kuma kilisa zan fita, zan neme ki amma" daga haka ya kashe wayar, ya saka a aljihunsa ya fice.
*********
Ruma ta sha kashedi a wurin su Huzaifa, a kan ta shiga hankalinta a makarantar nan, dan ba ƙaramin girmansu ake gani ba, halinta ba zai sa mutuncinsu ya zube ba.
Ta cigaba da zuwa makaranta, amma ba ta gane komai, idan Yasir ya zaunar da ita zai koya mata kuma, sai ta ce ita ta gaji ba ta so.
Ranar wata juma'a da yamma, Abdallah yana ta haɗa kayan miya, za a kai markaɗe, Yasir ya kalleshi ya ce "Abdallah kyanta na ɗau hotonka kana haɗa kayan miyar nan, na je na nunawa yarinyar nan mai awara".
Haɗe rai Abdallah ya yi ya ce "A'a mai wake zaka nunawa ba mai awara ba"
Yasir ya yi dariya ya ce "Zaka ga mai wake, wallahi yarinyar nan ta mato a kan ka, kawai ka nutsu ku daidaita, wallahi shar da kai awararka zaka yi ta ci"
"Na rantse idan ba ka yi mini shiru ba sai na ɓarar da kai"
Yasir ya ce "Yaya ba zan ƙoƙari na tayata kafa gwamnatin ta ba, kullum sai ta kyauta mini".
Buut Ruma ta fito daga ɗaki ta ce "Yasir yakamata muje ka gabatar mata da ni, na dinga biyawa idan zan je makaranta".
Tsaki Yasir ya yi "To munafuka waye ya sako dake, na zaci ma bacci take wallahi "
Abdallah ya ce "Wallahi ko da wasa ki ka je, sai na kakkarya ki".
"To ni ce maka ma nayi zan je?"
"Ke dai ki ka sani gulayya" Yasir yayi maganar yana hararta.
"Wallahi ni ba gulayya ba ce" shareta suka yi suka cigaba da hirarsu, yayin da Ruma ta koma gefe tana naɗar abin da suke faɗa.
Kamar yadda a islamiyya ruma ba wani ja take ba, haka ma makarantar boko ba uwar da take ganewa sai wasa.
Ta na cikin top 10 na marasa ganewa a aji, sannan ta farko a sahun marasa ji.
Yau bayan an taso daga makarantar boko, ta biyo ta hanyar da lambun mai unguwa yake. Ƙaton lambu ne da ya kasance mallakin wani a babba masarautar Kano, wanda yake ƙarƙashin kulawar mai unguwa, ba kowa ya san da hakan ba sai ɗaiɗaikun mutane.
Gaba ɗaya hanyar ba ta cikin jerin hanyoyin da zata bi su sada ta da gida, amma tun da ta ji 'yan ajinsu suna labarin mangwaron lambun ya fito yayi kyau, tayi alwashin bi ta hanyar dan ganewa idonta abin da suka gaya mata.
Aikuwa babu ƙarya, lambun ƙato ne na gaske, wani wurin an kewaye shi da katangar bulo, wanu wurin kuma aka ƙarasa kewaye shi da waya.
Akwai bishiyoyi kala-kala a ciki, wasu duk sun yi 'ya'ya kasancewar lokaci ne na damuna.
Mangwaron nan yayi 'ya'ya sosai gwanin ban sha'awa.
Ƙatuwar ƙofar shiga wurin ta gani, babu kowa a wurin, dan haka kai tsaye ta kutsa a gaban wata ƙatuwar bishiyar mangwaro ta tsaya, yanayin wurin yayi mata kyau sosai da sosai.
Ta samu dutse, ta dinga jifan bishiyar, suna faɗowa tana ɗiba, ta tara ta cika jakarta, sannan ta nufo hanyar fitowa.
Tana fitowa wani matashi yayi caraf ya danƙeta yana faɗin "Alhamdilillah, shegiya ɓarauniya ashe ku ne masu shiga lambun nan suna ƙurguma mana sata".
"Ban gane ba wace iri ɓarauniya me nayi maka?"
"Zaki ga me ki ka yi mini, gidan mai unguwa zan kai ki, ke saboda ƙwarewa ma, da ki ka sata sai ki ka biyo ta ƙofa zaki fita, kina 'ya mace kina sata"
Cikin rashin kunya Ruma ta ce "Wallahi ni ba ɓarauniya bace ba, ta ƙofar nan fa na shiga, ba wanda ya haura gida ne ɓarawo ba?"
"To da ki ka bi ta ƙofar, wa ki ka tambaya ki ka shiga ki ka ɗebo abibda ba naki ba?"
"A'a, to ni wa na gani a wurin, kuma ma naga ai bishiyar ta Allah ce, Allah ne ya fito da ita, kuma sai ace sai an tambayi wani sannan za a ɗau abin da Allah ne ya fito da shi, kai iskar da ka ke shaƙa wa ka tambaya ka ke shaƙarta?" Saroro ya bi ruma da kallo, wata 'yar cukul da ita sai shegen surutun tsiya.
"Zaki yi bayani, sai na kai ki gaban mai unguwa"
"Daɗinta shi mai unguwar ba shi da wutar da zai sakani, kuma duk in da za a je ai bishiyar Allah ce, kuma ka sakar mini hijjabi dan ni ba 'yar iska bace ba.
Bai ko saurareta ba, ya figi hijjabinta ya fara janta.
"Ka dai na ja na haka kamar wata akuya, ba ƙaramin aikina bane na cire maka hijjabin nan na ƙara gaba.
Mama sai kallon agogo take yi, tana kallon hanyar shigowa, amma babu ruma babu alamunta.
Tsakar gida ta fito tana kiran Usman, kasancewar shikaɗai ne a gidan, ya dawo da wuri bashi da lectures.
"Ka ga haryanzu yarinyar nan shiru ba ta dawo ba"
Usman Ya ce "wataƙila tana can tana rashin hankali a titi da ƙawayenta, amma maybe ki ganta yanzu".
"A'a zunnuraini, shi biyu da rabi fa take dawowa amma kalli yanzu ƙarfe ɗaya da rabi, hankalina ya kasa kwanciya"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Kuma fa kamar ma ga 'yan makarantar su lokacin da nake hanyar dawowa, amma bari na je makarantar ta su" yana rufe bakinsa, suka ji ana ƙwala sallama a waje.
Usman ya amsa, ya nufi ƙofar gidan, aikuwa yana zuwa ya tarar da an riƙo ruma, tana rungume da jakar makarantar ta, sai kumbura baki take, tana cika tana batsewa.
Kallon matashin saurayin yayi, ya ce "Bawan Allah lafiya, ya zaka riƙo yarinya haka kamar ka riƙo ɓarauniya?"
Matashin ya ce "To kusan hakan ne, karɓi jakarta ka duba ka gani"
"Ka saketa mana" yayi maganar a fusace yana fincike hannun matashin daga hijjabinta.
"Me tayi maka haka?".
"Nan matashin ya kwashe komai ya gayawa Usman"
"Wallahi ni ba ɓarauniya bace ba, tun da ta ƙofar wurin na shiga kuma ban ga kowa ba, ai ba haurawa na yi ba"
Usman ya fizgi jakar ruma, ya buɗe ya ga mangwaro ya kai takwas a ciki manya, nunannu da ɗanyu, sai goba guda huɗu.
Ya kalli ruma, sannan ya kalli matashin ya ce "Yanzu kai a kan wannan zaka danƙota ka keto layi da ita haka? Ka taɓa kamata ta shiga ta ɗaukar muku abu ne?"
Matashin ya ce "Ban taɓa kamata ba, amma ana haura mana, ayi sata"
"To kuma sai aka ce maka nice nake yi, ni wallahi ban taɓa shiga ba sai yau".
Usman ya zura hannu a aljihunsa, ya ɗauko dubu ɗaya, ya miƙawa matashin ya ce "Na san dai abin da ta ɗauka, bai kai na hakan ba, gashi nan na biya, kuma kar ka sake kiranta ɓarauniya Please, ba halinta bane ba ba ta taɓa yi ba, dan ka ci sa'a da na biyewa zuciya sai na kifar da kai, saboda yadda ka riƙo mata hijjabi, ka keto unguwa da ita, saboda ɗanyen mangwaro"
Yana gama maganar, ya ingiza ƙeyar ruma zuwa cikin gidan, suna shiga gidan ya danƙota ya ƙwace jakarta, ya durƙusar da ita ya ce "Oya tsallen kwaɗo maza"
Waiwayo ruma tayi, ta kalleshi cikin mamaki, amma taga babu alamar wasa a tare da shi, cikin tsawa ya kuma cewa tayi tsallen kwaɗo.
Mama ta fito tana faɗin "Lafiya, me aka ce tayi, sallamar da ake kenan?"
Usman ya ce "Ƙyaleni da ita mama" nan ruma ta kama tsallen kwanɗo.
Duk yadda mama tayi a kan Usman ya gaya mata me aka ce ruman tayi, amma yaƙi, sai dai ruma ta ci ƙwal ubanta, dan ko miƙewa kasa wa tayi.
Duk yadda mama ta kaɗa ta raya, amma bai gaya mata ba, kuma babu wanda ya gayawa abin da ta aikata.
****
Islamiyyar su ruma, sanya mata ido suka yi, dan ba ta iya karatu balle kawo hadda, ko karatun aka zo sai dai a tsallake ta, dan ba iyawa take yi ba.
Malamin ajin ko sabgarta ba ya shiga, tun daga ranar da ya dake ta ta ce ita sikila ce. Yau dai ya kasa jurewa yace mata "Wai ke ba kya jin haushi yadda 'yan ajin ku suke karatu, amma ke ba kya iya wa?"
"To malam karatun yayi mini yawa, yaya zan yi?"
"Su sauran da suke iyawa, da me suka fiki?"
Ita kanta ruma gaba ɗaya malamin bai yi mata ba, dan bai fi sa'an Abdallah ba, shi ma ɗalibi ne a makarantar, amma ya dinga takura mata.
Tayi masa banza tana kallon wani gefen daban.
"Magana fa nake miki?"
"To ya sayyadi me zance maka? Ni wallahi ba zan iya karatun nan ba, ni fa tun farko ba son makarantar nake ba, kawai dan yayana ya kawo ni ne".
Ita gaba ɗaya kanta tsaye take faɗar magana, ko tayi maka daɗi ko kar ta yi maka kai ta shafa.
Tsaki yayi ya ce "Daƙiƙiya mara zuciya"
Ɗagowa tayi ta kalleshi ta ce "Malam wannan ba halin musulmi nagari bane ba, ba koyarwar addinin Musulunci bace. Saboda bana iya karatu dama duk ka bi ka tsaneni Allah ya buɗa mini ƙwaƙwalwata nima. Zuwa zan yi a canza mini aji" ta tashi ta ɗau jakarta ta bar ajin, ba tare da ko izini ta nema ba.
Ta bala'in jin haushin cin mutuncin da ya yi mata a gaban 'yan ajinsu, wai daƙiƙiya mara zuciya.
Ofishin shugaban makarantar ta nufa, dan ta sanar masa a canza mata aji, malaminsu ya tsaneta, amma ta tarar baya nan.
Azuzuwa ta shiga dubawa, aikuwa ta ganshi a ajin su Yasir yana yi musu karatu.
A ƙofar ajin ta tsaya ta ce "Headmaster ina wuni?"
Ya ɗago ya kalleta, ba wanda yake ce masa wani head master sai yau a bakinta.
Ya ce "Lafiya lau"
"Malam zuwa na yi ka canza mini aji, ni na gajj da ajin nan, malamin ya tsaneni"
Dariya 'yan ajin suka fara yi, Yasir kuwa ya sunkuyar da kai ƙasa.
Yayi murmushi ya ce "To shikenan, ki je ki jirani, idan an tashi sai mu yi magana"
"To, Yasir in jiraka idan an tashi mu tafi tare?"
Wani mugun kallo ya yi mata ya ce "Da tare muka zo"
Murguɗa baki tayi, ta koma kan barandar ajin ta zauna, shiru-shiru ta gaji basu tashi ba, ta kaɗa kai tayi tafiyarta gida.
A hanya ta biyo ta filin ball ɗin su Yaya Aliyu, maza sun yi cincirindo, ana kallon ball, ta tsaya tana leƙawa ko zata hango yaya Aliyu.
Kutsawa ta dinga yi, sai gata ita ɗaya a cikin maza.
"Ruma me ki ke yi a nan?" Ta ɗaga kai ta kalli mai maganar, abokin Aliyu ne.
"Yaya Aliyu nake nema"
"To ai yana cikin fili, ball yake"
"To ai na sani, kallonsa zan yi"
Ya jinjina kai ya ce "To ai shikenan"
Kamar daga sama ya ji ana kiran sunansa, da 'yar siriryar muryarta.
Duk da yadda ya taso ball ɗin a gaba, amma sai da ya tsaya ya waiwaya.
Ruma ya hango a gaban garada, tana ɗago masa hannu.
Waro ido ya yi, ya nufi in da ruma take.
Coach ɗin su Aliyu ya fara masifa, dan ajiye ball ɗin da ya yi, ya waiwaya aka ci su ɗaya.
"Ke me ki ke yi a nan?"
"Wucewa zan na ce bari na zo na ganka"
Ya dafe kai ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ki wuce ki tafi gida"
"Dan Allah ka bari na gani"
Hankalinsa na kan ruma, coach kuma na ta masifa.
"Kai dalla wacece wannan, ku koreta daga wurin nan".
"Wallahi ba inda zani, ai wurin yayana na zo".
Aliyu ya kalli abokinsa ya cewa "Aminu, dan Allah jire mini yarinyar nan" ya koma cikin filin yana waiwayenta.
Aminu ya bata wata ƙatuwar jaka ta zauna a kai, ita kaɗai mace a cikin maza.
Yana ball ɗin amma hankalinsa yana kanta.
Ta dinga yi masa tafi tana bashi ƙwarin gwiwa, kusan duk hankali ya dawo kanta, gaba ɗaya ta bawa wasu dariya a wurin.
Da yaya Aliyu ya ci ball kuwa, ta dinga tsalle tana murna, ya ci ball biyu.
Da aka tashi har hoto aka yi mata, ita da Aliyu ta riƙe kofin da suka ci, kasancewar ball ce ta cikin unguwa.
Ba a tashi daga ball ɗin ba, sai ana kiran sallar magariba, mama tana can ta sa an yi sahu ya kai uku a makarantar su, ana nemanta.
Suna tafe a hanya tana yabawa yaya Aliyu, abokansa sai tsokanarsa suke yi a kan ruma.
"Yaya Aliyu, akwai wani wanda kuna ball ɗin, ya dakar maka ƙafa, na ji haushi idan na ganshi sai na buga masa dutse wallahi".
"Ni ban saki ba, kuma baki ga an bamu pk ba da ref ya gani"
"Oho ni na san wani pk, amma da ka tsaya ja masa duka ka rama, daga wasa sai cin zali"
Haka suka ƙarasa gida, mama na tsaye da carbi a tsakar gida, tana tunanin ta ina ruma zata dawo.
Sai gata ita da Aliyu, yana riƙe da hannunta.
Mama ta kalleta ta ce "Ke daga ina?"
Sai a yanzu ta tuna daga islamiyya ko gida ba ta zo ba, ta kalli ya ya Aliyu ya kalleta.
"A ina ka ganta?" Mama ta tambaye shi tana kallon ruma.
Aliyu ya ce "wallahi mama nima kawai ganinta na yi a filinmu, ban san ina za ta tsaya ba idan na ce ta taho, shi ya sanya na ce ta tsaya"
"Kina mace uban me ya kai ki filin ball?" Huzaifa yayi maganar a ƙufiule, dan takalminsa har tsinkewa ya yi saboda nemanta.
Hararsa tayi ta sake noƙewa a jikin Aliyu.
Duka Huzaifa ya kawo mata, Aliyu ya tare ta, ya ce laifina ne duk Allah ya baku haƙuri.
Mama ta fara tunanin anya ba zata kai ruma wurin malaman ruƙiyya ba, abin na ta ya fara bawa mama tsoro sosai da sosai.
Kamar yadda ruma ta saba kwatsa zance, bayan kowa ya halarra, haka yau ma sai da kowa ya halarran, an gama cin abinci sannan ta gyara murya ta ce "Yasir, wai yaushe ku gama karatun ɗazu da naje ajinku".
"Ban sani ba" ya bata amsa.
"Mhmm ai dama ba zaka sani ba, nifa gaba ɗaya mutuncin malamin nan ya zube a idona, wallahi mama idan kin ji me yake gaya musu sai kin riƙe baki, duk da wani abun bana ganewa, duk basu san daga waje ina jiyowa ba, kuma maimakon Yasir ya fito daga ajin nan, amma ina yana zaune ana koya musu abin da bai kamata ba.
Saroro yasir ya yi, ya ji me aka koya musu da bai kamata ba, suna haɗa ido da ruma, ya tuna karatun da aka yi musu, kan ya kai ga ɗaukar mataki ta ce "Ina ji ai yana ce muku, wai ko idan mutum ya rungume mace alwalarsa ba ta karye ba, ko kiss, dan Allah wannan mama ba iskanci bane da ɓata tarbiyya, nan idan muna kallo aka nuno kiss ɗauke tashar ake yi, amma wai malaminsu yake gaya musu.
Kuma naga ai turawa ne kawai suke rungume-rungume da kiss, mu wannan ba ɗabi'ar mu ba ce amma yake gaya musu, wallahi makarantar nan ɓata tarbiyya ake yi".
"DANƘARI!!"
GODIYA GA TARIN MASOYA MASU BIBIYAR LITTAFIN ƘANWAR MAZA, COMMENT ƊIN KU NA SANYA NI NISHAƊI, KAR A MANTA DA SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊIN MU DOMIN SAMUN DAƊAƊAN LITATTFAN HAUSA NA SAURARO.
AYSHERCOOL
08081012143
[25/06, 4:11 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
P7
Dafe goshi Yasir ya yi yana murzawa a hankali, ruma 'yar bala'i ce, ba zata tashi yi maka hansfree ba a cikin jama'a sai kowa ya hallara kamar mai sanar da wani abu mai muhimmanci, in da ya gode wa Allah da ya kasance, a makaranta ta ji ana koya musu, da bai san da wasu kalaman zai amfani wurin kare kansa ba.
Ita kuwa ta zaƙalƙale tana ta jawabi, babu wanda ya tanka mata, karo da idanun Umar ne ya sanya mata aya a jawaban da take kwarowa babu ƙaƙƙautawa.
"Zo nan" yayi maganar cikin bada umarni.
Kamar mara gaskiya haka ta tashi ta je gabansa ta durƙusa.
"Je ki ɗauko mini jakarki ta makarantar boko da ta islamiyya"
"Dummm ta ji gabanta ya faɗi, har gara jakar islamiyyar ta ma, tun da ba a daɗe da sakata ba litattafan da mutuncinsu, amma ta makarantar boko dai kam sai dai Allah ya kyauta.
Jiki babu ƙwari ta je ta kwaso jakunkunan, ta zo gabansa ta ajiye su.
Ya kalli jakarta ta makarantar boko, duk ta ci ubanta da jagwalgwalon biro, har da zanen 'yan aljanu a jiki da su ABCD a jikin jakar, sunan 'yan gidan nan kuwa babu wanda ba ta rubuta a jiki bs. Tun daga nan ya san cikin jakar ma ba za ayi abin arziki ba.
"Oyaa zazzage litattafan na gani"
Babu musu ta janyo jakar ta zazzage, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, litattafan nan sun ga duniya, tamkar ɓera ya ci rage mata. Kaf litattafan babu bango a jikinsu, sun yi kaca-kaca, wasu ma nannaɗe su tayi, wasu ta ninka su biyu, a taƙaice kai ka ce bolar wani office ɗin ce. Sai uban fensura sun kai biyar a cikin jakar, ga su ulu da farar ƙasa da sauran goriba duk a ciki.
Umar ya kalli ruma, ya kalli bolar dake gabansa, dan ba zai ce litattafai ba.
"Yanzu wannan sharar ce litattafan karatun naki?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
Ya sanya hannu ya ɗau littafi ɗaya yana dubawa, ba uwar da take yi a ciki, littafi ɗaya sai ta yi duk subject ɗin da ta ga dama a ciki.
A hankali ya cigaba da duba litattafan nata, ga class work da tarin assignment, wasu tayi ta ci zero wasu makin da take ci ma gwanin ban haushi, subject ɗaya ya ga ta mayar da hankali tana yi yadda yakamata, kuma ba ta faɗuwa shine maths.
Yayi ajiyar zuciya ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Ashe asarar kuɗin tara kawai ake a banza ko? A biya miki kuɗin makaranta idan zaki tafi sai an baki abin tafiya makaranta, amma ki je kina wannan jakancin, kalli wai wannan ne litattafan ki na karatu, kalli wannan wai 4\20 ki ka ci, ba zaki iya kawo abin da baki iya ba gida a koya miki, wasa da surutun banza faɗi ba a tambaye ki ba shi ki ka saka a gaba ko?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"Ƙarya na yi miki kenan? To bari ki ji na gaya miki, ina nan zan zuba ido a kan result ɗin da zaki kawo wannan karon, wallahi idan bai yi mini ba sai an miki repeating "
Ras! Gaban ruma ya faɗi "Na shiga uku, dan Allah ka yi haƙuri, zan daina surutun in dinga karatu".
"Kar ma ki yi, wallahi primary 1 zan saka a mayar da ke, ki cigaba da daƙiƙanci, kuma ina samun information a kan abin da ki ke a islamiyya, ke kin zama jan wuya zaman ajinku ma ba kya yi, ke kin sakawa kan ki ba zaki iya karatu ba ko? Oya buɗe Alqur'ani nuna mini a surar da ku ke"
Ai nan ma badan-badan tayi ta yi, domin kuwa ba ta san a ina suke ɗin ba.
Carbi ya bata, ya biya mata aya biyu, ya ce tayi ta maimaitawa sai tayi ƙafa dubu.
Da haka yaya umar ya ƙwaci yasir, ta zauna ta dinga nanata karatu har barci ya fara ɗaukar ta, da ta fara bacci yake zuba mata carbi a ƙafa, ta tashi a gigice ta cigaba da karatun, da haka sai da ta haddace rabin shafi, bai ƙyaleta ta kwanta ba sai wurin ƙarfe ɗaya na dare, da kuka haka ta kai karatun nan, ya sa ta kwashe bolar litattafan ta ya sallame ta.
Washegari, har makarantar boko, yaya umar ya je ya iske ta, ya kai mata sababbin litattafai, ya sanya aka kirawo ta ofishin shugaban makaranta, nan ma ba abin da suke yi, sai wassafawa yaya Umar halin ta na rashin ji.
Ya bata litattafan, yayi mata kashedi tare da jadadda mata, idan har ta cigaba da daƙiƙanci, sai ya sa an yi mata repeating.
*********
Zaune take a kan makeken gadonta, ɗakin cike da kayan alatu kai da gani ka sam mai ɗakin 'yar gata ce.
Ta dunƙule wuri guda a kan gadon, idanunta sun yi jawurr alamar ta sha kuka.
Daga ita sai doguwar riga 'yar kanti, kanta babu ɗan kwali, kallo ɗaya zaka yi mata ka san tana cikin matsananciyar damuwa.
Turo ƙofar ɗakin aka yi, wata babbar mace ce ta shigo ɗakin, idonta sanye da farin gilashi, hannunta riƙe da tray da cup.
Cikin tausayawa ta kalli yarinyar, ta ɗan girgiza kai, ta ƙarasa ta ajiye trayn, ta rungumota tana faɗin "Haba Iman ɗina, shikenan rayuwa bawa ba zai jurewa ƙaddara ba? So ki ke ciwona nima ya tashi?"
Iman ta girgiza kai, hawaye na cika idanunta.
"To Meyasa zaki takura kan ki, haka Allah ya so dama, ai dama tun farko biyayya ce zaki yi mini, kuma Allah bai yi yiwuwar abun ba, amma ki yi haƙuri kin ji babyna"
Ta jinjina kai lokacin da take sake kwantar da kanta a jikin matar.
Ta ɗakko tea a kofa tana bawa Iman a baki, tana sha tana share hawaye, kai da gani ka san akwai tsantsar soyayya da ƙauna a tsakanin su. Ta gama bata tea a baki, ta dinga shafa gashin ta, tana yi mata nasiha.
**********
Mama ta mayar da hankali sosai a kan ibada, mutane na ta shirin zuwan watan ramadan, mama tana ta azumi ita da su yayyen ruma, amma ban da hajiya ruma da cin abincinta ne kawai ya dameta.
Yanzu haka ta cinye taliya, ba ta ƙoshi ba, ta kwaɗa garin kwaki ta zauna tana ci.
Yasir sai masifa yake mata, wai shegen ci ne da ita kamar akuyar ƙauye, ko saurarensa ba ta yi ba ta cigaba da tura abincinta.
Mama ta kalleta ta ce "Wai ke ruma, ko zuciya ba zaki yi ba, azumin nan da kowa yake yi na neman lada ko guda ɗaya ki gwada ba?"
Ɗan ɓata fuska tayi ta ce "Mama ni sai Allah ya kaimu watan ramadan, idan na fara azumi tun yanzu, ai ramewa zan yi kan salla"
"Ke ta ramewa ki ke, dan ubanki ina nuna miki ibada amma ke ba kya so"
Shiru ta yiwa mama tana cigaba da danƙarar garin kwakinta, dan ba ta ji za ta iya wannan azumin ba, idan na du gari ya zo dai ta jarraba.
Bisa ga jajircewar yaya Umar, aka samu ruma take ɗan taɓuka abin arziki a makarantar islamiyya, shima ba wani sosai ba, dan sam ba ta bayar da hadda, tana iya ƙoƙarin ta ko ba duka ba, ta ɗan iya karatun da aka biya musu, saboda idan yaya umar ya titsiyeya ta ɗan samu abin karanta masa dan ya bari ta yi barci, idan kuwa ba baka ba ta san sauran.
Yau ana can ana sallar la'asar, ruma tana zaune tana shan mangwaron ta, tuni ta yi sallarta a cewarta ba za ta iya bin jam'in nan ba, tun tana tsayuwa sai jiri ya fara kwasarta ba za ayi a idar ba.
Ta gama shan mangwaronta, ta tafi wurin alwala wanke hannu.
A wurin alwalar akwai yaran da suma ba sa sallar, suke ta wasan su.
Babu tsammani, ruma ta ji an zuba mata bulala. Tamkar wadda ta fita hayyacinta, haka ta tashi a gigice, tana duba wanda yayi mata wannan ɗanyen aiki haka.
Wani prefect ta hango, bayan ya zuba mata bulalar ya tafi kora sauran yaran da bulala.
Cikin kiɗimewa, ta ɗauki ƙatuwar buta guda ɗaya, ta bishi a guje tana ihu, ta dinga watsa masa ruwan. Ya waiwayo ya tsaya yana kallonta, ta ga hakan bai mata ba ta dinga ƙwala masa butar, daga ƙarshe ta durƙusa ta ɗibi ƙasa tana watsa masa tana kuka.
Tamkar soko, haka ya tsaya yana kallonta, ko ƙwaƙwƙwaran motsi ya kasa, balle ya kare kansa.
An idar da salla kenan, hankali ya fara dawowa kan in da kukan rumaisa ke tashi, bayan ta gama ɓata masa jiki da ruwa da ƙasa a gogaggen uniform ɗin sa, ta haɗa hannayenta biyu tana yakushinsa gami da kai masa duka.
Da ƙyar wani malami ya ɓanɓareta daga jikin matashin yaron, wanda ba dan ya girmeta ba, kuma babu dutse to babu abin da zai hana ta fasa masa kai da dutse, dan ba ta ga laifin da ta aikata zai zuba mata wannan bulalar ba.
Malamin ya dubi ruma ya ce "Meyasa ki ka yi masa haka? Meye haka ki ka yi?"
Cikin kuka ta ce "Dukana ya yi babu abin da na yi masa, wanke hannuna kawai nake yi shine ya dake ni, kuma wallahi ban yafe ba". Har ta gama maganar kuka take yi, jikinta yana rawa.
Yayin da hankalin ɗaliban duk ya dawo kan su ruma, da jikin Auwal da ruma ta duƙunƙuna masa kamar ya faɗa taɓo.
Haƙuri malamin ya bashi, ya ce ya je ya wanke jikinsa.
Kuka ne kawai auwal bai yi ba, amma ya ji zafin abin da ruma ta yi masa ba kaɗan ba.
Auwal ɗan ajin su Yasir ne, ya san ƙanwar yasir ce, sai dai sam bai taɓa shiga sabgar ruma ba, kuma shi bai ma san ita ce a durƙushe a wurin ba, yayi mamakin ƙarfin hali da kuma tsaurin ido irin na ruma.
Ko da labarin abin da ruma ta aikata ya kai kunnen yasir, haƙuri yayi ta bashi, auwal ya nuna ba komai, amma a cikin ransa yana jin ba zai iya ƙyale ruma ba sai ya ɗau mataki a kanta.
Babu yadda Yasir bai yi da ita a kan ta ba wa auwal haƙuri, amma mursisi ta ce sai dai ya mutu idan har sai ta bashi haƙuri.
Tun da ruma ta yiwa auwal wannan haukan, sauran prefect ɗin ma tsoron taɓata suke yi, dan sun fi yadda da aljanu ne da ita, saboda tsaurin idonta yayi yawa sosai.
*********
Gaba ɗaya ruma ba ta wani ɗokin zuwan salla, saboda ta san ba ta da kayan salla, mama da gaske ba zata ƙara mata komai na kayan salla ba, ko kayan ado da ake saya mama taƙi sai mata, a cewar mama wannan shine hukuncinta na ƙin jin magana. Ta ji haushi sosai amma ta danne ta cigaba da zuba ido, dan kuwa sallar akwai sauran lokaci.
Yau ta shigo gida daga makarantar boko, da wata takarda a hannunta sai yashe baki take yi.
"Deluwa, murmushin me ki ke yi ne haka, takardar meye a hannunki?"
Kallon banza ta yiwa Huzaifa ta ce "Na gaya maka bana son sunan amma ka ƙi daina gaya mini, sai na maka rashin kunya ace bana ji"
Huzaifa ya ce "Yi mini rashin kunyar, ki gani idan ba ɓarar da ke ba".
"Hmm haƙuri halin abin ƙaunar mu Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, shi ya sa ba zan kula ka ba" girgiza kai yayi yana murmushi, ta cire takalmanta ta shiga ɗakin mama.
Mama ce da Abdallah a zaune a falonta suna hira, yana guga.
Mama ta dubi ruma ta ce "Murmushin me ki ke yi ne?"
Ruma ta ɗagowa mama takarda ta ce "Presentation zan yi a makarantar mu, kowa aka bashi, ni ba a bani ba, na dinga kuka da ƙarfi nace idan ba a bani ba, na daina zuwa makarantar, shi ne fa Headmaster ya ce nima sai an bani, spelling b ne zamu haddace words ɗin nan ɗari biyu da hamsin, zamu yi mu da 'yan wata makaranta"
"Ai fa kai ba hankali, wai ki ka dinga kuka da ƙarfi ko kunya ba ki ji ba" Abdallah ya faɗa a hasale.
"To ai da ban yi hakan ba, ba zasu bani ba" tayi maganar cikin taɓara.
Mama ta ce "amma dai ba su san ta nawa ki ke zuwa ba ko da suka baki?"
Ruma ta tsuke fuska ta ce "Wato mama ke ma dai daƙiƙiyar zaki ce mini ko?"
Abdallah ya ce "To mecece idan ba daƙiƙiyar ba" gaba ɗaya haushi ya kamata, ba ta kuma kulasu ba ta shiga sabgoginta. Duk wanda ya shigo ta ce masa an bata spelling b sai su ce ai ba ci za ta yi ba, kada makarantar za ta yi.
Babu wanda ya bata ƙwarin gwiwa, ga yaya Abubakar ya koma makaranta, dama dai yana nan ne shine zai biye mata.
Zaune yake a cikin chemist ɗin, yana jiran mai chemist ya sallame shi, kamar daga sama ta shigo chemist ɗin ta ce "Gashi ka bawa mama maganin ciwon kai" na zai manta wannan muryar ba, ko a mafarki ya ji ta, yana ɗaga kai suka haɗa ido.
Murmushi ta yi masa ta ce "Yaya auwal ina wuni" juyawa ya yi ko da wani take ba da shi ba.
"Baka da lafiya ne?" Tayi maganar tana kallon allurar da mai chemist ɗin yake zuƙewa.
A hankali ya ce "lafiya lau, ya su yasir?"
"Suna nan lafiya, ya jiki?"
Da sauƙi ya bata amsa, yana tuna yadda ta damalmala masa kaya a islamiyya, da yadda yayanta ya rutsata ta bashi haƙuri amma ta ce sai dai ya mutu, ba zata bayar ba, idan suka haɗu a makaranta, sai ta tsaya ta harare shi, har da murguɗa baki, amma wai yau take gaishe shi, har da su yaya bayan ko yayan nata yasir ba ta ce masa yaya.
"Deluwa wannan hamsin ɗin taki za ta karɓuwa kuwa?" Cewar mai chemist.
"Awaisu mai chemist, duk ranar da na tashi jajjaga maka rashin mutunci, a kan kirana da deluwa, sai ka yi kuka" ta faɗa very serious.
Dariya ya yi ya ce "Ke, ai ko ban kai sa'an 'yan biyun gidanku ba, na san na girmi Aliyu, amma ni zaki saka kuka?"
"To shikenan, ka cigaba zaka gani, bani maganina na tafi"
Bayan ya bata maganin ta kalli auwal ta ce "Yaya auwal, Allah ya ƙara lafiya" tana gama maganar ya fita tana tsalle kamar kwaɗuwa.
Tun da ga ranar da suka haɗu da auwal a chemist, kullum ta ganshi a makaranta sai ta gaishe shi, duk da baya sakar mata fuska idan zai amsa, amma bai sanya ta daina ba.
****
Ɗaya ga watan ramadan, bayan gari ya ɗauka an ga wata, mutane na ta shirin ɗaukar azumi, da asuba mama ta tashi kowa sahur, amma da ƙyar ruma ta tashi ta yi sahur, saboda nauyin bacci.
Ranar ɗaya ga azumin ya kama asabar ce, ruma ta ce gaskiya ba zata iya zuwa islamiyya ba, tun ƙarfe goma take jin kamar zata mutu.
Wajen ƙarfe sha biyu na rana, ta dinga yiwa mama kuka tana burgima wai hanjinta na gutsutstsurewa ita fa mutuwa zata yi.
Aliyu ya ce 'mama dan Allah ki ƙyake yarinyar nan, tun da ba zata yi ba ta je ta ƙarata".
"Aikuwa sai ta yi, idan ya wajaba a kan ta wa zai mata?"
"Mama ki bari ua wajaban sai ta yi, kalli fa kamar zata rasu"
Mama ta ce ruma ba zata karya azumi ba, mama tana can tana salla, ya kandamowa ruma ruwa ta sha ta karya azumi.
Sai da mama tayi kamar ta zane Aliyu dan takaici, a ganinta sangartar ruma ta yi yawa.
Abu kamar wasa, ruma taƙi yin azumi, idan ma ta ɗauka ta ji wuya, sai ta karya abin ta, idan aka sha ruwa kuwa tafi uban kowa zaƙewa, daƙyar ska samu ta yi shida, shima Usman ya ce bai yarda da ingancinsu ba. idan aka ce ta je sallar asham kuwa sai ta ce ita wallahi gajiya taje yi da tsaiwa, ƙafafuwanta sai sun fara suɗewa ake ruku'u, nan ma sai bayanta ya kusa karyewa ake ɗagowa ba zata iya ba. mama kuwa ta gaji ta kamata ta zaneta da mafici.
Idan kuwa aka matsa ta je sallar asham, wataran a can cikin yara ake tsintowa mama ruma tana tsalle -tsalle ko dambe a maimakon salla, tilas mama ta hanata zuwa take titsiyeta su yi a gida.
Sai da salla ta gabato, ruma ta sake da tabattar da mama ba zata yi mata wani ɗinkin ba, ta dinga yi wa mama magiya, a kan ta yi mata wasu kayan, amma mama ta ce ba zata yi ba, lokaci ne da zata rama rashin jin da ruman take yi mata.
Gaba daya ɗokin sallar ya fita daga kanta, saboda ba ta son kayan da aka sai mata, gashi sallar bana ko arzikin takalmi da jaka bata samu ba, dan haka ta ce ba zata yi ko kitson salla ba.
Mama ta bata kuɗi ta ce taje ayi mata lalle, dan ba zata yi salla haka ba.
Ruma ta tafi ƙunshi tun safe, sai bayan la'asar ta dawo.
Mama ta kalli lallen nan babu kyan gani, kamar ana saka shi aka ɗauraye.
Kafin mama tayi magana mai lallai ta kira mama, suka gaisa.
Mai lalle ta ce "Mama, wallahi kar ki ga lallen ruma bai yi kyau ba, ana saka mata wai sai an cire ba ta so ta gaji, da na ƙi cire mata, ta cire abinta wai kashi take ji"
Mama ta ce "To shikenan, kar ki damu na gode sosai" ta kalli in da ruma ta tsaya ta ci magani kawai ta jinjina kai ba ta ce mata komai ba.
Tun magariba, ruma taga mama ta kwaɓa lalle kaya guda, ba ta kawo komai a ranta ba, ta cigaba da harkokinta.
Sunanta da mama take kirane, ya sanya ta san asuba ta yi, ta yinƙura zata tashi, ta ji motsin leda a ƙafarta, ta tashi zaune amma ta ga hannunta da ƙafarta duk leda.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, mama me ya sameni?"
"A ina?"
"Wannan ledar mecece?"
Mama ta ce "Ahh, ruma ai ba ke kaɗai ki ka san ta kan tsiya ba, na sai miki kaya ba godiya ki ka raina, na biya kuɗi ayi miki lalle ki ka ƙi zama, ai da ni ki ke zancen, kina wannan shegen baccin na yi miki dungulmi da shi zaki yi sallar, tsohuwa ta faɗa kwata ba, irin wanda nake yi, kuma kitso ma gidan Hanne zan saka Huzaifa ya kai ki, tayi miki zane huɗu ba dai ba kya ji ba, ai daidai nake da ke, ina sane nake kawar miki da kai".
Ruma ta kalli yadda aka ƙunshe mata ƙafa har ƙwauri, ga hannayenta kuma ana batun ayi mata zanen Hausa guda huɗu a ka tayi salla, ta tuna uwar rigar da zata saka a matsayin kayan ssllarta, ta ɗora hannu a ka ta zunduma ihu.
DAN ALLAH MASU NEMA DAGA FARKO KU DINGA TAMBAYA A GROUP KO DUBA WATPAD KO AREWABOOKS NA GODE
AYSHERCOOL
08081012143
[03/07, 2:14 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode
*Ina miƙa saƙon godiya, ga waɗanda suka yi mana ta'aziyya na rashin uba da 'yar uwa Naima Suleiman (Nimcyluv) ta yi, muna fatan Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahama.*
*TAƘABBALALLAHU MINNA WA MINKUM, INA TAYA AL'UMMAR MUSULMI BARKA DA BABBAR SALLA, UBANGIJI ALLAH YA KARƁI IBADUNMU YA MAIMAITA MANA*
P8
Da rige-rige Usman da Abdallah suka shigo ɗakin, suna tambayar meyafaru da ruma take wannan uban ihun.
Kallonta Usman ya yi, ya kalli mama ya ce "Mama meya sameta ne?"
Mama ta ce "Ku tambayeta mana, ba gata nan a zaune ba"
Abdallah ya ce "Ke menene?"
Nuna masa hannunta ta yi, tana sake fashewa da wani uban kukan.
"Wannan ledar ta meye haka a hannunki, kamar wata miskiniya"
Ɓare baki tayi, ta cigaba da kuka iya ƙarfinta.
"Dalla ki rufewa mutane baki, kiyi mana bayanin menene?" Usman ya daka mata tsawa.
"Ba mama ce ba"
"Me maman tayi?"
"Ta yi mini lallen tsofaffi wai tsohuwa ta faɗa kwata ina bacci, wallahi dariya za ayi mini idan aka ganni da shi".
"Kuma saboda baki da mutunci, ki ke mana wannan uban ihun da Asubar nan, ke dai ba zaki yi hankali ba ko?"
"Wallahi mama ba ta sona, ban san meyasa ta tsaneni ba, wayyo Allah na"
Abdallah ya ce "Allah ya ƙara, a wannan shegen baccin naki, har aka yi miki lallen baki sani ba".
Mama ta ce "Ki tashi ki kwance lallen nan kiyi salla".
Ko motsi ruma ba ta yi ba balle ta tashi.
Abdallah ya ce "Wai wane irin lalle ne tsohuwa ta faɗa kwatar ne?"
Cikin kuka ruma ta ce "Irin fa wanda mama take yi a ƙafarta"
Dariya ce ta ƙwacewa Abdallah, ya ce "Haba mama, ya zaki yi mana haka?"
Mama ta ce "Hukunta ta nayi, duk rashin jin da take yi ba ta zaci ina da hanyar hukunta ta ba, na bada kuɗi ayi mata abin arziki na zamani, amma taƙi zama, ai da ni ki ke zancen, kuma ajima da kaina zan kai ki kitso zane huɗu za ayi miki".
Sosai ruma take kuka, Usman kuwa ficewa yayi ya cigaba da sabgarsa, Abdallah ne ya kaita bakin rariya, ya tayata ya cire ta wanke, aikuwa hannunnan yayi jawur, lalle ya kwanta ɗoɗar hannunta da ƙafarta.
Da gari yayi haske kuwa, Huzaifa ya ga lallen rumaisa, ya zauna ya sakata a gaba ya dinga yi mata dariya, har da kifawa, wai hannunta kamar kuturwa.
Ko Abincin safe ruma ba ta ci ba, sai kuka da goge hawaye, wajen ƙarfe goma na safe, mama ta sakata a gaba zuwa gidan kitso.
Kamar yadda mama ta faɗa, kitson hannu biyu aka yiwa ruma, gashi ta sha azaba a wurin mai kitson, saboda da ta ƙi tsayawa, mama na dukanta, matar kuma ta matse mata kai a tsakanin cinyoyinta, ga kitson azabar zafi tamkar za a zaro ƙwaƙwalwarta saboda yadda matar ke jan gashin.
Ko da aka gama kitson, ruma ta haɗa gumi ga hawaye da majina saboda azabar zafi, mama ta sakata a gaba suka tafi gida.
Ruma da ta kalli hannunta ranta yake ɓaci, saboda hannun ganinsa take kamar ba nata ba.
Har ana gobe salla ruma bata farin ciki, ji take ina ma ace an fasa sallar idi wannan shekarar, saboda wannan yankan ƙauna da mama tayi mata.
Har bata son a aiketa, dan idan ta fita ta ga yara sun sha kitso da ƙunshi, sai ta yi kuka, saboda yadda ta ƙarfi ita aka mayar da ita zamanin mutanen da.
Yanzu haka tana tafe a hanya, zuwa aiken da mama tayi mata, ta gaji da tafiya ga ɓacin rai, ta samu wuri tayi zamanta a kan wata baranda, tana share hawaye.
"'Kukan me ki ke yi ne haka, ba aiken ki aka yi ba?"
Ta ɗaga kai taga mai maganar, Auwal ne, na makarantar islamiyya da ta yiwa bori rannan.
Shiru tayi masa tana tura baki.
"Meyasa ki ke kuka?"
Miƙewa ta yi tsaye tana faɗin 'Babu komai"
Ya ɗan girgiza kai ya ce "Ina Yasir?"
Cikin ƙunƙuni ta ce masa bata sani ba, tayi wucewarta.
Mamaki ne ya kama shi, duk in da ta ganshi ko ba zai kulata ba, sai ta yi masa magana, amma yau tayi masa wulaƙanci.
Aiken da bai fi tayi shi a mintuna ashirin ba, sai da ta shafe awa biyu da rabi, ta koma gida Aliyu sai da ya murɗe mata kunne, saboda yadda ta je ta daɗe.
Da safiyar salla kuwa, an kai ruwa rana da hajiya ruma kafin tayi wanka, dan cewa ta yi ba zata je idi ba.
Huzaifa kuwa musamman ya ƙi shiri da wuri, sai ya ga shigar da ruma zata yi yayi mata dariya.
Ta na kuka, mama ta watso mata wannan atamfa da ta zauna ta dinga kushewa.
"Mama dan girman Allah ki barni na saka tsofaffin kayana, wallahi bana son kayan nan".
"Ni ki ke gayawa ba kya son kayan nan, zaki saka ki wuce ko kuwa?"
Za ta tsaya gardama Aliyu ya yi mata tsawa, ya ce ta ɗau kayan ta saka su wuce sallar idi.
Ga lalle dungulmi, ga kaya ɗinkin mutanen farko, ga kai babu kitso mai kyau, ba yari ba sarƙa koma kamar 'yar ƙauye.
Huzaifa kamar ya shiɗe don dariya.
"Yarinya kin yi kyau kamar bafulatanar ƙauye" Yasir ya yi maganar yana dariya.
"Babu ruwanka da ni Yasir, zan maka rashin mutunci wallahi".
"Na kuma jin bakin ki sai na ɓarara da ke, maza wuce mu tafi" Aliyu yayi Maganar yana nuna mata hanyar fita.
Usman ne ya miƙo mata sabon hijjabi ya ce "Gashi nan ba dan hakinki ba".
Ajiyar zuciya ta yi, ko ba komai hijjabin zai taimaka mata ta rufe wannan buhun ɗinkin, tun da hijjabin dogo ne.
Karɓa tayi tana yi masa godiya, ta saka suka tafi idi.
********
"Masha Allah, looking take away my beautiful angel" Ammi ta faɗa tana kallon Iman.
Murmushi iman tayi ta ce "Ammina, an yi salla lafiya"
"Alhamdilillah my dear, ina fatan dai an yi mini Addu'a"
Murmushi ta yi ta ce "Ba dole ba Ammina"
Wata matashiyar budurwa da ke zaune a kan kujera, ta ɗago ta ce "Wai mu Ammi baki ganmu bane?"
"Na ganku mana"
"Ai shikenan Ammi, wannan wariyar launin fata tayi yawa, mu shikenan ba za ki dinga kallanmu ba, sai wannan mai kama da bafulatanar dajin" cewar ɗaya yarinyar.
Ammi ta ce "Kun dai ji kunya, da ku ke kishi da ƙanwarku"
Iman tayi musu gwalo ta ce "Iya wuya dai, nice ta gaban goshin Ammina"
'Ta mayar da ke ciki, ko a saka ki a zanin goyo a baki Nono, ƙarshen ƙauna"
Ammi ta girgiza kai ta ce"Allah ya shirye ku, Iman ki je ki shirya direba zai kai ki gidan zinariyar Galadima, ki kai musu Abincin salla".
Ɓata fuska Iman tayi ta ce "Ammi"
Kan ta ƙarasa maganar, Ammi ta ɗora yatsanta a kan lips ɗin ta ta ce "Shhhh, bana son musu, tana ta complain ba kya zuwa" Ɗan gyaɗa kai Iman tayi ta ce "Shikenan Ammi, bari na shirya"
*****
"Ke ba zaki ta so ki fara kai tuwon nan ba"
Ruma ta kwaɓe fuska ta ce "Dan Allah mama ki yi haƙuri, ki bawa su huzaifa su kai wallahi idan na fita dariya za ayi mini"
"Ni nake aiken ki, ki ke cewa na aiki wani ruma, ni ko ruma?"
"A'a mama ba haka bane ba, wallahi dariya yara suke yi mini" tayi maganar hawaye na taruwa a idonta".
"Tashi ki wuce ki je aiken da aka yi miki" Usman ya daka mata tsawa.
Jiki na rawa ta tashi, ta ɗau kwanukan da mama ta zuba tuwo, ta fara kai wa.
A hanya ta haɗu da wasu 'yan makarantar bokon su, cikin fara'a ɗayar ta ce "Laa ruma, ya ki ke ina kayan sallar ki?"
Ruma ta kalleta ta ce "Ji masifa, to ba ni da su, ba a ɗinka mini ba"
"Daga tambaya sai masifa?"
"Eh, ina ruwanki da ina kayan salla na, tsirara ki ka ganni?" tayi maganar tana saye hannun ta a cikin hijjabi.
"Kutmelesi, ruma meye wannan a ƙafarki?" Gaba ɗaya suka kalli ƙafar ruma, da take sanye da silifas ɗan madina, ga ƙafa tayi maroon da lalle, kasancewar ruma ba iya ɗaurin zani ta yi ba, zanin ya ɗage har ƙwaurinta, kuma hijjabin bai gama rufe ƙafar ba.
"Kutmelesi, wane irin lalle aka yi miki, lallai mai lallen nan ta cuceki, kut kamar ƙafar tsohuwa"
Dariya yaran suka kwashe da ita suna sake leƙa ƙafarta.
Cikin takaici, ta juya zata tafi, amma wata zaƙaƙurar yarinya, ta biyo ruma tana ɗage mata zani.
Mai jiran ƙiris ya samu a sarari, tuni ruma ta yi watsi da kwanuka, ta fara sana'ar ta ta dambe.
Kasancewar a ƙule take dama, ta rasa in da zata sauke fushinta, dan haka ta zage ta kama yarinyar nan ta dinga jibagarta kamar Allah ya aikota.
Suna cikin damben Allah ya bawa yarinyar sa'ar ketawa ruma hijjabi, hakan ya ƙara tunzura ruman, ta danne yarinyar tana duka.
"Wannan yarinya an yi jarababbiya, duk in da ta tsuguna sai dambe, sai ka ce annoba" cewar wani mai awo a gefe, da bai raba su ba sai zance.
Ɗagowa ta yi cikin masifa ta ce "Wallahi ni ba annoba bace ba"
Ta duƙa ta cigaba da dambenta. ji tayi an yi sama da ita, ta fara kokowar ƙwacewa tana kai duka.
"Zaki nutsu ko sai na kakkarya ki" yaya Aliyu ne ya tsare ta da ido.
"Dama abin da ta aiko ki kenan?" Ta yi shiru tare da sunkuyar da kai.
"wuce mu tafi, dage uwar faɗa"
Haka ta kwashi kwanukan, da yagaggen hijjabinta a hannu ya tasa ta a gaba, zuwa gida.
Mama na ganin ruma ta shigo tare da Aliyu, a yadda ta shigo kawai mama ta gane halin ta je ta gwada a waje.
"Damben ki ka je ki ka yi kenan ko, mara kintsi?"
Wage baki ruma tayi zata fara yiwa mama bayani, amma mama ta katseta ta ce "Ban tambayeki ba ruma, ki je ji yi tayi, bakin mutane kawai ya ishe ki"
Gefe ta koma ta zauna, tana jin yadda ba ta gamsu da dukan da ta yiwa Hauwwa ba, saboda dariyar da suka yi mata.
Yaya Umar ne ya fito daga ɗakin su, cikin wata dakakkiyar shadda dark blue, ya karya hula sai ƙamshi yake zubawa.
Tsuruu ruma ta yi da ido, tana jiran ya sauke mata masifa, tun da ya ji ance ta yi dambe.
Nufota ya yi, ita kuma ta ƙura masa ido ko ƙiftawa ba ta yi.
Ya kalleta ya ce "Na canza miki ne?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ka yi kyau ne"
Murmushi ya yi, ya miƙa mata leda ya ce "Je ki ka gwada wannan" da sauri ta tashi, ba tare da sanin meye a ciki ba ta karɓa ta shiga ɗaki.
Doguwar riga ce ta shadda kalar kayansa, da mayafi da sabon takalmi da yari da sarƙa.
Ko da ta saka ta fito ba ƙaramin kyau ta yi ba.
"Mama kin ganni, na yi kyau"
Aliyu ya ce "Saboda son kai, shine ku ka yi kaya iri ɗaya babu ko labari"
Cikin tsananin farin ciki ta ce "Yaya Ussy, kalleni dan Allah na yi kyau?"
"Eh to, babu laifi sai ki ka zama kamar budurwa, duk da ƙwaila ce".
Cikin tsananin farin ciki, ta faɗa jikin yaya Umar tana murna "Yaya na gode sosai, Allah ya saka maka da alkhairi ya sa ka gama da duniya lafiya"
Ganin yadda take murna ya sanya shi yin murmushi na gefen baki ya ce "Allah ya sa ki daina rashin ji".
"Iyee, lallai mai sunan Baba, ni sai ka haɗani da atamfa kala uku, amma kai da ƙanwarka ka yi muku kaya iri ɗaya, wato an fi son ta a kaina" mama tayi maganar cikin sigar wasa.
Murmushi ya yi, dan ya san halin mama da barkwanci wasu lokutan.
Mama ta shiga ɗaki, ta fito da wata ƙatuwar leda, ta miƙawa ruma ta ce "Gashi nan, ba dan halinki ba, kayayakin da suka yi miki ne, na wannan sallar naƙi nuna miki dan in hora ki"
Rikicewa ruma tayi, dama suna yi mata ɗinke-ɗinke, amma sallar bana bata san sun yi mata ba, dan a ƙalla ta tashi da kaya ku san dozen, banda hijjabai da abun hannu da sauransu.
"Wayyo Allahna, dama kuna so na haka? Duk nawa ne wannan mama kin ga fa duk nawa ne"
Gaba daya suka kewaye ta suna murmushi, ganin yadda ta rikice tana murna.
Bin su ta dinga yi ɗaya bayan ɗaya tana yi musu godiya, tana zuwa kan Huzaifa ya wani maze ya ce 'Kar ki damu, wannan fa bakomai bane ba, idan har zaki dinga biyayya".
"Ba zan yi biyayyar ba, na san ma ba uwar da ka saya mini, duk gidan nan waye ya kai ka talauci da son banza?"
"Laaaa, ke fa ba a abin arziki da ke ko?"
"A'a yi haƙuri mama, shi ɗin ne zai ɓata mini rai, yanzu a cigaba da zuzzuba tuwon ina kaiwa, amma wallahi duk in da na san ba za a bani kuɗi ba, sai dai Yasir ko Huzaifa su kai"
Haka tayi ta rabon Abinci cikin annashuwa, gidan da aka bata kuɗi tayi ta murna, idan ba a baya ba tayi ta jin haushi.
********
Ba zata iya ƙayyade rabonta da gidan nan ba, dan haka ta ɗaga kai take ta na kallon sauye-sauyen da aka yi a gidan.
Ya ƙawatu, duk da ginin yana nan a yadda yake, amma an yi wa gidan gyara sosai.
Da haka ta ƙarasa cikin ƙaton falon da ke cikin gidan.
Hadimai ne ke ta kaiwa suna komowa a cikin tangamemen falon, suna aikace-aikace.
Ɗaya daga cikin hadiman ce ta kalli Iman da fara'a ta ce "Maraba da zuwa".
Iman ta ce "Yauwwa sannunku da aiki, Ummma fa?".
"Tana cikin turaka, bari ayi miki iso"
Babu jimawa hadimar ta fito, ta kalli Iman ta ce "Bisimillah, ta ce ki shiga"
Bayan hadimar Iman ta bi, zuwa turakar Ummma.
Shigarsu ɗakin ke da wuya, gaban Iman ya faɗi, bisa tozali da mutanen da ba ta son ko haɗa hanya da su, ba dan jinin Ummma bane su, to tabbas da kai tsaye zata iya cewa mutanen da ba ta ƙauna.
Faɗaɗa murmushi Ummma tayi ta ce "Masha Allah, Iman dama talaka na ganinki?"
Murmushin yaƙe iman ta ƙaƙalo, ta durƙusa a kan gwiwoyinta tana gaida Ummma.
Cikin mutuntawa Ummma ta amaa mata, tare da tambayarta ya Ammi.
"Hajiya Iman, manya manyan 'ya'ya a gidan Galadima, ya kike ya school?" cewar wata matashiya da ke zaune a gefen Ummma.
Ko ba a gaya mata ba, ta san da biyu budurwar ta yi wannan maganar, ta dake ta ce "Lafiya lau Anty Soafy, an yi salla lafiya?"
"Hmm lafiya lau, irin wannan ado haka, Ummma wannan leshin kamar irin sa Khairiyya ta saka ranar kamunta ko?" Tayi maganar tana ƙarewa Iman kallo.
Umma ta ce "Eh irinsa ne"
"Wow, it worth 120k fa, lallai autar gidan Galadima, kin riƙe wuta".
Iman jin ta take tamkar a kan wuta, dan haka a gurguje ta ce "Ummma dama abincin salla ne, Ammi ta ce na kawo miki, kuma nazo mu gaisa, bari na tafi".
"Kai Iman tun da wur haka, ke dai ba kya son mutane, shikenan bari na baki barka da salla".
"A'a Umma, ai na girma da barka da salla" iman tayi maganar tana miƙewa .
"Ƙaniyarki, tsaya ki karɓa mana" girgiza kai iman tayi, ta fice daga ɗakin da sauri.
Har ta kai tsakiyar falon, ta ji an riƙe mata jaka.
Ta waiwayo tana kallon wadda ta riƙeta.
"Duk na san kin ci kin ta da kai, Ammi tana ji dake, na san kina da kuɗi baki rasa komai ba, amma yakamata ki karɓa tun da kin san baki da gado a cikin dukiyar gidan Galadima?"
Cikin rauni Iman ta ce "Anty Soafy me kuma ya kawo wannan maganar?"
Cikin ko in kula Soafy ta ce "Yau aka fara gaya miki irin wannan maganar ne, ai gara a dinga yi ana tuna miki, ko ba haka ba?" Ta fizgi jakar iman, ta saka mata kuɗin, ta saƙala mata jakar a kafaɗarta ta koma ciki.
Gwiwa a saɓule, iman ta nufi fita daga falon, tuni idanunta suka cika da hawaye, sai dai tana fitowa ya sha gabanta, ya ƙureta da idanuwansa.
Ƙoƙarin ratsewa take ta wuce, amma ya ce "Me ta ce miki ne, har ta saka ki kuka?"
Girgiza masa kai tayi alamar bakomai.
Yayi murmushin gefen baki ya ce "Anyway, kin yi kyau sosai a outfit ɗin nan, ashe yayanki yana Saudiyya babu ko sallama?".
"Uncle J, am sorry sauri nake, Ammi na jirana" daga haka ta wuce ta bar shi a wurin a tsaye.
**********
Zuwa yamma mama ta saka ruma a gaba sai sa ta cire shaddar nan, dan idan ta bar ruma da ita sai shaddar ta fita daga hayyacinta.
Kwanukan da aka ɓata, Yasir ya tattara yana wankewa, mama ta ce "Ke, shiga ɗakinsu ki dudduba mini idan da kwanukana, cokula ko kofi, duk ki fito mini da su, dan na san hali, sai a kai mini kwano ɗaki a ƙi fito da shi"
Ruma ta tashi ta nufi ɗakin samarin nan, ba tare da ko sallama ba.
Usman ne a kwance yana waya, kuma da alama da mace yake wayar.
Buɗe baki tayi, ta tsaya tana kallonsa. Zumbur ya tashi zaune, ya katse wayar ya ajiye ya haɗe rai ya ce "Zo nan" ba musu ta ƙarasa in da yake.
"Me ki ka ji?"
Ta ce "A ina?"
"Ina tambayarki kina tambayata? Nace me ki ka ji?"
"Wallahi ban ji komai ba, kawai dai na ji ka ce....." Sai kuma ta yi shiru.
"Ba zaki faɗa ba sai na taka ki?"
Ta tura baki sannan ta ce "Na ji ka ce, wai kwalliyar ta tayi kyau, kamar farin wata".
"Sai kuma me?"
"Shikenan na ji wallahi "
"To na rantse da girman Allah, idan ki ka sake ki ka faɗa, wallahi sai na yi miki dukan tsiya, ƙanwar abokina ce ba wata ba"
"To ai ni dama ban ce zan faɗa ba, mama ce ta aikoni" daga haka ta shiga duddubawa mama kwanukanta.
Aikuwa ruma ta fito da kwanuka a hannuta tana faɗin mama "Kin ga kofin ki, an sha fura a ciki sha zumamu ya siɗe miki kofi tas, har ɓera ya fara ci. Kin ga plate ɗin ki har da sauran alalar da ki ka yi tun sati biyu da suka wuce".
Yasir ya ce "To munafuka, uban waye ya saka ki wannan sharhin?"
Mama ta ce"Ai ba ƙarya ta yi ba, ku yi ta kwasar mini kwanuka kuna kaiwa ɗakin ku, sai na bi na tsinto abina, ƙazaman banza kawai"
Mama na tsaka da mitar sai ga Aliyu ya shigo, ya ce "Ina ruma"
Ta ce "Gani"
"Yo sauri, abokaina ne na filin ball suke tambayata kina ina, shi ne suka biyo ku gaisa, saura kiyi wani haukan da zaki zubar mini da mutunci ".
Murmushi ta yi ta ce"A'a ba zan zubar maka da mutunci ba, bari na sako gyalena"
Yana maganar ya fice, Huzaifa ya ce "Mama ke ba a zo gaishe ki ba, sai wannan yarinyar lallai ruma".
Ta fito daga ɗakin mama da sauri, ta kalli Huzaifa ta ce "Ka yi mini Addu6, Allah ya sa su bani kuɗi" tana gaya masa ta kwasa da gudu ta fita waje.
Da fari gaishe su tayi kamar nutsatsiya, suka amsa mata cikin mutuntawa.
"Ya makaranta ya rikici2?"
Ta ce "Makaranta lafiya ƙalau, amma ni bana rikici" suka din ga jan ruma da hira ita kuma tana zuba, Aliyu sai hararta yake amma ta cigaba da zuba.
Dariya suka dinga yi mata, suka babbata barka da salla, ko ɗan cewa ba zata karɓa ɗin nan ba tayi ba, zuruf ta miƙa hannu ta karɓe tana godiya.
Wani mugun kallo yake wa ruma, amma ko saurararsa ba tayi ba.
Ta duba a cikin kuɗin da aka bata, akwai ɗari biyu da ta tsufa sosai, ta kalli wanda ya bata ya ce "Ɗan uwanmu ɗan canza mini wannan, ba zata karɓu ba" buɗe baki Aliyu ya yi yana bin ruma da kallo.
Aikuwa ya karɓa ya canza mata wata, ta ce ta gode ta shige gida.
"Mama kin ga abokan yaya Aliyu sun bani, kuma sun ce suna gaishe ki"
Mama ta ce "To madalla"
"Mama gashi ki ajiye mini, ki ɗora da lissafi, idan kin manta ni ina sane da lissafin, dan Allah mama kar na zo karɓar kuɗina ki fara ce mini, abubuwan da ki ke mini ba da kuɗina ki ke yi mini ba, wallahi mama da za ayi lissafi ban san iya adadin kuɗin da nake bin ki ba"
Cikin gatse mama ta ce "To Anty ruma, ki zauna ki lissafa duk kuɗin da ki ke bina, na biyaki"
"Dan Allah mama da gaske ki ke?"
"Eh mana" murna ta dinga yi tana cewa 'Ai mama kuɗin da nake binki, sai ma zauna musamman na yi lissafi, tsaf sai na zama attajira da kuɗin nan, unguwar da muke zuwa a bani kuɗi ai da yawa"
Yasir ya ce "Ba zaki taɓa hankali ba".
Aliyu ne ya shigo rai a ɓace yana hararar ruma.
Kawar da kanta tayi gefe taƙi kallonsa.
"Dole ki kawar da kai mana, yarinyar nan ana bata kuɗi ta karɓe, wai har da cewa wai wata ba zata karɓu ba, da yake ke ki ka basu ajiya"
"Yaya ba kyau mayar da hannun kyauta baya fa"
"Zaki mini shiru, ko sai na mareki, mara kai kawai"
A ranta ta ce "Ohoo dai, tun da Allah ya sa na karɓa".
Bayan sallar isha'i yaya Umar ya dawo, duk sun daddawo suna gida, ana ta hira.
Ruma tayi gyaran murya, ta kalli Yaya Usman ta ce "Mama kin san me?"
Mama ta ce "A'a".
Usman ya zubo mata ido, kowa ya yi shiru yana sauraron wani shirmen zata faɗa.
Ayshercool
08081012243
(INCLUDE ME IN YOUR PRAYERS PLEASE 🙏)
[05/07, 5:40 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
P9
Wani irin kallo Usman yake mata, amma ta basar ta ce "Mama kin san me yaya Usman ya yi?"
Mama ta ce "A a sai kin faɗa"
Usman ya ce"Haka muka yi da ke ruma?"
"Oho ni dai bana munafurci da rashin gaskiya, duk abin da aka yi mama bata nan sai na gaya mata, ba zan ga ana ba dai-dai ba mama bata sani ba na yi shiru".
Kamar ya yi kuka ya ce"Amma haka muka yi da ke?"
Mama ta ce "Gaya mini ina jin ki"
Ruma ta kalli Usman ta ce "Sai dai ka yi haƙuri fa, amma wallahi sai na faɗa a gaban kowa da kowa, ba zan zuba ido ana abin da ba dai-dai ba"
Ba dan ya san idan ya yinƙura zai yi mata wani abu mama zata hana ba, da sai ya kife Ruma da mari, ya san idan ta ɗaga maganar nan akwai damuwa, zai sha faɗa da mita.
Uwa uba ga Yaya Umar a zaune a wurin, kuma ba shi da tabbacin iya abin da ruma ta gaya masa ta ji, shi kaɗai ɗin ta ji, dan kawai ɗaga kai ya yi ya ganta a tsaye lokacin da yake wayar.
Ta gyara zamanta sannan ta ce "Ɗazu, da ki ka aikeni kai tuwo gidan mai ƙuli, na ganshi a ƙofar gidan su wannan abokin nasa Yahaya, shi da abokansa sun dawo daga idi, ko gida ba su zo ba, ya zauna an fito da abinci sun haɗu suna ci, kuma kin hana hakan"
Ajiyar zuciya ya yi, yana hamdala da ba wancan zancen ta yi ba.
Mama ta ce "To wannan abun ne ki ke ta zuzutawa, ai shima ya zo ya ɗau abinci ya fita da shi sun ci tare"
"To mama sai aka ce ya je ya zauna a ƙofar gida yana cin abinci ai rashin kamun kai ne, kuma ke ki ka ce rashin kamun kai ne fa".
Mama ta ce "To shikenan, za a yi masa faɗa".
"To mama kiyi masa faɗan mana yanzu"
A fusace ya ce "Ke wai ni sa'an ki ne?"
Umar ya ce "Maganinku kenan da ku ke wasa da ita"
Can ta sake gyara zama ta kalli mama ta ce "Mama, kin san wani abu?"
"Ke na gaji da wannan shirmen naki fa" mama ta faɗa cikin ƙosawa.
"Mama ba shirme zan ba, ɗazu na ga Habiba a masallacin idi, da tsofaffin kaya na ganta".
"To ina ruwanki? Kin ga ina rabaki da sabgar munafurci amma ba zaki dai na ba ko?"
Jiki a sanyaye ruma ta girgiza kai ta ce "Mama so nake a bata kaya ɗaya a cikin kayana" gaba ɗaya juyowa suka yi suna kallon ta jin abin da ta ce.
Huzaifa ya ce "Kina da hankali kuwa?"
"Amma dai ka san tun da nake ni ba mahaukaciya ba ce ko? Mama dan Allah a bata ita ma ta saka sabon kaya"
"Rufewa mutane baki, mara zuciya nan babarta ta zo ta ciwa mutane mutunci, amma ki ka cigaba da shishshige mata, ba za a bayar ba ɗin" Aliyu ya faɗa yana zaro ido.
Mama ta girgiza masa kai, ta dubi ruma ta ce "Allah ya kaimu gobe, sai ki zaɓi wanda zaki batan"
Murmushi ruma ta yi ta ce "Na gode mama, Allah ya saka da alkhairi, to zaki ɗan zuba mini naman kazar ita ma na kai mata ta ci, na san su basu yanka kaza ba".
Yasir ya ce "Dama ta yaya zasu yanka, wannan babar ta su tana kiwon kaji kamar su kasheta, amma ba zata yanka su ci ba, bayan talauci har da son zuciya"
"Ka daina zagar mini babar ƙawa dan Allah"
Mama ta ce "Kin ga, tashi ki wuce ki je ki kwanta"
Ta miƙe ta shige ɗaki, mama ta mayar da idonta kan Aliyu ta ce "Aliyu, kar ku hora yarinyar nan a kan halin rowa, duk rashin jin ta tana da tausayi da son taimako, idan har abin da za ta yi bai saɓawa shari'a ba ku ƙyaleta"
Aliyu ya jinjina kai. Ruma kuwa ji take kamar ta janyo washegari, ta kai wa habiba wannan kayan, ita ma ta saka ta ji daɗi.
Washegari da wuri ruma ta yi wanka, ta yi kwalliyar salla da ɗaya daga cikin kayanta, ta zauna ta ɗaukarwa Habiba set ɗaya na atamfa har da ribbon da abin hannu.
Mama bata hanata ba, ta ƙulle mata nama ta bata ta kai wa Habiban.
Har zata ɗauka ta fita, ta tsaya ta ce "Mama, dan Allah idan ta yi kwalliyar zamu je gidan 'yan ajinmu mu yi wasa".
Mama ta ɗan ɓata fuska ta ce "Amma dai kin san babna son wannan abun ko, ba na son yawace-yawace"
Ta ɗan marairaice ta ce "Dan Allah mama, kin san bana yawo, daga aike sai makaranta, yanzu fa salla ce".
"Shikenan, na ji, saura kuma ki je ki zauna sai an nemo ki, ina da ina zaku je?"
Ruma ta lissafa mata, mama ta yi ajiyar zuciya ta ce"Yanzu ƙarfe goma da rabi, kar ki wuce sha biyu, idan ki ka wuce abin da zai zo biyo baya ba zai yi miki daɗi ba".
Cikin murna ta ce "Mama da wuri zan dawo in sha Allah " ta yi waje ta na murmushi.
Kai tsaye gidansu Habiba ta nufa, ko da ta je ta yi ta sallama, shiru ba a amsa ba.
Tsayawa ta yi a tsakar gidan ta cigaba da sallama.
Sani ne ya leƙo yana amsawa, yana ganin ruma yayi saroro ya ce "Ke uban me ki ka zo yi mana a gida?"
Hararsa ta yi ta ce "To ina ruwanka ai ba wurinka na zo ba, ba yayana yayi maka tsakani da ni ba, babu ni babu ba, ko kuma na kira shi, ya zo ya ƙara kumbura maka fuska"
Tana tsaka da maganar, sai ga babar Habiba ta fito daga banɗaki, tana ganin ruma ta tsuke fuska ta ce"Ke me ki ka zo yi mini a gida?"
"Gurin Habiba na zo"
"Da izinin wa ki ka zo wurin Habiban?"
Habiba ce ta fito daga ɗaki, hannunta riƙe da kwanon tuwo da miyar kuka, tana ganin ruma ta ce "Laaa ruma, kin dai na zuwa makarantar allo "
Ruma ta ce "Ba na ganki a masallacin idi ba ki ka ƙi kulani"
Habiba ta ce "Wallahi ruma ban ganki bane ba? Ya salla?"
"Lafiya lau, wurin ki na zo, zo ki ji?"
Mamaki ya cika babar su Habiba, ta riƙe haɓa ta ce "Habiba, wato cigaba da shiga sabgar yarinyar nan ki ka yi ko?"
Habiba ta girgiza kai ta ce "Wallahi Ummanmu ba kulata nake yi ba, na daɗe ma bamu haɗu ba".
Ruma ta miƙowa Habiba leda ta ce "Kawo miki na yi, ki zo ki karɓa ki gani"
Babu musu ta ƙarasa ta karɓi ledar, taga ɗinkakkiyar atamfa ga abin hannu da ribbon, sai kuma ƙullin nama.
Habiba ta ce "Ruma wannan na waye?"
"Naki ne, in gaya miki, kayan salla na kala goma sha biyu da hijjabai, har da abin hannu da sarƙa, shine na ce bari na kawo miki ɗaya, ki saka mu je yawon salla".
Babar su Habiba ta ce "Ba ta so ba zata karɓa ba, bana son shishshigi, ba ta kayanta ce muku aka yi tana buƙata? Ita ma tana da kayan salla"
Idon Habiba ya cika da hawaye ta ce "Wallahi Umma bani da kayan salla, ina son kayan dan Allah ki bar ni na saka".
Ruma ta ce "Dan Allah Umma ki bari ta saka, mun shirya ai mun dai na faɗa, dan Allah ki bari ta saka"
Umma ta kalli yadda Habiba ta rungume kaya tana kuka, wai tana so, haka ta ƙyaleta. Habiba ta shiga ɗaki ta saka kayan, aikuwa tamkar dan ita aka ɗinka su suka yi mata kyau.
Sani ya din ga ce wa habiba mara zuciya.
Abin ka da ƙuruciya, tuni habiba ta shirya a cikin kayan, duk da babar Habiba na jin haushin ruma, hakan bai hanata rawar jiki wurin raba naman kazar da ruma ta kawo ba, fan kuwa an daɗe ba a haɗu ba.
Daga haka suka fita nasu yawo.
Tamkar awakai haka suka dinga yawo, kusfa kusfa gidajen ƙawayensu, wasu a haɗu a rabu da su ƙalau, wasu kuma a ƙare da faɗa. Ruma ba ta tashi tuna kashedin mama ba, sai bayan azahar tana ta gararanbarta a gari.
A suwkane ta nufo gida, tana ta tunanin yadda za ta kare kanta a wurin mama, dan ta san zuwa yanzu ana can ana nemanta kamar kuɗin guziri.
Yaya Usman ta hango a tsaye a jikin wata mota, ya sha kwalliya, shi da abokansa, da alama fita za su yi.
Da gudu ta ƙarasa in da yake tsaye ta ce "Yaya ussy, me ka ke yi a nan?"
"Ban sani ba, wuce ki tafi gida, ki kai aiken da aka yi miki" abin da ya faɗa ne ya sanya ta fuskanci kamar mama ba ta neme ta ba, dan haka ta ce "Dan Allah ina zaka?".
"Zamu ɗan fita chilling ne"
"Meye chilling kuma?"
Ya haɗe rai ya ce "Cewa na yi fa ki tafi gida ko?"
"Dan Allah ka yi haƙuri, zan bika dan Allah"
"Ke wai ni sa'an wasanki ne? Ba zaki wuce ki tafi gida ba?"
Ta sake marairaice wa ta ce "Dan Allah Yaya"
Riƙe rigarsa tayi tana kallonsa kamar za ta yi kuka. Tunawa ya yi da haushin ƙin tafiya da ita zai iya sanyawa ta tona masa asiri.
Yayi ƙasa da murya ya ce "To ki je ki tambayo mama, idan ta yarda sai mu tafi"
"Wallahi na san idan na tafi, tafiya zaka yi"
"Shegiya sai ka ce mayya, idan na tafi da ke a ina zan saka ki motar ba space" yayi maganar a ƙule.
"Sai na zauna a cinyarka" duk yadda ya so ya yakice ruma, taƙi ta nace, gashi ya san zai sha kunya, idan har ruma ta tona masa asirin yana waya da budurwa, dan ya san sai dai ya kasheta bayan ta faɗa zare idonsa ba zai hanata faɗar abin da ta yi niyya ba.
Haka ya sakata a motar, dama ta abokinsu ce, ita kaɗai a cikin maza, sai zaginta yake, amma ko a jikinta, ya sakata a gefensa.
Abokansa sai dariya suke masa, suna "Ka ga Ƙanwar maza, suke mulkin amma dole a biki ko ba a so" ba wanda ta kula a cikinsu suka tafi.
Wurin shaƙatawa suka je, duk abin da suka ci sai da suka sayawa ruma ita ma ta ci, da ta ji ta ƙoshi ta kalli Usman ta ce "Yaya ussy, a samo leda a ɗaure mini sauran na tafi da shi gida"
"Saboda kowa ma bashi da hankali kamar ke? Wallahi baki isa ba" ba dan ya ji daɗin fitar ba, ya azalzali abokansa suka koma gida, saboda yadda ruman ke ta zubar masa da mutunci a idon abokansa.
Ko da suka je gida, mama a kiɗime take, tun sha biyu ake nemanta ba a ganta ba.
Bin su da kallo mama ta yi, ta dubi Usman ta ce "A ina ka ganota?"
"Nima a hanya na ganta bayan la'asar, zamu fita da abokaina, ta nace sai ta bini, na kira Aliyu a waya na gaya masa muka tafi da ita".
"Ku ka je ina?"
"Wurin wani cin abinci ne, ni da su Isma'il ne"
"Kuma ita kaɗai a cikin maza Usman, ka san tun yaushe yarinyar nan ba ta gidan nan, ka ga tashin hankalin da na shiga kuwa? Wallahi yau sai kin ci ubanki"
Abdallah ya ce "Wallahi mama ko ba ki daketa ba, sai na zaneta yau, ki yi mata bugun shekararriyar dawa, yarinyar nan ta ci a bata gado a Asibitin mahaukata".
Mama a tsananin fusace ta janyo ruma, ta din ga turjewa tana ihu, mama ta zaro bulugari ta dinga bugunta da shi tana kurma ihu tana neman taimako.
Mama ba ta saba tarbiyya da duka ba, amma idan ta kai bango jikin mutum yana gaya masa, sai da Usman ya ƙwaci ruma da ƙyar a hannun mama.
Tun daga ranar, mama ta ce ba zata bata sauran kayan sallar baz gashi an aiko mata da kayan salla daga can garin su, ga dangin mahaifin su ma, sun ɗinko mata kaya, sun aiko mata da su, duk mama ta ce ba zata sake sakawa ba ta gama kwalliyar salla.
Washegari ta na ji ta na gani mama ta shirya, ta tafi cikin gari, ta bar ruma a gida.
Gidan duk ya yi mata babu daɗi, sai faɗace-faɗace take da su Yasir.
Suka gama suka fice suka bar ta a gidan. Ta ji babu daɗi rashin tafiya da ita da mama ba ta yi ba, gaji da zama ta tashi tana neman abun yi.
Ɗakin 'yan mazan ta shiga, ta fara gyara musu ta ci karo da shaddar yaya Umar ya saƙaleta.
Wani tunani ta yi, ta kwaso shaddar ta fito da ita tsakar gida. Ta zuba ruwa a bokiti ta tuttula omo ta zunduma shaddar nan a ciki, ta koma ta cigaba aikin gyaran ɗakin.
A ƙalla shaddar nan ta kai awa biyu a ruwa, ruma ta fito ta jagwalgwala ta shanya. Ai kuwa shaddar nan gaba ɗaya ta daina wannan shining ɗin da take yi saboda azabar omo.
Aka jima, ya haɗa wuta a dutsen guga, ta hau goge masa ita.
Abdallah ne ya dawo, ya tarar da ruma ta duƙufa tana guga.
Ya tsaya yana ƙoƙarin gane me take gogewa.
"Wai meye wannan ki ke gogewa haka?"
Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Kayan yaya Umar ne, na ga ya saƙale su a ɗaki, na san wankewa zai yi, shi ne na wanke masa nake goge masa".
Abdallah ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ruma da me ki ka wanke shaddar nan haka?"
"To za ayi wanki ba da ruwa da omo bane?"
"Uban waye ya ce miki ana wanke shadda da omo?" Ai suna cikin maganar ruma ta ƙone gaban rigar.
Dafe kai ta yi ta ce "Innalillahi, na shiga uku, Abdallah ya zan yi na ƙona masa shadda?"
Abdallah ya ce "Maganinki shegen karambani, kya san mai zaki gaya masa"
Hannu ruma ta ɗora a ka ta dinga kuka, dan ta san yau kashinta ya bushe, sai yadda Allah ya yi da ita.
Haka mama ta dawo ta tarar da ita, tana ta uban kuka, Abdallah ya gaya mata abin da ta aikata.
Cikin kuka ruma ta ce "Dan Allah mama ki bashi haƙuri, yau na san na mutu wallahi, dan Allah mama kar ki bari ya dakeni ko ya saka ni punishing".
"Ba ruwana, ai nima ba jin maganata ki ke yi ba".
Abu kamar wasa, har bayan la'asar ruma ba ta ci ko Abincin rana ba, sai kuka take yi.
Huzaifa ya ce "Ni ne mutum na farko da zai sanar da mai sunan Baba wannan taɓargaza da ki ka aikata masa"
Duk da mama a ƙule take da ita a kan laifin da ta yi mata jiya, amma hakan bai hanata saka ruma ta ci abinci ba, amma ruma taƙi ci sai aikin kuka. Ita kanta mama na tausayawa ruma hukuncin da zata fuskanta a wurin Umar idan ya dawo ya tarar da ɓarna da ta aikata masa, sai dai ita ta janyo kanta, rashin jin ta ya yi yawa.
Mai sunan Baba bai dawo ba sai bayan sallar magariba, tun da ya shigo ta sake takurewa tana uban kuka.
Ya dube ta, cikin kakkausar muryarsa ya ce "Kukan me ki ke yi?"
Huzaifa ya gyara zama, ya wassafa masa ɓarnar da ta aikata.
Duk da babu isasshen haske a tsakar gidan, ta tsorata da kallon da ya yi mata.
"Dan Allah yaya ka yi haƙuri, ba a son raina na aikata hakan ba, wallahi kawai niyyata na baka mamaki, na wanke maka na goge maka ban san haka abin zai zama ba"
Kalmar ta bashi mamaki sai da ta saka Aliyu dariya, ya ce "Lallai kin bashi mamaki kam"
Yadda ta firgice ne, ya sanya Yasir ya ce "Dan Allah yaya ka yi haƙuri, kuskure ne, tun da tsautsayin nan ya faru ba ta ci Abinci ba"
"Zaka ɗau hukuncin da zan yi mata kenan?" Yayi maganar ba tare da ya kalli Yasir ba.
Yasir ya ce "Eh ni ka hukunta ni a madadinta, a tsorace take"
A ɗan tsawace ya ce "Tashi ki ɗauko mini kayan na gani"
Sumi-sumi ta tashi ta je ta ɗauko kayan, ta miƙa masa.
Ya karɓa ya duba, gaba ɗaya kayan sun tashi daga aiki, jikinta sai rawa yake yi.
"Tun da ki ke na taɓa saka ki wanki?" Ta girgiza kai.
"To Meyasa ki ka wanke nawa kayan?"
"So nake nima na yi abin arziki, ban zaci zai zama na tsiya ba"
Ya girgiza kai ya ce "Zubo mini Abinci" ta tashi tana ta tsuma, ta je ta zubo abinci ta kawo masa tana kallonsa.
Ya karɓi Abincin, ya ajiye a gabanta ya ce "Ci Abinci"
Fuska duk hawaye ta ce "Dan Allah ba zaka saka ni kama kunne ba?"
Ya girgiza mata kai ya ce "Ba zan saka ki ba" yayi maganar yana ɗebo Abincin ya kai bakinta.
"To ka haƙura?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
"To dan Allah ka yi haƙuri, tsautsayi ne"
"To, ci abinci" sai a lokacin ta ji ranta ya yi sanyi, har ta fara cin abinci, babu wanda bai yi mamakin yadda mai sunan Baba ya ƙyale ruma ba, basu taɓa kawo zai rabu da ita ba.
Sai da ta ci ta ƙoshi sannan ta ce "Me sunan Baba"
"Na'am"
'Dan Allah ka yi haƙuri, zan karɓi kuɗina na wurin mama sai na saya maka wata "murmushin gefen baki ya yi ya ce 'To Shikenan".
Bayan yaya Umar ya fita, Huzaifa ya lallaɓa ya bi ruma ɗaki yana cewa "Ruma, wace addu'a ki ka yiwa mai sunan Baba ya ƙyale ki ne? Zo ki gaya mini"
Usman ya ce "Wallahi nima na yi mamaki duk ɓarnar nan da ta yi masa ya ƙyaleta"
Babu wanda ta kula a cikinsu ta kwanta tana yiwa Allah godiya.
Hidindimun Salla suka wuce, aka koma makaranta, ruma ta koma makaranta, sai dai fafur ta ƙi zaman ajinsu, wai malaminsu baya son ta, wani malam Habibu ɗan mai makarantar ta liƙewa, duk ajin da za shi ya yi ƙari sai ta bishi, gashi ta maƙalewa Auwal, yaya sama yaya ƙasa haka take kiransa saboda yana sayen tsami gaye da goriba ya bata.
Yanzu ma 'yan ajin su Yasir suna jiran malam Habibu ya zo yayi musu ƙarin Alqur'ani, sai ga shi ya shigo shi da ruma.
Yasir yana ganinta ya tsuke fuska, dan tun wancan hansfreen da ta yi masa a gida, ya hanata zuwa ajinsu, amma sai gata.
Malam Habibu ya zauna, ya ce ta shiga cikin mata ta zauna. Aikuwa ta shiga ta zauna, ta nutsu kamar gaske aka yi ƙarin nan aka idar.
Aka zo kowa yana biyawa, aka zo kan Yasir shi ma ya biya, sai cewa ta yi 'Inyee ashe ka na ja, hmm da ba ka iya ba wallahi da sai na faɗa a gida, in ce kai ma baka iya karatu ba"
Dariya 'yan ajin suka hau yi suna kallon Yasir, ya sunkuyar da kai yayi mata shiru.
Kowa ya gama biyawa, ruma ta ce "Malam nima zan karanta"
Ya ce "To bisimillah"
Abun mamaki sai ga ruma ta karanta shafi guda, duk da tana yi ana cin gyaranta, amma ta kai shafi guda, ba ƙaramin mamaki ta bawa Yasir ba, yarinyar da ta ce ita gejinta aya biyu kawai.
Ɗari biyar malam Habibu ya bata, tare da jinjina mata, dan babu wanda bai san ruma ba ta ja ba.
Da ya kammala ƙarin ya ce ta ta so su tafi, amma ta kalli yadda Yasir ya haɗe rai ta ce "Malam ni ka bar ni a nan ajin"
Malam Habibu ya ce "To shikenan, duk malamin da ya zo ace masa ruma ajiyata ce, sanna ba ruwan kowa da ita kar a takura mata"
Suka ce to.
Yasir kuwa kamar ya zo ya rufeta da duka, dan ba zata taɓa zama shiru ba.
Ruma ta shige cikin 'yan mata, suna hirarsu, ita kuma tana shan farar ƙasarta, amma duk tana jin me suke faɗa.
Yau har aka tashi tana ajin su Yasir, sai da aka tashi ta bar ajin.
Ta je ta samu tsohuwar da take sayar da kayan yara a a ƙofar makarantar, ya titsiyeta wai sai ta bata farar ƙasa kyauta.
Duk shegen son kuɗi irin na iya, sai da ta bawa ruma farar ƙasarar nan, saboda shegen surutun ta da nacin tsiya.
Ta karɓi farar ƙasarta ta yi gida, haryanzu makarantar nan ba ta da ƙawaye, a cewarta ɗaliban ba su yi mata ba, kuma ba komai bane su ɗaliban sa'aninta kowanne ya mayar da hankali a kan karatunsa ne, ita kuwa ruma 'yar abi yarima a sha kiɗa ce.
Tun da ta je gida take tafa hannu tana masifa, "Wallahi an mini laifi a gidan nan, kuma sai kowa ya hallara zan faɗi me aka yi mini" jin kowa ya shareta ya ƙi kulata ya sanya ta ce "Mama yanzu dan Allah abin da ake yi mini a gidan nan ya dace?"
"Da aka yi miki me?"
"Mama a gabanki 'ya'yanki suke ce mini ƙwaila, amma baki taɓa hana su ba"
Mama ta dubeta ta yi murmushi cikin manyance ta ce "To ba ƙwailar bace ba?"
Ruma ta buɗe baki ta ce "Au mama har da ke?"
Aliyu ya ce "To meye dan an ce miki ƙwaila, ai ƙwailar ce"
Ruma ta ce "Kutt, ƙwaila fa wadda ba ta da nono kenan?"
Aliyu ya ce "Innalillahi wannan gingimemiyar maganar fa"
Mama ta ce "ke waye ya gaya miki haka?"
"'yan ajin su Yasir ne suke faɗa, matan nan ina jin su da kunnen nan nawa, sun zaci bana jin su"
Mama ta ce "To ke nonon ne da ke da ba za ace miki ƙwaila ba?"
"Mama gori dai ake yi mini kenan? Sai in je wurin Mai furar nan na bakin hanya, na sayo nonon, na zo na ƙulla a leda na dinga sakawa" cike da takaici mama take bin ruma da kallo, ta ma rasa me zata ce mata. Usman yana tsakar gida, sai ƙyaƙyata dariya yake ƙasa-ƙasa lamarin ƙanwar nan ta su sai Addu'a kawai.
Aliyu ya ce"Ke da ki ke ƙanwar maza, me zaki yi da wannan abun? Ki yi zamanki a haka ai sai kin fi kyau"
Ta ce "Kuma fa haka ne" ta cire rigar islamiyyar, daga ita sai vest, ta sinsina rigar ta kuma cewa "Mama, dan Allah yaushe zan fara warin hammata, ina son idan na cire riga na sansana na ji tana ɗan warin nan da ƙamashin turare "
"Fitar mini daga ɗaki dan ubanki, shashasha mara alƙibla fita ki bar mini ɗaki".
AYSHERCOOL
08081012143
[08/07, 4:58 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
*A TAIMAKA AYI SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA NA COOL HAUSA NOVELS, KO IN KOMA POSTING SAU ƊAYA A SATI 😒*
10
Ɗan tsayawa ruma ta yi tana kallon mama, cikin sangarta ta ce "Mama wai me na yi to?"
"Ban sani ba fitar mini daga ɗaki, mara kan gado, ni ba dan a gida na haifeki ba, cewa zan yi an canza mini 'ya, idan an yi gabas sai ki arta ki yi arewa, me ake da wani wari ban da rashin kan gado irin naki?"
Tsayawa ruma tayi tana kallon mama tana wasa da gashin kanta.
"Ba zaki fita ki bar mini ɗaki ba, sai na taso kan ki?"
Fitar ta tsakar gida yayi dai-dai da shigowar Yasir, da shi da Huzaifa.
Yasir ya aika mata da wani irin mugun kallo ya ce "Me na ce miki game da zuwa Ajinmu?"
Ta murguɗa baki ta ce "Ni wurinka na zo, ai ba wurinka na zo ba, ni da malam Habibu muka zo"
"To uban me ya hana ki je ajin su Huzaifa?"
Huzaifa ya yi caraf ya ce "Wallahi ta zo mana aji, sai na mata dukan tsiya, ta zo ɗin ta gani"
Hararsu ta dinga yi, tana cewa wallahi sai ta je.
Bayan Huzaifa ya canza kaya, ya shiga ɗakin mama ya ɗau jakarta.
Ruma ta ɗaga murya ta ce "Mama, ga Huzaifa nan ya ɗaukar miki jaka"
Ya ce "To munafuka"
"Wallahi ni ba munafuka ba ce, mama Huzaifa zai satar miki kuɗi"
Huzaifa ya ce "Mama aron naira ɗari zan ɗauka"
Mama ta ce "Ajiye mini jakata, ba zan baka aron ba, idan ka ɗaukar mini kuɗi ba bani ka ke ba"
"Dan Allah mama ki bani, zan baki wallahi"
Daga kitchen mama ta ce "Ba zaka ajiye mini jaka ba sai na zo ɗakin nan?"
"Mama wallahi bai ajiye miki ba"
A fusace Huzaifa ya ajiye jakara, yana yiwa ruma kallon banza, kamar ya kai mata duka haka ya fice.
Ruma ta ce "Dana sani na bar shi ya ɗauka, nawa nake bin mama ba biyana take ba"
***
Yau za a rufe makarantar su ruma a tafi hutu, yau za ayi spelling B da aka bawa su ruma.
Sai bin malaminsu take tana ce masa ita fa sai an sakata a cikin masu spelling B.
Malamin ya ce "Ki kwantar da hankalinki, zamu san yadda za ayi".
Azabar nacin ruma sai da ya sanya aka sakata a cikin masu spelling B, amma aka ce kar ta yi magana.
Ƙarshe dai ruma ce ta taimaki 'yan ajinsu, gaba ɗaya kalmomin nan babu wanda ba ta haddace ba, ruma ta bawa malaman makarantar su da ɗaliabai mamaki, dan ko bata takardar da aka yi, tsabar naci ne ya sanya a ka bata.
Ai kuwa ruma ta samu kyaututtuka sosai, karo na biyu a rayuwarta, da ta samu wani abun arziki a saboda harkar karatu.
Aka bata litattafai kaya guda, da kayan koyon karatu.
Ruma baki har kunne ta je gida, mama ta ganta da kaya niƙi-niƙi.
"Ke wannan kayan na menene?"
Ruma ta zubewa mama kayan ta ce "Mama, duk nawa ne a makaranta aka bani"
"Meyasa aka baki?"
"Wannan takardar da aka bani ce a makaranta, kowa ya ƙi koya mini, na je na yi ta yi da kaina, shine fa aka yi yau na samu wannan kyautar"
Mama ta ce "Hmm, ai shikenan"
"Mama wai na ga kamar ba ki yadda da bayanin da na yi miki bane?"
"Eh to kusan hakan, dan abin da kamar wuya gurguwa da auren nesa"
Cikin rashin fahimta ruma ta ce "Mama wace gurguwar kuma?"
Cikin gajiya da halin ruma mama ta ce "Ki tashi ki cire uniform ki yi wanka"
Ruma ta tashi ta cire kayanta, ta ɗebi ruwa ta shiga wanka. Ta na tsaka da wankan, ta jiyo muryar Usman ya shigo, daga banɗakin ta buɗe murya ta ce "Yaya Usyy Albishirin ka"
"Ruma ban hanaki surutu a banɗaki ba?"
Ta ce 'yi haƙuri mama"
Ba dan ta gama wankan ba, cikin zumuɗi ta fito daga wankan 'Yaya usman, bari na nuna maka wani abun mamaki"
Ba ta san a ya ta fito daga banɗakin ba, sai da mama ta daka mata tsawa, daga ita sai pant ta fito. Ta koma ta ɗauko zani, sannan ta kwaso kyaututtukanta ta nunawa Usman.
Ya kalli ruma sannan ya kalli kayan ya ce "Ruma ban yarda da ke ba"
Ta ce "Saboda me?"
"Ina ki ka ga kwanyar da zaki yi wani abun arziki ke?" Tsuke fuska ta yi tana kallonsa ta ce "To me ka ke nufi?"
"Ɗauko takardar da aka baki, na yi miki tambayoyi" ta miƙe ta je ta ɗauko masa takardar ta miƙa masa.
Ga mamakinsa duk abin da ya tambayi ruma, sai ta bashi amsa daidai ko gyaranta ba ya ci.
Ya ajiye takardar, ya kalli ruma ya ce "Ni fa haryanzu mamaki nake, matar da take zuwa ta kusa da ta ƙarshen aji, ita ta yi wannan ƙoƙarin"
Ruma ta yi murmushi sannan ta ce "Ikon Allah kenan, baku san haushin da nake ji idan aka ce mini daƙiƙiya ba, shi ya sa na dage na je na iya"
"Congratulations, ina ma zaki cigaba da dagewa da kin ga cigaba a rayuwarki"
Ta taɓe baki ta ce "A'a da wahala gaskiya, ka san baƙar wahalar da na sha kan na iya wannan abun, dan a dai na ce mini daƙiƙiya daga wannan ba zan kuma ɗaukar dala ba gammo ba"
Usman ya yi murmushi ya dafa kafaɗarta ya ce "Haba ƘANWAR MAZA, rayuwa ce fa, kuma idan da rai da lafiya yanzu aka fara, kar ki sake ɗarsawa ranki cewa akwai wani abu da zai gagareki komai wahalar sa, rayuwa sai da gwagwarmaya da faɗi tashi, musamman ga ɗan talaka. Kar wani abu ya ƙara razana ki, ko ki yadda ke daƙiƙiya ce zaki iya komai kema"
Ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce "Dan Allah da gaske Yaya Ussy?"
Ya jinjina mata kai ya ce "Sosai makuwa, ki dubi rayuwarmu a cikin gidan nan, tun baki da wayo, har zuwa yanzu a cikin gwagwarmaya muke, farincikinmu kawai ki ke gani, amma kowa akwai kalar ƙalubalen da yake fuskanta, ki kalli mama ba ta yi karatu mai zurfi ba, amma ta cancanci a kirata jarumar uwa, ba lallai ki fuskanci me nake nufi ba a yanzu, amma ki saka maganganun nan a ranki akwai ranar da za su yi miki amfani. Amma ki tsaya a kan ƙafafuwanki, ki fuskanci abin da yake baki tsoro, ke fa jaruma ce, bai kamata sunan daƙiƙiya ya biki ba"
Ruma ta ɗan yi shiru sannan ta kalli Usman ta ce "Yaya Usy, in sha Allah zan dinga mayar da hankali na yi karatu sosai na daina wasa"
"Yauwwa ko ke fa, ai hakan ya fi deluwa"
"Kuma zan cigaba da ƙoƙari, in zama mai ƙarfi sosai, duk wanda ya tsokane ni, in yi masa dukan tsiya in farfasa masa baki da hanci, in kakkarya mutum"
Mama da take jin su ta ce "Ke kuma ba kya fatan ki girma ki yi hankali, sai rashin hankali ke ba kya fatan Allah ya shiryeki ki daina faɗace-faɗacen banzan man a matsayinki na mace, faɗa ba na 'ya mace bane"
Ruma ta ce "A'a mama, gara ki bar ni na koyi ƙarfi sosai"
"Sai kuma ki yi ai".
Usman ya kuma murmusawa ya ce "Ba irin wannan ƙarfin ake magana ba, ƙarfin zuciya da kaifin basira wurin sarrafa duk wata Matsala da za ta tinkaro ki, kar ki bari matsalolin ki su razana ki, ko sau ɗaya kar ki bada wannan damar, ki turje ki dake ƙalubale duk girmansa, ki yi gaba da gaba da shi"
Ruma ta ce "Mhmm, gashi dai hausa ka ke yi, amma bana gane me ka ke faɗa, sai na ji kamar ma wani yaren ka ke daban, ban wani gane me ka ke nufi ba"
"Ni ma na san ba zaki gane a yanzu ba shekarunki da hankalinki babu lallai ya kai, saboda ke a yanzu ba ki sa wata damuwa ko matsala. Tashi ki zubo mana Abinci mu ci" Ruma ta miƙe ta tafi kitchen.
Mama ta ce "Kai ma banda abinka, wannan zaka zaunar ka na wani gayawa wannan bayanan, me zata gane a ciki? Ita ban da wautarta da tambayoyin ta na rashin kan gado me ta sani?"
Usman ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Haka kurum mama ina jin tausayin yarinyar nan, jikina na bani za ta yi gwagwarmaya a rayuwa, gwagwarmaya a bugiren da ba zamu iya tsaya mata ba, ko yi mata wani taimako ba, gwagwarmayar da take buƙatar ta tsaya da ƙafarta ta cimma nasara"
Mama ta ce "Tooo ikon Allah, to koma dai menene, ni dai addu'a kullum cikin yi muku ita nake, ba ku kaɗai ba, dukkan 'ya'yan muslmai baki daya, Ubangiji Allah ya shiga lamarinku, ya tsare gabanku da bayanku, ya kula da rayuwar ku"
"Amin mama, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana uwa ma bada mama"
"Amin ya rabb"
A ranar duk wanda ya shigo, sai ruma ta nuna masa kyaututtukan da aka bata, har a waya sai da aka kira mata yaya Abubakar ta gaya masa, tun ana tayata murna da Allah ya sanya albarka har ta fara ƙular da mutanen gidan. Dan hatta maƙwabta sai da ta shiga ta gaya musu ai tayi ƙoƙari a makaranta an bata kyauta.
Da ta je Islamiyya kuwa, har ofishin shugaban makaranta ta je, shi ma ta gaya masa, ya tayata murna tare da sanya mata albarka, ta ƙarasa staff room bayan sun gaisa da malaman suma ta gaya musu ai a makarantar boko tayi ƙoƙari an bata kyaututtuka. Nan suka yi ta mata fatan alkhairi, ji take a duniya yau ta ƙure daɗi tayi abin da ba ta taɓa ba.
"Malam to idan an idar da salla dan Allah a sanar"
Wani malami ya kalleta ya ce "A sanar da me?"
"Na yi ƙoƙari a makarantar boko mana, har na ciyo kyauta, word kusan ɗari biyu da hamsin fa na haddace yadda ake spelling ɗin su"
"To amma ai nan ba makarantar boko ba ce ba, ki bari idan ki ka yi bajinta a nan ma, sai a sanar wa ɗalibai"
Ruma ta ce "A'a malam gara ai a sanar, saboda masu ce mini daƙiƙiya su san ƙwaƙwalwata na aiki, wataran zan bayar da mamaki".
Malam Habibu ya yi caraf ya ce "Ƙwarai kuwa, dole a sanar da ɗalibai wannan namijin ƙoƙari da ki ka yi, nima ba rannan na yi ƙari kin iya ba, duk za a sanar kar ki damu" cikin jin daɗi ruma ta ce "Yauwwa malam na gode"
Bayan tafiyarta ya yi dariya ya ce "Yanzu idan ba ku yi yadda take so ba, Allah kaɗai ya san wace tijarar zata yu, amma yanzu idan aka faɗa ɗin, za ta ji daɗi da ƙara samun ƙwarin gwiwa".
Ruma da ta ga an idar da salla, ana neman a watse ba a sanar ba, ta tafi ƙofar masallacin maza, ta leƙa ta ce "Malam Habibu kar ka manta fa, na ji ba a faɗa ba".
Malam Habibu ya ce "To bari a sanar, ai yakamata wannan abin arziki haka"
Haka malam Habibu ya tashi ya ce "'yan uwa ɗalibai da malamai, a taya 'yar uwa murna, wato 'ya ta rumaisa, bisa nasara da ta yi a wata gasa da aka shirya a makarantar bokon su, har ta samu kyaututtuka dan Allah ayi mata Addu'a, Allah ya ƙaro nasarori"
Daɗi kamar ya kashe ruma, masu dariya na yi, masu jin haushi na yi.
Huzaifa da suka yi salla sahu ɗaya da Yasir ya ce "Ka ji abin da wannan mara kan gadon ta yi ko?"
"Bar motsatsiya, suma malaman da suka biye mata, idan ba tayi wasa ba sai na ƙona banzayen litattafan da aka bata, kowa ma ya huta".
Cike da annashuwa ruma ta tafi gida, ta je ta bawa mama labarin yau har a wurin salla, aka sanar da ta ci kyauta a makarantar boko. Tana shiga gidan ta tarar da Yaya Abubakar ya zo hutu, da kuma waa dattijuwar mata a zaune a tsakar gida.
Da sauri ruma ta nufi dattijuwar ta faɗa jikinta ta ce "Gwaggo Atine, yaushe rabon da na ganki?"
Dattijuwar ta washe baki ta ce "Dama ina zaki ganni, nayi-nayi da babarki ta din ga kai mini ke ina ganinki, amma ta ƙi saboda ina ƙauye".
Mama ta ce "Haba Yaya Atine, wallahi ba haka bane ba, kin san yanayin makaranta kuma ruma ba ta ji idan aka kai miki ita sai ta gallabe ku"
Ruma ta haye kan cinyar matar cikin jin daɗi ta zauna.
Matar ta ɗora da cewa "Ba wani rashin ji, a kawo mini ita a hakan ina son ta, duk rashin jin ta. Ɗan uwana ya ƙallafa rai a kan ta yana son ta, nima ina matuƙar ƙaunarta da na ganta shi nake tunawa amma ba za a kawo mini ita ba, sai wannan ƙartin ne kawai suke zuwa in da nake" ta yi maganar tana fashewa da kuka.
Mama cewa take "Allah ya baki haƙuri, in Allah ya yarda za a dinga kawota".
Ruma kuwa ta kalli Gwaggo ta ƙyal-ƙyale da dariya ta ce "Dan Allah Gwaggo ki daina wannan kukan, ni wallahi fuskarki dariya take bani idan ki na yi, kin ga yadda ki ke yamutsa kuwa?"
Yaya Aliyu ya ce "Ai gara ta fara gwada miki halin"
Gwaggo ta tsaya da kukan ta ce "Rumaisatu, kukan nawa ne yake baki dariya?"
Ruma ta ce "Eh mana, amma ki daina ce mini wata rumaisatu, sai ka ce wata masara, kowa aka saka masa suna mai daɗi a gidan nan, amma aka saka mini wata Rumaisa kamar masa"
Gwaggo ta jinjina kai ta ce "Ikon Allah"
"Gwaggo wai ina wannan 'yar ta ki, mai kamar ni ɗin nan?"
Jin ruma ta tambayi 'yar autarta ya sanya Gwaggo yin murmushi ta ce "Au Lawisa tana nan ƙalau, ta na ta a gaishe ki, ita ana biki sun tafi da tuni tare zamu zo"
Ruma ta yi dariya ta ce "Wai Lawisa, ai har gara nawa sunan ma da nata, wata lawisa kamar za ace lawashi, ta fini girma yanzu?"
"A'a zaku yi tsayi ɗaya da ita"
Ruma ta yi murmushi tana kaɗa ƙafa.
Abubakar ya ce "Ruma ɗaga mata ƙafa mana"
"A'a ƙyaleta, ai haryanzu yarinya ce, Allah dai ya kai ni auranku ke da Lawisa"
Ruma ta ce "Amin, ki yi mini Addu'a, Allah ya sa na yi tsawo na isa aure, kuma Allah ya sa na auri kyakykyawa mai kuɗi sosai"
Mama ta riƙe haɓa ta ce "Ruma, ƙanƙanuwarki da ke, har kin san wani miji mai kyau mai kuɗi?".
Gwaggo ta ce wa mama "Wai ke ina ruwanki da mu ne, muna hira kina saka mana baki" ta mayar da hankali kan ruma ta ce "Amin 'yar albarka, Allah ya kai ki in da zaki huta, mu ci mu sha mu yi wadaƙa".
"Amin, kuma Allah ya sa na auri me kyau".
Aliyu ya ce"Da wannan shegen hancin naki kamar na aladae zaki auri me kyau?"
Gwaggo ta ce "Ƙarya ka ke dan ubanka, wallahi kamar ta ɗaya da babanku, kuma hanci ne da shi har baka, in Allah ya yarda sirikina kyakykyawa ne kuma mai abin hannu, tun da 'ya ta ba daga nan ba"
"Gwaggo kin san wa nake so na aura?"
"A'a sai kin faɗa"
"Kina kallon wrestling?"
Gwaggo ta ce"A'a ni ban san shi ba"
'To ball fa?"
"Ni ina zan ga wannan shirmen"
Ruma ta ce "Da kina kallo, da na gaya miki wanda zan aura a cikin su".
Cikin son katse surutun da ruma ke yi ba kunya ba tsoro mama ta ce "Ruma tashi ki canza kaya, zan aike ki" ruma ta miƙe daga cinyar Gwaggo ta tafi sauya uniform.
Tun da Allah ya sa Gwaggo ta zo gidan nan, ruma taɓara ta ƙaru, don ko me ruma za ta yi ba zata bari a yi mata faɗa ba, gashi kullum cikin faɗa take da mai sunan Baba, dan kome za ta yi idan ruma tayi laifi hukunta ta yake yi.
"Wannan yaro da fuska kamar bajimin sa, ba ka da imani, wannan 'yar tatsitsiyar yarinyar guda nawa take, da zaka dinga azabtar da ita wallahi Hauwa wannan ɗan naki mugu ne"
Gaba ɗaya ruma da Gwaggo suka gallabi gidan nan, ruma kuwa aka samu tikitin rashin ji dan ma tana tsoron mai sunan Baba.
Yau Malam Habibu yana babban aji, ruma tana tare da shi, yayi musu ƙari, tana ta wasanninta da ciye-ciye, sai da ya kammala yana amsa tambayoyi sannan ruma ta ce "Malam ka ce idan mace tayi mafarkin namiji sai ta yi wanka zata yi salla, to ni kuma kullum sai na yi mafarkin yayyena, Kuma ni sai zan tafi makaranta nake wanka watarana kuma mama ta ce bana fita tayi mini wanka, to yan.....
Kan ta ƙarasa 'yan ajin suka hau dariya, dan ba zaka taɓa cewa hankalinta na kan abin da yake koyarwa ba.
Malam Habibu ya ce " 'ya ta ta kaina, ai wankan da mama take yi miki ya wadatar, duk ɗayane"
Ta ce "Au ho, na gane"
Tana dawowa daga islamiyya ta turke Abubakar ta ce "Yaya Sadik yau ka san meyafaru a makarantar islamiyya ?"
Sadik ya ce "A'a"
"Ka san na canza aji a islamiyya, saboda malaminmu baya ƙaunata, Ajin su Yasir kuma ya ce idan na ƙara zuwar musu aji sai ya dakeni, sai na koma ajin malam Habibu gaba ɗaya ajin 'yan sauka"
Abubakar ya ce "To ban da abinki kin taɓa ganin an fara gini daga roofing, ai daga tushe ake farawa"
"Oho dai koma yane, wani karatu aka yi nake son na tambayeka, da zan tambayi malam Habibu na manta"
"To ina jin ki"
" 'yan ajin ne da su da wasu na ga wataran ba sa salla fa, ko su ƙi zuwa da Alqur'ani izifi sittin wai Haila suke yi. Na tambayesu sai suka ce mini wai ai mata ba kullum suke salla ba, idan ba su yi salla ba haila suke yi ko biƙi. Aikuwa nima na ƙi yin salla, wata prefect ta ce me yasa ba na salla nima na ce biƙi nake"
Gwaggo da ta idar da salla ta ce "Subhanallahi" jin maganar ruman kamar saukar aradu.
Ita kuwa ko a jikinta, ta cigaba "Shi ne ta ce dan ubana ni na isa in yi biƙi, na ce ba dai ubana ba sai dai na ta, kuma tun da nima biƙi nake ba zan salla ba, ashe wataran mata ba sa salla amma ni kullum mama sai ta ce sai na yi"
Abubakar ya ce"To, wannan zancenku ne ke da maman ita zata baki amsa".
Ruma ta ce "Mama....."
Mama ta katseta ta hanyar cewa "Rufe mini baki, kar ki sake ki yi mini shirme, kuma ki tashi ki yi sallar da ki ka ce baki yi ba dan ubanki"
"To mama ai idan ana biƙi ba a salla"
"Biƙin ubanki, ke kin san meye biƙin ne?"
"To meye biƙin?"
"Ba zaki tashi ki yi sallar ba, sai na zane ki da bulugarin nan?"
Ta kalli Gwaggo ta ce "To ke gaya mini"
Kamar wadda ta tambayi meye wani babban zunubi Gwaggo ta ce "A'a ni babu ruwana, ga uwarki nan ta baki amsa ni zaki tambaya wannan babban al'amari ba a bakina ba, 'ya'yan binki wayewar ku ta yi yawa".
"Ohh ni ruma, komai na yi laifi ne, ai shikenan"
Tun daga lokacin ba ta kuma kula kowa ba, ta koma tayi shiru wai ita ta ji haushi.
Har zuwa sallar magariba, ba ta sake kula kowa ba, Gwaggo ma ta gaji da yi mata hirar, amma Ruma taƙi saurarata.
Yaya Sadik ne yayi gyaran murya ya ce "Ruma, wai ni kuwa idan kin girma me ki ke son ki zama ne? Da na je taron PTA ɗin ku an ce da kun shiga primary 6, za'a fara shirin common entrance, shi ne na ce idan kin shiga Sakandire me ki ke sha'awa Art zaki yi ko science?"
Ta kalle shi ta ce"Wai in din ga drawing?"
"Wane irin drawing kuma?"
"To ai ji na yi ka ce Art, Art ba drawing ba kenan?"
"A'a ba wannan ba"
"Ni dai kawai sana'ar da zan samu kuɗi nake so, ko kuma in zama 'yar sanda, in dinga tsayawa a titi ina bada hannu masu mota suna bani kuɗi, ko kuma a buɗe mini kanti, ko na zama mawaƙiya ko 'yar film!"
Ayshercool
08081012143
A TAIMAKA AYI SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA NA COOL HAUSA NOVELS, KO IN KOMA POSTING SAU ƊAYA A SATI 😒*
[11/07, 4:25 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
P11
Girgiza kai kawai Abubakar ya yi, ya ja bakinsa ya tsuke.
"Yaya ya na ji kuma kayi shiru?"
"To ruma ba dole na yi shiru ba, kowa yana nemawa kansa mafita a rayuwa, amma ke in da ki ka dosa daban?"
"To wai me na faɗa ba dai-dai ba?"
"Yanzu ke tsakanin ki da Allah, kin taɓa ganin mace a titi tana bada hannu a ƙasar hausa?"
Ta ɗan yi shiru sannan ta girgiza masa kai ta ce "A'a, to mawaƙiya fa ko film?"
Abubakar ya ce "Ba kushe sana'ar wani zan yi ba, amma ki yi tunanin wani abun daban"
"To ba sai a buɗe mini kanti ba"
"Yanzu a unguwar nan gaya mini shagunan da ki ka ga mata ne a ciki suke sayar da abu?"
Ta yi farat ta ce "Ga maman Olu beyerabiya"
"To ke bayerabiya ce?"
"A'a amma dai....."
"Kin ga, ya isa haka, dama ni a kan career ki nake magana, tun da baki gane me nake nufi ba shikenan" ita sam ba ta ga aibun abin da ta ce tana so ba, dan haka ko a jikinta ta share.
Gwaggo ta fara shirin tafiya, su Yasir suna ta murna, dan dama duk ta ishe su da faɗa da azabar saka ido.
Shi kansa mai sunan Baba murna yake ta tattara ta tafi ta bar musu gida su huta, dan ta saka shi a gaba da yawa, dan ma Allah ya taimaki Abubakar bai fi sati ba ya koma makaranta.
Amma kullum cikin surutu takewa mama "Hauwwa wannan zagada zagadan yaran naki, duk sun isa aure amma kin tare su a gaba kina ado da su a gida, ga ƙauye can muna da mata burjik, amma dan mugunta kin tare su kin hana su motsi'
Mama ta ce "Haba Gwaggo, guda nawa yaran suke, haryanzu su Baba basu haɗa talatin ba fa, duk girman jiki ne, kuma kina ganin irin rayuwar da ake sai godiyar Allah, babu mai ƙwaƙwarar sana'a sai ƙarfin hali, idan suka ɗauko aure da yaya za su riƙe?"
"Ba wani nan, idan mutum yayi aure Allah zai warware, amma kallesu dan Allah tuma-tuman gwauraye ki na ado da su a gida, babu mai mata, kalli dai wannan zagaren, sai dai ya shigo fuska kamar bajimin sa, ya zo ya ɗau abinci ya fita yana zazzare ido kamar wani zaki, ko fara'a ba ya yi, kai haka zaka yi wa matar ma idan an aureka?, ko da yake ma wace macence za ta auri mutum ba fara'a ba komai fuska kamar kunun kanwa ba rahama"
Lomar Abincinsa kawai yake kawai, ko motsi bai yi ba, balle ya nuna ya san da shi take, yana jin ta ya share ta.
Ruma kamar ta kwashe da dariya, jin an ce fuskar yaya Umar kamar kunun kanwa, amma sanin ruwa ba sa'an kwandon ba ne ya sanya ta ja bakinta ta tsuke.
"Umaru da kai fa nake" A hankali ya ɗago idanunsa ya yi mata wani irin kallo, ya mayar da kan sa ya cigaba da cin abinci.
"To Allah ya kyauta, ka ma dai mayar da ni mahaukaciya, ka je ka ƙarata, tattara kayana ma zan yi na bar muku gidan ku, gobe goben nan zan bar garin nan.
A hankali yasir ya ce "Alhamdilillah, Allah ya raka taki gona"
A rikice ruma ta ce "Haba Gwaggo, ni bana son ki tafi, dan Allah ki zauna bamu gaji da ganinki ba".
Huzaifa ya yi ƙasa da murya ya cewa Abdallah"Ji munafukar 'yar nan, ko a gidan uban waye bamu gaji da ganin na ta ba, mata duk ta addabi mutane?"
Abdallah ya ce "Ashe ka manta wacece ruma, ai wannan yarinyar tsaf sai ta haɗa yaƙin duniya na uku, duk abin da ta san za ta aikata wanda ba a so shi take yi"'
Kamar wasa ruma har da kuka, wai kar Gwaggo ta tafi, ji suka yi kamar su yi wa ruma taron dangi su zaneta.
Ganin ruma na kuka, ya sanya Gwaggo ta ce ba zata tafi yanzu ba, saboda ruma.
*****
Sauri-sauri take yi, tana tafe tana duba agogon hannunta, tana daf da makara zuwa wurin da zata.
Tana ƙarasawa harabar gidan ta ɗan ɗaga murya ta ce "Gali, gani na fito zo mu je na makara"
Cikin girmamawa da murmushi Gali ya taso ya ce "Allah ya taimaki 'yar gaban goshi, Allah ya ƙara miki lafiya uwar ɗakina, ai tun ɗazu ke nake jira, tun da tun huɗu ki ka ce mini"
"Kai dai bari, na tsaya na yiwa Ammi girkin dare, kar na je ban dawo da wuri ba ka san ba komai take ci ba"
Ya ce "Haka ne, bari na fito da motar" ya yi gaba ita kuma ta tsaya.
'yan mata ne su huɗu, suka fito ta ƙofar wani sashi na cikin gidan, suka tunkaro in da take wajen harabar gidan, hakan ya yi dai-dai da fito da motar da Gali ya yi.
Kai tsaye suka tinkari motar ba tare da sun kulata ba, suna ƙoƙarin buɗewa su shiga.
Da sauri Iman ta ce "Kai, fita fa zan yi, zai kai ni unguwa ne"
Ɗaya daga cikin su ta kalleta ta ce "Saboda ta ki fitar zamu fasa tamu ne?"
Iman ta ce "A'a ba haka nake nufi ba, na ga kun iya driving, kuma ga wasu motocin, ni Ammi ta hanani tuƙi ne, kuma na yi magana da Gali tuntuni a kan zai kai ni unguwa"
Cikin tsawa ɗaya daga cikin su ta ce "Shut up! Mu ki ke kallo ki ke gayawa haka, kin manta a tuna miki ne?"
"Me ku ke yi haka a tsatstsaye?" Gaba ɗaya suka waiwaya suka kalli mai maganar.
Jikin Iman ne ya yi sanyi, tare da shiga wani yanayi mai wuyar fassara, bayan sanya idanuwanta a cikin nasa.
Fauziyya ta cire glass ɗin fuskarta ta ce "Bro, wannan ƙanwar ta ka ce take yiwa mutane rashin kunya, duk motocin gidan nan ta rasa wadda za ta hau, sai da muka zo muka ce a kai mu unguwa, wai ita ma tilas ita zata hau a fita da ita"
Ya tsuke fuska ya kalli Iman ya ce "Wato ke tsagerancin naki har ya kai ki din ga yiwa na gaba da ke rashin kunya ko? Sa'anninki ne su?"
Jiki a sanyaye ta kallesu, sannan ta mayar da idonta kan sa, sai dai ta kasa magana, sai hawaye da suka cika mata ido.
"Ina magana zaki yi mini kuka, get out from my sight, stupid girl"
Gaba ɗaya ta rasa meya kamata ta yi, jiki a sanyaye ta nufi hanyar fita daga gidan.
"Ke zo nan" ta ji muryarsa ba tare da ta yi tsammanin hakan ba.
Ta juyo ta dawo in da yake tsaye.
"Ina zaki?"
"Napep zan je na hau"
"Wuce ki koma, ba zaki fita ba" yayi maganar cikin bayar da umarni. Ta kalli yadda motar da su Fauziyya suka shiga ta bar gidan. Ba ta ce masa ƙala ba, ta koma sashin su, sai dai duk yadda ta so ta riƙe hawayenta abin ya faskara, tuni hawayen suka wanke mata fuska.
"Subhanallah, abar ƙaunata ya haka? Meyafaru? ya baki tafi ba?" Ammi ta yi mata tambayoyin a jejjare cikin ruɗewa bayan ganinta ta na kuka.
Iman ta share hawayenta ta ce "Bakomai Ammi, kawai fasawa na yi"
No ban yarda ba, gaya mini"
"Ammi su Fauziyya ne da Yaya Mahmud".
Nan da nan Annurin fuskar Ammi ya ɗauke gaba ɗaya ta ce "Mahmud again? Tura fa ta fara kaiwa bango, meya yi miki?"
Iman ta share hawayenta ta ce "Ammi dan Allah ki bar maganar, kar ranki ya ɓaci, bana son ki damu"
Ammi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce "Na ji, amma me suka yi miki?"
"Dan Allah kar ki damu Ammi, bakomai ki yi haƙuri"
Jinjina kai Ammi ta yi sannan ta ce "Yanzu shikenan, kin fasa fitar kenan?"
Iman ta ɗaga mata kai alamar eh. Ta ja hannun Iman suka bar falon.
****
Cikin rarrashi mama take magana, "Ruma, aiken ki nake son yi, amma bana son ki je ki yi mini shirme, ko ki tsaya a in da ban aike ki ba"
"In sha Allah mama, ba zan tsaya a ko ina ba, fiii zan ware dogayen ƙafafuwana da bala'in gudu na je na dawo"
Mama ta ce "Wane irin gudu kuma? Kalen ki watasar mini da kayan aiken, ki tafi a hankali, ki yi sauri ki je ki dawo"
"In sha Allah zan yi sauri, na je na dawo"
Mama ta gaya mata in da take so ta je, tare da abin da za ta kai, ruma ta sauya kaya ta saka hijjabi, ta fita yi wa mama aike, ta ƙuduri aniyar za ta je ta yi sauri ta dawo ko dan ta farantawa maman.
Tashin farko ta bi ta cikin unguwa, tana tafe tana kalle-kallenta, duk wani lungu da saƙo idan ta bi sai an kira sunanta, dan kusan kowa ya santa.
A ƙofar wani shagon aski ta ga keken Huzaifa, hakan ya tabattar mata da yana cikin shagon.
Murmushi ta yi ta nufi ƙofar shagon askin, da sallama ta buɗe ta shiga cikin shagon.
Duk maza ne a ciki, ga Huzaifa ya zauna a kan kujera za ayi masa aski, jin sallamar mace ya sanya dukkansu suka juya suna kallonta.
"Ohh Huzaifa yau Allah ya yi zaka cire wannan sumar kenan? Kuma wallahi aka yi maka askin 'yan iska kai da mai sunan Baba"
A ƙule Huzaifa ya ce "Ke uban me ya kawo ki nan? Ba ki ga shagon aski bane?"
"To ni ina ruwana da wani shagon aski, ba dai mutane ne a ciki ba, keken ka na gani a waje na san kana nan, na ce bari na leƙo na ganka"
"To na ji na gode, fita ki bar wurin nan"
"To sai ka tsaya na gama kallon kalandar askin nan, sai na tafi " tayi maganar tana riƙe ƙugu, tare da zubawa kalandar ido.
"Ni wannan yarinyar ba ke na taɓa rabaku faɗa da wasu yara ba, kun dawo daga makaranta?" Cewar wani da yake zaune shima yana jiran askin.
"Eh nice, me na yi kuma?"
Ya ce "A'a gane ki kawai na yi"
"To yanzu da ka gane ni lada nawa aka baka?"
Mai aski ya ce "Deluwa, dan Allah ki yi haƙuri, wurin nan duk maza ne, ki je aiken da aka yi miki, ko kuma in saka a riƙe mini ke na yi miki aski"
"Aikuwa da sai ka kasa zaman Ɗorayi, sai na saka yayyena sun kakkaryaka sun zubar, ni zaka yiwa aski?"
Huzaifa ya miƙe tsaye rai a ɓace ya ce "Bi ƙofar da ki ka shigo ki fita"
Ta ɗan kwaɓe baki ta ce "Huzaifa ba ayi maka gwaninta, daga ziyara?"
"Ki fita na ce, wallahi na zo in da ki ke sai na gwara kan ki" ja ta yi ta tsaya cike da taurin kai tana kallon idonsa, hakan ya ƙara tunzura shi, yayi kanta amma suka riƙe shi, ta fita da gudu daga shagon.
Tana fita ta yi ƙwafa, ta tura keken sa ta ji bai rufe ba, keken ya fi ƙarfinta, amma ta haye ta yi gaba.
Wani ya leƙa shagon askin ya ce "Huzaifa ƙanwarka ta ɗau keken ka fa ta tafi"
Da sauri ya miƙe ya leƙo, ai tuni ta kusa ƙarshen layin, ya san ko da ya bita ba zai cimma ta ba.
Kawai yayi tsaki ya koma ya zauna, zuciyarsa na tafasa, 'yan cikin shagon suka din ga dariya, kowa na tofa albarkacin sa a kan halayar ruma.
Haka nan tun da ruma ta fita, mama ta kasa nutsuwa, kawai dai gata nan ne dai, ta fara dana sanin dalilin ma da ya sanya ta aiketa.
Tun tana saka ran ta ga ta ina za ta shigo gidan, har ta fara fidda rai, yanzu ba ta fiye ɗaga hankalinta ba, idan ruma ta fita makaranta ko aike ba ta dawo da wuri ba, sai dai fargabar mai za azo ace mata ruman ta aikata.
Aikuwa ilai, tana cikin wasi-wasi sai ga sallamar wata matashiyar budurwa da wata yarinya, yarinyar bakinta a fashe, jikinta duk kwata ga fasashshiyar roba, da sauran gari a cikin ta, yarinyar sai kuka take, yawu da jini yana zuba daga bakinta.
Cikin kaɗuwa mama suka gaisa da matashiyar yarinyar, mama ta hau tambayar ba'asi.
Babbar ta ce "Dama cewa aka yi na zo gidan su na faɗa, ruma ce ta taho a kan wani ƙaton keke kashe gardi, ta taho da gudu, ƙanwata ta karɓo niƙa, ta bugeta da keken ta faɗa kwata, ita ma ta faɗi a gefe, ta tashi ta karkaɗe jikinta ta hau keken ta gudu, kuma ba iya ƙanwata ta buge ba, tun da tana tafe tana faɗuwa a kan keken"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ya Allah kai ka jarrabeni, Allah ka dube ni, ka bani ikon cin wannan jarrabawa" mama ta kamo hannun yarinyar da aka jefa kwatar, ta wanke mata jiki, ta basu dubu ɗaya tare da basu haƙuri ta ce zata zo har gida ta basu haƙuri.
Gwaggo kuwa ta hau masifa "Wallahi mutanen maraya ba ku da kara a kan ɗa, yanzu saboda wannan ɗin aka wani aiko yawon kan ƙara, ai ɗa na kowa ne, kuma fitinar maraya ai daban take"
Kamar mama za ta yi kuka ta ce "Ba wnai fitinar maraya, dama can haka ake fama da ita, a ina ta samu keken da ta hau ni da na aiketa wuri daban, kullum sai ruma ta sakani asarar kuɗi da yawon ban haƙuri, nan gaba idan ba ayi wasa ba, sai wasu sun kai ƙararmu ga hukuma"
"A'uzubil'ahi kina uwa ba zaki faɗi alkhairi a kan yarinyar ki ba, ƙuruciya ce, kowa da irin ta sa" mama ba ta kuma cewa komai ba, idan ta biyewa zuciya, za ta iya musayar yawu da Gwaggo, wanda ba za ta so hakan ba.
Huzaifa ya shigo a kumbure yana bala'i "Mama! Ina ruma take wallahi yau sai na tattakata, sai na ci mutuncinta"
Mama da take a ƙule ta kalle shi ta ce "A ina ka ganta?"
"Mama shagon aski fa ta bini, na koreta shi ne ta ɗauke keke na ta gudu, ni sa'an wasanta ne ita duk wani halin zubar da mutunci ta iya"
Mama ta safe kai ta ce "A ina da ta samu keken kenan? Za ta gane ba ta da wayo da Baba zan haɗata bari ta dawo"
"A'a ke wace irin uwa ce, wannan mugun ɗan na ki, haka kawai ya kassarata a'a ban lamunta ba "
Huzaifa ya harari Gwaggo ya ce "Wallahi ko ba a gaya masa ba, da hannun nawa zan ci ubanta, sai na girgiza ƙashin haƙarƙarinta "
Har gefin magariba babu ruma babu alamarta, tun mama tana jurewa, har ta saka aje a nemo mata ruma.
Aliyu Allah ya bawa sa'a, ya ganota a wata tawagar 'yan d.j, ana biki an kunna d.j, ta shige tsakiyar manyan mata, ana rawar sabada, ta gantsare sai rawa take, tana wani juye-juye sai ka ce an saka mata batir, ga ta a shafe ba gaba ba baya ama sai karkaɗa jiki take.
Cikin 'ya'yan Mama, Aliyu Ustaz ne, ba shi da ra'ayin wannan abubuwan, amma yau a saboda ruma, sai gashi a tsakiyar mata, ya samu bayan ruma da take ta juyi, ya tsula mata tsumagiya.
A zafafe ta ƙandare ta juyo, a zaton ta yaron mai D.J ne ya daketa, dan dama yana ta korar yara daga cikin filin rawar taƙi tafiya. Ba kuma rawar kawai take yi ba, har da satar kuɗin liƙi tana sakawa a cikin hijjabinta, sai ta gantsare tana rawa idan aka liƙo sai ta wayance ta ɗauke kuɗin.
Cak ta tsaya tana kallon Aliyu, ta ɗaga kai ta kalli yadda gari ya yi duhu.
"Sannu 'yar makaɗa, aike da aka yi miki kenan ko? Fita ki wuce mu tafi"
Kasa magana tayi, a take tayi saranda, da jin za ta iya ɗaukar kowane hukunci, saboda ita kanta ta san ta tafka ta'asa.
Ta janyo keken Huzaifa, da Allah ya sa ba a sace ba, ta hau turawa, Aliyu ya haske keken, tayoyi duk sun sace, dan ɗayar ma fashewa ta yi, ga kaca ta zube keken duk wani gurin ya lotse, adon fitulun da ya yiwa keken kuwa, suma wasu duk sun fashe.
Yana tafe yana kallon ruma, yana tunanin anya ruma mutum ce, fitinarta ko su da suna kamarta ba su yi haka ba, su dai akwai dambe kamar zakaru, kamar su cinye juna, amma rashin ji a gida, rashin ji a unguwa rashin ji a makaranta wannan sai Ruma ƘANWAR MAZA.
A ƙofar gida suka tarar da Uamar, yana tsaye yana waya, tana ganinsa ta fara kuka, tana cewa "Kashina ya bushe"
Aliyu ya ingiza ƙeyarta zuwa cikin gidan, da sauri Huzaifa ya taso, dan ta kekenaa yake yi, sai dai yana kallon keken ya san ko a wurin 'yan gwan-gwan wannan keke ba zai daraja ba, kamar yayi shekara da shekaru.
A ka rasa wanda zai ce mata komai, duk suka zubo mata ido.
Mama ta ce "A ina ka ganota?"
"Ga ta nan ku tambayeta"
Cikin muryarsa mai razanata musamman idan ba ta da gaskiya ya ce "Daga ina ki ke?"
Jikinta ya hau rawa ta ce "Dan Allah mai sunan Baba......
"Daga ina ki ke fa kawai na ce?"
Gwaggo ta ce"Ya zaka razanata da wannan muryar ta ka, ka tambaye ta cikin nutsuwa mana"
Huzaifa ya daɗe bai ji abin da yake shirin sanya shi kuka ba irin yau, ya kasa ko tari tun bayan tozali da kekensa.
Rarraba ido kawai take tana kokowa da numfashi, ganin yadda kowa ita yake kallo yana jiran amsarta.
Wata irin gigitacciyar danƙa Uamar ya yiwa kunnenta, ta kurma ihu, ya janyota har tsakiyar tsakar gidan, ya dungurar da ita, ya naɗe hannun rigarsa cikin tsawa ya ce"Ina ki ka je da aka aike ki?"
Cikin kiɗima da razani, ruma ta wassafa komai, ba ta ɓoye ba ciki har da zuwa wurin aski da yadda ta ɗau keke tana tafe tana faɗuwa, duk ta gurje gwiwa, da yadda bayan ta dawo daga aike ta tsaya wurin 'yan bikin da ba ta san suwaye ba ma, tana rawa tana satar kuɗin liƙi.
Sai a lokacin ta faɗi har faɗa suka yi da yaron dj yana ce mata shegiya ɓarauniya.
"Yanzu ina kuɗin da ki ka ɗebo ɗin?" Yayi maganar yana miƙa mata hannu.
Aikuwa ta zura hannu a rigarta, sai ga kuɗi, a ƙalla idan aka ƙirga sun kai dubu uku da ɗoriya.
(SORRY FOR THE LATE UPDATE, AYYUKA SUN YI YAWA NE, INA GODIYA DA TARIN ADDUOI DA ƘAUNAR DA KU KE WA BOOK ƊIN ƘANWAR MAZA)
Ayshercool
08081012143
[13/07, 9:01 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
12
Mai sunan Baba ya kalleta a tsanake ya ce "Sata ki ka koma yi kenan ko?"
Ta girgiza kai da sauri ta na zazzare ido.
"Ba zaki buɗe baki ki yi mini magana ba?"
"A'a Yaya wallahi ba sata nake yi ba"
"To idan ba sata ba, me ki ka yi, kin san su masu bikin ne, ko kuma sun sanki, idan ba sata ba baki suka yi, ko nan aka aike ki?" Ta girgiza masa kai.
Ya ce "Good, tashi ki je ki yi alwala ki yi salla, zan gauraya da ke, tashi maza ina jiran ki"
Huzaifa da yake ta huci, ya cika ya batse kamar ya sha yeast ya ce "Wallahi yau sai na lallasaki, za ki gane baki da wayo"
Gwaggo ta ce "Ku dai din ga haƙuri yarinya ce, ƙuruciya ce kawai take damunta"
Huzaifa ya yi ƙwafa ya ce "Ba ƙuriciya da yarinta ba, Allah ya sa ɗanyar ƙwaƙwalwa ce a kan ta da ba ta nuna ba, sai na lallasata na koya mata hankali"
Duk da tana cikin tashin hankalin rashin sanin hukuncin da za ta fuskanta, hakan bai hanata murguɗawa Huzaifa baki ba, tana harararsa, duk da laifin da ta tafka masa.
Daga shiga banɗaki alwala ta tsiri kashi, duk dan ta ɓata lokaci kar ayi mata hukunci mai wahala, ta na fitowa, Umar ya ce a tsakar gida za ta yi sallar, dan haka ta ɗau hijjabi ta tayar da salla.
Ita kanta ba ta san adadin raka'ar da ta yi ba, kawai yin sallar take cike da zullumi, a sujudar ƙarshe kuwa kai kace neman gafara take ko bacci tayi, amma babu ɗaya nazari kawai take.
Haka ta idar ta saka addu'a, abin da ba ta saba ba, ko sallar ta yi sai mama ta yi ta faɗa sannan take zaman yin addu'a.
Ganin taƙi sallame addu'a ne ya sanya Umar yi mata wani irin kallon, da babu shiri ta shafa addu'a ta tashi.
Ya ce "Oya, kamun kunne"
Cikin marairaicewa ta ce "Dan girman Allah Yaya.....
"Shut up! Zaki abin da na ce ko kuwa?"
Jiki a sanyaye, ta durƙusa ta kama kunnenta, nan da nan jikinta ya hau rawa, ta fara gajiya ta saka kuka.
Gwaggo ta ce "Kai ina mace ina wannan goho, kai meyasa ba ka tsoron Allah ne? Ke tashi dalla wannan wace irin azaba ce?"
Ruma ta ce "A'a Gwaggo, ba zan iya tashi ba sai ya ce dan Allah ku tayani bashi haƙuri"
Mai sunan Baba yayi shiru, ya ƙi kula Gwaggo, ta dubi mama ta ce "Ke ba zaki saka baki ya ce ta tashi ba, tun da ni ban isa ba?"
Mama ta ce "Ba haka bane Gwaggo, ai gara a din ga hukunta ta idan ba haka ba, sangarta da rashin jin da zata yi sai Allah ruma ba ta ji sam" ƙarshe mai sunan Baba ya tashi ya bar gidan ma gaba ɗaya ruma kuma ko da wasa ba ta tashi ba daga kamun kunnen, sai dai ta cika musu gida da koke-koke da magiya.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan Allah mama ki saka baki, na tuba na bi Allah, dan Allah ki bashi haƙuri ya ce in tashi"
"Babu ruwana, ba dai ba kya ji ba, ai na gode Allah da ya bani waɗanda zasu hukunta ki idan ki ka yi ba dai-dai ba, kuma kar ki sake kiran sunana"
"Wayyo Allahna na shiga uku, wallahi mama zan iya rasuwa, kaina da wuyana ciwo suke yi mini, bana son na mutu yanzu, bana nafila karatun Alqur'ani ba kullum nake yi ba, gashi ina yi miki abin da ba kya so, bana son na mutu yanzu ban tuba ba, wallahi mama zan iya rasuwa a wurin nan"
Yasir ya ce "Ba ki jigata bane ba, da ki ke iya wannan surutun"
Gwaggo ta ce"Ji min kafirar yarinya, ba nace ki tashi ba kin ƙi, ni babu abin da ya ƙular da ni, irin wannan goho da ya saki kina 'ya mace, kema da azababben taurin kai na ce ki tashi kin ƙi".
Ruma ba ta kula Gwaggo ba, sai cigaba da rusa kuka da tayi, tana magiya da neman taimako.
Cike da ƙuluwa Yaya Aliyu ya ce"Ki yi mana shiru dan ubanki, tun da ba wani ne ya aike ki ki aikata abin da ki ka yi ba" haka ruma ta ja bakinta ta tsuke, tana kuka ƙasa-ƙasa dan wasu lokutan yaya Aliyu ma ba daga nan ba wuri8iya tsare gida da hukunci, dan daga yaya Umar sai shi a zafi.
Har mai sunan Baba ya dawo ruma tana nan tana aikin kamun kunne, tana yi tana faɗuwa tana tashi.
Sai da ya dawo sannan ya ce ta tashi, kuma ya ce mata washegari za su gauraya.
Tana miƙewa tsaye jiri ya kwasheta sai amai, Gwaggo ta fito da sauri ta kama ruma, kanta sai juyawa yake saboda azabar wahala.
A zaune ta yi alwala tayi sallar isha'i, ko abinci ba ta nema ba, ta kwanta saboda galabaita, cinyoyinta sai azabar ciwo suke yi mata, dama da fari suna ciwo saboda hawan keke, gwiwoyinta na raɗaɗi saboda duk ta ƙuje su saboda keke, yanzu kuma ga kamun kunne, jikinta kamar an mata duka haka take jin ta, a take wani irin wahalallen bacci ya kwasheta.
Sai dai kwana ta yi da wani irin zazzafan zazzaɓi, wanda ita kanta ba ta san ya hau ta ba, jin surutan ta ya yi yawa a baccin ne ya sanya mama zuwa ta taɓa jikinta, ta ji da zafi sosai.
Duk da mama a ƙule take da ruma, haka ta fita ta ɗebo ruwa ta sanya ɗan ƙaramin towel, ta din ga shafawa ruma ruwa a jikinta.
Tun asubar fari kuwa, ruma amai ne ya tasheta, saboda har a lokacin jiri take yi.
Yanzu ma a zaune ta yi sallar asuba, ta nemi wuri ta kwanta.
Tun mama na basar da ita, har kuma ta fara damuwa, Gwaggo kuwa ta samu wuri ɗaya ta zauna sai mita take na masifa a kan mama tana gani aka bawa ruma gwale-gwale amma ba ta ce komai ba.
Bayan gari ya gama wayewa, Gwaggo ta karya ta yi haramar tafiya, sai dai a lokacin ruma ta samu bacci, dan a galabaice take. Gwaggo ta ce kar a tasheta, Abdallah ya tafi rakata tasha, suna ta murna zasu huta, dan dama Gwaggon ta ishe su, ruma ce kawai take son zamanta a gidan.
Mama ta tashi ruma, ta matsa mata a kan lallai ta ci Abinci, ta na ci tana kuka ta ɗan sha tea kaɗan ta kuma kwanciya, sai dai ko mintuna goma ba ayi da cin Abincin na ta ba, ta tashi ta cigaba da amai.
Ba shiri mama ta ce Aliyu ya zo ya kai ruma chemist a dubata.
Da ƙyar take iya tafiya, suna tafe tana kuka, har sai da ran Aliyu ya fara ɓaci, amma ya shareta suka cigaba da tafiya a hankali. Cikin sa'a kuwa suka tarar ya fito, kasancewar asabar ce, ranar ba ya zuwa aiki.
Ya na ganinsu cikin kulawa ya ce "Subhanallah, 'yar gidan mama yau ke ce ba lafiya?" Ita dai ba ta iya magana ba ta nemi wuri ta zauna. Aliyu ya zauna ya rungumeta, saboda ƙoƙarin faɗuwa take yi.
"Meya sameta haka?"
Aliyu ya ce "Ina ga zazzaɓi ne dai, da amai ta fara jiya"
Bakinta bai mutu ba, ta ce "Kamun kunne aka sakani, kusan awa goma shine ya sani rashin lafiya"
"Subhanallah, waye ya saki kamun kunne kuma?"
"Mai sunan Baba ne"
"To ki yi haƙuri, yanzu dai zan ɗibi jininki na yi miki gwaji, in duba meye ya haddasa zazzaɓin"
Ɗiban jinin da za'a yiwa ruma, tamkar za a cire mata ido, ta dinga kurma ihu, tana fizge-fizge, ga ta da shegen ƙarfi, da ƙyar Aliyu ya riƙeta aka ɗebi jinin nan.
Kuka har da majina, Aliyu ya dinga dungure mata kai yana zaginta.
Ya gama gwaje-gwajen da zai yi mata, ya ce "Malaria ce ke damunta, dan haka akwai buƙatar ayi mata allurai, da kuma magunguna"
Ruma ta yi masa zuru da ido, tana jiran ta ga a ina za ayi allaurar.
Ya haɗa alluransa ya nufo ta, ta miƙe tsaye.
"Ke malama ki tsaya, dan ba zaki sake wahalar da ni ba"
"To a ina za ayi mini allurar?"
Mai chemist ya ce "Ai a baya ake yin ta"
"Wai bayana" tayi maganar tana nuna bayanta.
Nasiru mai chemist ta ce "A'a a mazaunai"
"Suwaye mazaunan?"
Aliyu ya haɗe rai ya ce "Ke juya ki tsaya ayi miki allurar nan mu tafi, kin san sarai a in da za ayi".
Ta riƙe skirt ɗin ta gam ta ce "Ni wallahi ba zai ganni ba"
Aliyu ya fizgota, ya riƙeta da ƙyar suka danneta suka yi mata, Aikuwa ta din ga zunduma ihu, kamar sun mata wani abu.
Haka aka gama yi mata treatment, suka taho gida, ban da uban kuka babu abin da take yi.
"To subhanallah, ko me aka yi mata kuma take wannan uban kukan haka oho" mama ta yi maganar tana fitowa tsakar gida.
Aikuwa suna shigowa, ta nufi mama tana kuka.
"Meye haka, kukan me ki ke haka,ki ke ɓare baki?"
"Mama yaya Aliyu ne da Nasiru mai chemist"
"Suka yi miki me?"
"Bayan ya ɗibar mini jini, kuma suka buɗe mini tsiraici na aka yi mini allura"
Mama ta ce "Subhanallah"
"Mama ba ke ki ka ce ɗuwawu tsiraici bane ba, amma har da Yaya Aliyu ya riƙe ni, Nasiru mai chemist ya ganni, wallahi ban yafe ba"
Mama ta girgiza kai, ta ƙiftawa Aliyu ido sannan ta ce "Haba Haidara, ya zaka yi mini haka, dan me za'a buɗe mata jiki ayi mata allura?"
Aliyu ya ce "To mama ai larura ce, ko a addinance ba haramun bane".
Cikin masifa ta ce "To shi yayana ne da zai ganni? Har da taɓani ya yi mini allura a wurin"
Aliyu ya ce "Sa'anki ne ni, uban me za a kalla a jikin naki?"
"Wallahi ba zan taɓa yafewa ba, Allah ya jijjigo bala'in duniya da lahira ya ɗora masa, tun da ya ganan mini tsiraici na"
Mama ta ce"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace irin Addu'a ce haka, kar in kuma ji, baki san larura ba?"
Aliyu ya ce "Sakarya, kamar ba tsairaicin ki ka je kina kaɗawa a gaban mutane ba jiya"
Umar ya shigo ɗakin mama, suna magana, bai kula ruma ba amma dan ya duba jikinta ya shigo.
Tana kwance ga zafin ciwo, ga na takaicin allurar da aka yi mata, zafin allaurar bai dameta kamar ganinta da mai chemist ya yi.
Sai da yamma mama ta sakata ta yi wanka, ta canza kaya ta ɗan ji ƙwarin jikinta.
Sai da ta kwana uku tana fama, sannan ta ware gaba ɗaya, sai dai rashin lafiyar da tayi ya sanya aka mance da laifin da ta tafka, kowa sai lallaɓata yake, ban da Huzaifa.
Ta ware sarai har ta koma makaranta, kullum mama cikin nasiha take yi mata, tare da yi mata addu'a da fatan shiriya.
Tun daga ranar ruma ta daina bi ta hanyar chemist ɗin Nasiru, idan kuwa ta ganshi ko kallonsa ba ta yi, balle ta gaishe shi, a cewarta ɗan iska ne tsairaicin ta ya kalla.
"Mama wai yaushe zaki haihu ne, babannin 'yan ajinmu sai haihuwa suke yi, amma ke ban taɓa ganin kin haihu ba"
Mama ta ce "Ikon Allah, ba gaki na haife ki ba, ai ke ce auta ha zan kuma haihuwa ba, sai dai in kin girma kin haifa na ɗauka"
"To ni yaushe zan haihun?"
"Sai kin girma kin yi aure"
Ruma ta ɗan yi jimm sannan ta ce "To ni so nake na haihu, ina son ƙani ko ƙanwa da zan din ga wasa da su"
"Ruma ki ka haihu yanzu ai a nemi tsari, sai an yi aure ake haihuwa"
"To gaskiya mama ni so nake na haihu yanzu"
Usman da yake jin hirar ta su ya ce "Ke, idan ki ka haihu ba aure tsanarki za ayi, a kore ki daga gidan nan da unguwar ma gaba ɗaya, shi ya sa ba a wasa da maza, ki ka bari namiji ya taɓa ki to ciki zaki ki haihu, kuma korar ki za mu yi"
Waro ido ruma tayi ta ce "Amma ku kuke taɓani?"
"Ai mu yayyenki ne, muharramanki ne mu"
Ruma ta dafe ƙirji ta ce "Allah ya rufa mini asiri, ai da ban sani ba, taɓ idan aka koreni ina zani?"
"Oho miki dai, wannan damben da ki ke da maza ma, idan ba ki daina ba, sai dai ki ga kin haihu, kuma sai kin bar mana gida"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce "In sha Allah hakan ma ba zata faru ba, ai ni ban san hakan abin yake ba, Allah ya sa na yi tsawo na auri kyakykyawa mai kuɗi".
Mama ta ce "Ke zan ci ubanki ke da kyakykyawa mai kuɗin nan, miji na gari ake roƙon Allah, fitsararriya"
"Ni dai gaskiya bana son mummuna, mai kyau nake so"
"Ke dalla ware, da wannan munin za ki auri kyakykyawa?"
"Ni dai yaya Ussy, ka yi mini Addu'a, ka san wa zan aura a cikin 'yan ball".
Miƙewa ya yi ya ce "Ba ni da lokacin jij wannan shirmen na ki".
Tun daga wannan lokacin, ruma take kaffa-kaffa, da gudun kar wani namiji ya taɓa ta, saboda kar ta haihu a koreta ta shiga uku, kuma ta san idan aka koreta ba kuɗin mota za a bata ba, balle ta tafi ko ƙauye ne wurin Gwaggo.
Yau gaba ɗaya mama ta kasa gane kan ruma, tun da ta dawo daga makaranta yanayinta ya nuna kamar tana cikin damuwa.
Ba irin tambayar da mama ba ta yi mata ba, amma ta ƙi gayawa maman dalilin damuwarta ta, ta ce cikinta ne yake yi mata ciwo kawai
Mama ta aiki ruma sayen maganin sauro, ta je ta sayo, ta dawo ta tsaya a soro tana kuka.
Huzaifa ne ya sameta a soron tana kuka, dan sai da ya ɗan tsorota.
"Ke me ki ke yi a nan?"
Cikin kuka ta kira sunansa "Huzaifa"
"Na'am" ya amsa.
"Ka san wani abu?"
"A'a sai kin faɗa"
"Yaya Usyy ne ya ce mini idan namiji ya taɓani, zan yi ciki in haihu, kuma korata za ayi daga gidan nan, sai malam ya aikeni karɓo masa chalk, da na kawo masa hannunsa ya taɓa nawa. Na tambayi 'yan babban aji na gaya musu abin da yaya ussy ya gaya mini, suka ce eh haka ne wai ciki ne da ni, ka ga cikina ma ya fara kumbura yanzu ya zan yi bana son a koreni dan Allah ya zan yi" ta yi maganar har cikin zuciyarta tana rushewa da kuka.
Huzaifa a ransa ya ce 'Alhamdilillah, na samo maganinki'
"Tabbas Deluwa kin kwaso mana abin kunya, yanzu abin da zai faru shi ne, ki haɗa kayanki a ɓoye, cikin dare na kai ki tasha ki bar gidan nan, dan idan mai sunan Baba ya sani sai ya jefa ki a rijiya"
Sake rushewa ta yi da kuka har da majina, ya yi saurin cewa "Sai mama ta jiyo kina kuka asirinki ya tonu ko?"
Ta goge hawanyeta ta ce "To ya zan yi?"
"Shikenan, zan rufa miki asiri, amma zaki din ga yi mini wankin uniform".
"Eh na yadda, amma dan Allah kar ka faɗawa mama, bana son a koreni dan Allah"
Huzaifa ya yi wani murmushi cikin mugunta ya ce "To na ji, goge hawayen ba zan tona miki asiri ba"
Abu kamar wasa, ruma ko abinci ba ta iya ci, gashi kullum sai ta wanke wa Huzaifa kayan uniform.
Mama ta gaji ta ritsa ruma, har da bulala sannan ta zauna ta yiwa mama bayanin abin da yake damunta.
Mama ta yi salati ta sanar da Ubangiji, gaba ɗaya ruma ba ta da wayo, ga shegiyar tambaya idan kuma ka yi mata bayani yadda za ta fahimta, nan ma ta yi wata kwaɓar.
Sai da mama ta yi da gaske, sannan Ruma ta yadda ba ta da ciki, dan har da nunawa mama cikinta wai ya kumbura ɗa ne a ciki.
******
Ta na zaune a kan sallaya ta idar da salla, sai dai ta lula duniyar tunani, ba lazamin take yi ba.
Kamar daga sama ta ji ana kiran sunanta, ta yi firgigit ta dawo hayyacinta.
"Ohh Nusaiba, an gama girkin daren ne?"
Nusaiba cikin damuwa ta dubi Ammi sannan ta ce, "Ammi, tunanin me ki ke yi haka ne? kin san fa ba ki da cikakkiyar lafiya"
Ammi ta yi ajiyar zuciya ta ce "Nusaiba tunanin nan na dole ne, shi yake yin kansa, abubuwa sun yi mini yawa, bana son na nuna gazawata amma ni na san na gaza na kasa shawo kan komai, al'amura na ta ƙara dagule mini"
"Me kuma ya faru ne?"
"Mahmud, lamarinsa yana damuna, ga kuma yadda aka addabawa yarinyar nan a cikin gidan nan, haƙurina ya fara ƙarewa, duk wanda ya taɓa Iman ni ya taɓa raina ya na ɓaci fiye da tunaninki"
Nusaiba ta gyara zamanta ta ce "Ammi, kin san wannan duk shirin Mummy ne, so take ki magantu ku raba abin faɗa a cikin garin nan, ita take buga miki wannan wasan, ki ƙyaketa kuma ki yi haƙuri ki ɗauke kan ki daga Mahmud, ba ga takawa nan ba, mu da shi mun isheki rayuwa su je su ƙarata mana"
Ammi ta girgiza kai ta ce "Nusaiba kenan, ba zaki gane ba, tashi maza ki je ki tabattar an gama komai, sannan ki kira mini Iman, ba na son zamanta ita kaɗai"
Nusaiba ta ce "To shikenan Ammi, bari na je".
Sannu a hankali yake tafiya, tamkar ya na tausayawa ƙasar da yake takawa, har wani rangaji yake kamar wanda ake yiwa kiɗa.
Fuskar nan a murtuke babu annuri, in da ya sa a gaba kawai yake kallo, yake burin cinmma. Babu tsammani suka yi kiciɓis a baranda, ba tare da ɗaya ya san ɗaya ya taho ba, kuma aka rasa wanda zai bawa wani hanya ya wuce.
Kallon-kallo suka yi na wani ɗan lokaci, sannan ya lumshe idonsa a hankali ya buɗe. "Banihanya"
Kallonsa ya yi irin kallon ba ka isa ba ya ce "Ni da kai waye ya tarewa wani hanya?"
Cikin tsawa da zafin zuciya ya ce "Ka bani hanya na ce"
Murmushin gefen baki yayi, tare da rausayar da kai, yayi taku biyu ya koma gefe ya bashi hanya.
Sai da ya ƙare masa kallo, kamar ba zai wuce ba, sannan ya cigaba da takawa sannu a hankali ya wuce.
Ya waiwaya ya bi bayansa da kallo, yayi wani murmushi sannan ya ce "Zamu ga wanda ya fi iya buga wasan sa"
(A mini afuwa ban editing ba)
AYSHERCOOL
08081012143
[19/07, 8:42 am] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
P13
Kwanci tashi asarar mai rai, ruma ta kammala primary school za ta shiga sakandare, sai murna take yi, sai dai babu abin da ya sauya a halayenta na rashin ji, ta hanasu sakat,a gidan, da an jima sai ta buga tsalle ta ce "Wooo ni zan shiga sakanni in dire"
Yasir ya ce "Ji banza, me aka yi da maza meye wata sakandare, ai yanzu aka fara"
"A'a bar ni na yi tsalle, na samu cigaba a rayuwa ta, Sakandire fa, zan shiga jss1 ai girma ya zo, yanzu ni ma zan yi tsayi tun da zan shiga Sakandire"
Usman ne ya miƙo mata kuɗi ya ce "Yi sauri ki je wurin mai shayi, ki karɓo mini madara zan karya"
Ɗan ɓata fuska ta yi ta ce "Mama fa ta hana ni zuwa wurin mai shayi, da mai kifi da mai nama"
"Za ki wuce ki je ko sai na zo kan ki?"
Ba dan ta na son aiken ba, ta karɓa ta saka hijjabi ta fita, tama tafe tana shan farar ƙasa, bakinta yayi fari tas, kai ka ce akuya ce ta dumbuji dusa.
Ko da ta isa rumfar, dandzon matasa ne a ciki, sun cika kuma galibi abokan yayyenta ne, ba wanda ta kula a cikinsu ta miƙa kuɗi a bata madara.
"Rumaisa, ina Dambele?" Cewar wani matashi da yake ƙoƙarin kai lomar indomie.
Ta kalleshi ta ce "waye kuma dambele?"
"Ussy mana, na gidanku"
"Sai ka ce mini wani dambele kuma, kamar sunan rago, yana gida ya aka yi?"
"A'a ba komai, kawai na tambayeki ne, kin san Usman dambele wani ɗan ball ne, shi ma haka ake ce masa a filin ball".
"Ni zaka gayawa dambele ɗan ball me, ai sai dai na baka labari"
Kan kace me, aka ɓarke da hirar ball a teburin mai shayi tare da ruma, yadda take bayanin ball ya isa ka gane ƙanwar maza ce, gaba ɗaya ta manta da aike da aka yi mata, ta tsaya ana sharhi da ita.
A ƙalla ta kai mintuna arba'in a wurin, ta manta da aiken gaba ɗaya, ga wurin shayin a ƙofar gidan su yaje, ya ci ace ta je ta dawo, amma babu ruma babu dalilinta.
Ba shiri Usman ya sanya riga, ya fito nemanta, 'yar muryarta kawai yake jiyowa, tana bayani, har da dukan teburin mai shayi tana mayar da yadda aka yi.
"Ke! Meye haka?" Firgigit ta waiwaya, ta ga Usman a tsaye a bayanta.
"Aiken da na yi miki kenan?"
Kame-kame ta tsaya yi, dan har ga Allah ta manta da wani aike, musun ball na ɗibarta a rumfar mai shayi.
"Dambele yanzu nake tambayar ruma kai, ashe kana gidan ma, yarinyar nan ta burgeni, ta san ta kan ball abin mamaki, gaskiya na yarda ƙanwar maza ce"
A ƙule ya ce "Kai dilla ware, wannan ai hauka ne, kawai kun saka yarinya a gaba, kuna wani surutu, meye alaƙarku da ita?"
"Haba Usman, Ruma ai ƙanwarmu ce"
"Ba wani ƙanwarku, baku haɗa alaƙar komai da ita ba, ke kuma wuce kan na saka ƙafata, na kifa ki a wurin" sumi-sumi ta bar rumfar mai shayin ta nufi gida.
Ya bita gidan, ya dinga yi mata masifa, kamar zai cinye ta ɗanya.
*****
"Hutawarki lafiya uwar ɗakina ta kai na, jirgin sama maƙurar tafiya komai nisan ta"
Gyara zama ta yi ta dubeta ta ce "Bani labari, me ake ciki ne?"
"A'a, labarin bai gama nuna ba, amma ki bari ya ƙarasa tukuna, amma fa gida ya ƙara hargitsewa, ina ta gwara kawuna ta ko ina, na hanata sukuni, kusan tun bayan da Mahmud ya sa ƙafa yayi fatali da ƙudurinta"
"Hajiya Jamila, idan har muka tafi a kan tsarin da muka yi da farko, to tabbas zamu cimma buri, sarautar ta bar gidanku har abada"
Hajiya Jamila ta yi murmushi ta ce "Ai hakan na fi so, gara ai ayi biyu babu, sai na yi mata kassarawar da zata bar gidan nan da ƙafafuwanta, tun da dai na fuskanci asiri ba ya cin ta, gara ayi mutuwar kasko"
Dariya suka yi a tare, suna tafawa cike da duniyanci, tare da cigaba da tattaunawa a kan cikar muradansu.
****
Tamkar mai shirin zarewa, haka yake kai gwauro, ya kai mari a cikin katafaren falon, da ya sha ado da kayan alatu kamar ba za a bar duniyar ba.
Gefe guda wani babban mutum ne, zaune a ɗaya daga cikin jerin kujerun da suke falon, hannunsa riƙe da wani kwagiri, fuskarsa ɗauke damuwa.
Matashin ya daki teburi ya ce "Daddy meye abin yi ne? Ka na zaune ba ka ce komai ba?"
Dattijon ya numfasa sannan ya ce "Ka bini a hankali, ina tunanin wani abu ne"
"Daddy ba mu da isasshen lokaci fa, you know am following your footsteps, idan aka ɓata siyasarka, zai shafeni, mutum mai girma da daraja, kamar kai wannan ɗan ƙaramin alhakin zai kawowa barazana, gaba ɗaya gidajen jaridu, da dandalin sada zumunta, an buga labarin nan, kamar kai ka cancanci haka a ƙasar nan"
Murmushi mutumin ya yi ya ce "Easy Khalifa, ai ja da baya ga zaki ba tsoro bane ba, shirin yaƙi ne, haka zalika yaro bai san wuta ba sai ya taka, ka ƙyale shi, a yanzu ba ta tasa ma nake yi ba, na zuba ido ne in ga wani mataki za a ɗauka a kansa. Saboda idan ya matsa sai ya fasa ƙwai, to ba ni kaɗai za ta shafa ba, zata shafi manyan ƙasar nan da dama, yaron tone-tonensa ya yiwa, amma yana daf da tona wuƙar da za ta yi ajalinsa"
"Ohh my God, Daddy sai wasu irin maganganu ka ke yi, amma haryanzu ba ka gaya mini menene mafita ba"
Alama ya yiwa Khalifa da ya je, Khalifa ya ƙarasa gabansa ya durƙusa. Ya tallafo kan Khalifa ya yi masa raɗa a kunne.
A take damuwar kan fuskarsa ta gushe, murmushi ya mamaye fuskar ta sa ya yiwa mahaifin na sa alamar jinjina da hannunsa.
****
Sati biyu kenan da fara zuwan ruma makarantar sakandare, kullum sai ta yi gugar kaya, wai kar ta je da ƙazanta kamar ba 'yar sakandare ba, amma idan ta tashi dawowa tamkar ta yi dambe da kura, kayan nan duƙun-duƙun haka take dawowa da su.
Haka kawai yau zuciyarta ta raya mata, ta bi ta hanyar gidan mai unguwa, kasancewar a hanyar makarantar da take gidan yake.
A layin gidan mai unguwar, ta ga manyan motoci a fake, da alama wani abun ake yi. Hankalinta na kan lambun da ta taɓa zuwa ta ɗebo mangwaro mai gadi ya ce mata ɓarauniya, dan haka ba ta tsaya jin me ake a layin gidan mai unguwar ba.
Sai dai ko da ta ƙarasa layin lambun, wasu manyan motoci ta tarar guda uku a ƙofar lambun.
Lelleƙawa ta shiga yi, ta na haɗiyar yawu, saboda yadda take iya hango cincirindon bishiyoyin mangwaro da yadda suka yi 'ya'ya, ban da sauran 'ya'yan itatuwa.
"Ke uban me ki ke yi a nan wurin?"
Da sauri ta waiwaya, ta ga waye yake yi mata tsawa haka.
Ɗan gidan mai unguwa ne dai, da ya taɓa kamata.
"Taɓ dama kana nan?"
"Eh ina nan, yau ma satar ki ka zo yi?"
Ta tsuke ɗan bakinta ta ce "Ba yayana ya ce kar ka sake ce mini ɓarauniya ba?"
"Oho miki dai, ai ɗiba ki ka yi ba a baki ba"
"Eh amma ai dai ya biya"
Cikin hanzari ya ce "Wai me ma ki ke yi a nan wurin ne?"
Ruma ta ɗan riƙe haɓa ta ce "Hmmm, ashe haryanzu ka na nan, ba ka cigaba ba, ni gashi har na gama primary na shiga sakandare"
"Ke dalla ware, tun kan a haife ki na yi sakandare na gama, fitsararriya wai wani ban cigaba ba, ɓace ki bar nan wuri muna da baƙi"
Ta ɗan yi ƙasa da murya ta ce "Wai su waye suka zo, na ga ƙofar gidanku ma da mutane"
"Ban sani ba, ba zaki wuce ba sai na zane ki?"
"Dan Allah ɗan uwanmu mangwaro zaka san mini, ka ga dai yau ba sata na yi ba ko?"
Dariya ya kwashe da ita ya ce "A ina na zama ɗan uwanku?"
"Ai kai ɗan uwanmu ne na Musulunci"
Girgiza kai ya yi, zai wuce ta ya shiga cikin lambun, amma ta biyo shi.
"Wai ke baki da hankali ne, na ce miki muna da manyan baƙi masu wurin ne suka zo"
Cikin ko in kula ta ce "To ni ina ruwana, koma suwaye ai mutane ne ba mala'iku ba, dan Allah in biyoka ka san mini, ni sai na je na tambayo mai unguwa ma, na san shi zai ce ka bani"
Ya ƙarewa ruma kallo tsaf, a rashin hankalinta, tsaf za ta aikata abin da ta faɗa, na zuwa tambayo mahaifinsa, gashi yana tare da baƙi, ya dubeta ya ce "Yanzu abin da za ayi, ki zauna ki jirani, bari baƙin su tafi sai na baki"
"To, bari na je na zauna, kuma idan baka fito ba, biyoka zan yi"
"Wallahi ki ka shigo, zane miki jikinki za su yi"
"Su waye wai?" Ta yi maganar tana sake leƙa lambun.
"Kin ga tsaya, bari na je na samo miki" ya ƙarasa maganar tare da shigewa cikin lambun.
Dandamalin wani gida ta samu, ta ajiye jakarta, ta ɗebi duwatsu ta hau 'yar carafke.
Tun 'yar carafken na ɗauke mata hankali, har ta gaji da jiran ɗan gidan mai unguwa. Ta zube duwatsun ta tashi, ta je ƙofar shiga lambun ta tsaya, ta ɗaga murya ta ce "Ka cika alƙawari, zan shigo fa" magana ta fara ji ƙasa-ƙasa na mutane, alamar za a fito, ba ta yi niyyar matsawa daga bakin ƙofar ba, sai da ta hango akuya na shirin watso mata litattafanta, ta ci, ta nufi wurin jakarta, ta ɗau jakar ta na zagin akuyar, har da kiranta mayya mayuwanciya kamar tana magamaganana da mutum.
Tana waiwayo wa, taga mutanen sun fito, sai dai kusan duk sun yi rawani, sai mutum ɗaya da suke takewa baya, shi kuma suit ce ma a jikinsa.
Da gudu ruma ta kwaso, ta tsaya daga baya ta ce "Laaa sarki ne wannan?" Jin 'yar shilar muryarta ya yi, tamkar busar wata 'yar sarewa a kunnensa, duk da akwai dandazon yara da suke wurin, galibi suna zuwa idan har ya zo, saboda ya kan basu kuɗi. Har ya ɗan juyo, zai waiwayo ya ga wacece a cikin yaran, bai juyo gaba ɗaya ba, dogon hancinsa kawai ta iya ganowa, ya ɗauke kansa ya shige motar da aka buɗe masa.
"Sarki ka ganni, ka juyo ka kalleni, ko dai ba sarki bane ba, na ga sarki ba ya saka ƙananan kaya ai"
"Ke! Hattara yarinya 'yar talakawa, ba a yiwa takawa karan tsaye"
Shiru ta ɗan yi ta dube shi ta ce "'yar talakawa kuma, to wallahi gidanmu akwai abinci, mu ba talakawa bane ba, kuma ba gara ni ba ma, Idan mu ka je kallon hawa mandawari, mama ta ce mini masu irin kayanka bayi ne, sayar da su ake yi zamanin baya a karɓi kuɗi"
Kowa waiwayowa ya yi yana kallon ruma, ya yin da dogarin ya zabura ya yo kan ruma, aikuwa ta kwasa da gudu ta tayar da uwar ƙura, shi kuma ya bita yana a tare ta.
Da ƙyar ruma ta kai gida afujajan, ta na ta haki kamar numfashinta zai ɗauke, ta shige ɗakin mama ta ƙule ta na ta sauke numfashi.
Mama ta biyo ta ɗakin ta na faɗin "Ke!ke ruma ke da waye haka? Yanzun ma tsokanar ki ka yo ko? Tun yashe aka tashi 'yan makarantar ku, amma Allah bai nufe ki da shigowa ba sai yanzu ko? Ba zaki fito ba ina yi miki magana?"
Sumi-sumi ta fito, tana waige-waige sannan ta mayar da idonta kan mama.
"Daga ina ki ke?"
Ruma ta ɗan ɓata fuska ta ce "Mama ba ko ina fa"
"Zaki gaya mini ko na bari sai ya shigo?" Cikin kiɗima ruma ta ce "A'a, dan Allah kar ki yi mini haka, wallahi kallon sarki na tsaya, a lambun mai unguwa, shi ne wani bawa ya ce mini 'yar talakawa, shi ne" sai kuma ta yi shiru.
"Shi ne me?"
"Cewa na yi, ai gara ni ba baiwa ba ce, shi fa kayan bayi ne a jikinsa, wanda ki ka gaya mini ɗin nan ranar da muka je cikin gari kallon hawa, shi ne ya biyo ni da gudu"
Tafa hannu mama ta shiga yi tana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dama can na aike ki, na ce idan an tashi ki dinga zuwa wani wur?" Ta girgiza kai.
"Saboda tsabar rashin kunya da rashin hankali, ki ka tsaya kina cewa babban mutum bawa, daga yi miki bayani ranar, ke ba zaki taɓa hankali ba ko? Ina ma ya kama ki ya yi miki dukan tsiya, na gaji da halinki ruma, ki na girma ki na sake shiga dawa, gaba ɗaya babu alamar hankali balle nutsuwa a tare da ke. Ki je ki cigaba da abin da Allah ya nufe ki da yi, Allah ya gani na yi iya yi na, ban yi miki irin wannan tarbiyyar ba Allah ya shiryeki"
Ruma ta yi shiru, tana sunkuyar da kai kamar gaske.
A ɓangaren karatu, an samu sassauci daga halin ruma, kullum Usman ya na ba ta ƙwarin gwiwa, a kan kar abin da ya bata tsoro, duk wani abu da wani zai yi, ita ma za ta iya.
A makarantar islamiyya kuwa, tun da malam Habibu ya taɓa hannunta garin karɓar bulala ta daina bin sa, sai dai yau ta zauna a ajinsu, gobe ka ganta a wani ajin, ɗaukar magana kuwa ba ta fasa ba. Dan saboda tsaurin ido, har manyan 'yan matan nan haka take zagewa ta yi musu rashin kunya, ba abin da ya yi mata zafi. Kuma ku san ko yaushe ta na cikinsu, ba ta yawo da sa'aninta.
****
"Allah ya taimake ki Hajjaju Mummy"
Murmushi ta yi cikin isa da izza ta ce "Abin ƙauna, ka yi breakfast ɗin ne?"
"Eh, na yi" ya yi maganar ya na zama a kusa da ita.
Ta saka hannu ta shafi sumar kansa ta ce "Mahmud, ya kamata a rage sumar nan"
Yayi murmushi ya ce "Haba Mummy, wannan sumar yadda ki ka ganta ki bar ta kawai"
"Hmm to ai shikenan, ya shirye shiryen komawa school?"
"Alhamdilillah, ina nan ina yi, very soon zan koma"
Fauziyya ce ta fito falon riƙe kofin shayi, ta kalli Mahmud ta ce "Yaya Mahmud, barka da safiya"
"Yauwwa, ina Ruky, ban ganta ba?"
Ta nemi wuri ta zauna ta ce "Ba ta tash ba, bacci take yi" ya kalli agogon hannunsa ya ce "By this time?"
Mummy ta ce "Ka san ta na karatun dare, dole ta yi bacci da safe"
Ya jinjina kai ya ce "Haka ne".
"Amm Yaya Mahmud, takawa ya dawo fa, yakamata ku haɗu kan ka koma, kun daɗe baku haɗu ba" tsuke fuska ya yi, ya kalli Fauziyya ya ce "Yaushe ki ka fara tsara mini abin da zan yi a rayuwata? Ubana ne shi da lallai sai na ganshi? Na gan shi jiya mana so what?"
Mummy ce ta katse hirar, ganin Mahmud har ya ɗau zafi ta ce "Is ok, ya isa haka, ku dai idan ya shigo ku je ku yi masa sannu da zuwa, bana son ƙananun maganganu irin na gidan nan".
Sannu a hankali yake danna system ɗin da ke gabansa, kamar ya na tausayaa mata, hannunsa ɗaya kuma riƙe da cup ya na shan tea, idan ba ka kalleshi sosai ba, zaka ɗauka Mahmud ne a zaune.
Muryarta ce take dawo masa kunnesa, kamar a yanzu take magana *laa sarki ne wannan? Sarki ka juyo ka kalleni* ya tuna ƙarfin hali da ta dubi ɗaya daga dogarinsa, ta ce masa bawa, koma dai wacece a muryarta ya ji akwai yarinta da kuma tsananin tsaurin ido, idan sarkin ne shi a haka zata yi masa magana kenan, ba girmamawa?
Iman ce ta fito daga sashin Ammi, hakan ya kaste masa tunaninsa, ta ƙaraso falon ta zauna, ta kalle shi ta ce "Barka da hutawa ranka ya daɗe" tun ɗazu Nusaiba take falon, tun da suka gaisa ta ja bakinta ta tsuke, ta kasa ce masa komai, shi ma kuma bai kulata ba, amma Iman na fitowa ya yi murmushi.
"Barkanki dai auta ta Ammi, kin tashi kenan?" Ta jinjina masa kai sannan ta ce "Once again Ya hanya, ya kuma ibada?"
"Alhamdilillah, ya karatun?"
"Ina nan ina ta yi Yaya, ka yi mini Addu'a kuwa da ka je?"
Ya jinjina kai ya ce mata "Sosai, ban yiwa kai na Addu'a da na yi miki ba, na so mu tafi tare da ke, amma na san Ammi ba lallai ta yadda, sai dai ku je umarar azumi ke da ita"
Iman ta yi murmushi ta ce "Nima ina yi maka addu'a sosai yaya, Allah ya kawo abin da Ammi take ta fata"
Nusaiba ta jinjina kai, da wani ne ya tsare Yaya da wannan maganar da ya shiga uku, to wa ma ya ga fuskar hakan, ai sai Iman ɗin.
"Iman, ai kuma zaku iya samarwa Ami abin da take burin, ku fito mana da tsayayyu, a wuce wurin kawai"
Iman ta ɗan rausayar da kai ta ce "Sai dai Anty Nusaiba, amma ni dai kam sai a hankali " tayi maganar jiki a sanyaye.
Alama ya yi mata da hannu da ta zo.
Ta tashi ta tafi in da yake ta zauna, ya matsa kusa da ita, yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Na ji abin da ya faru lokacin ina Saudiyya, abin bai yi mini daɗi ba sam, da Ammi ta yi shawara da ni, ba za ta yanke wannan hukuncin ba, ai Allah ke da rayuwar kowanne bawa. Ki ɗau abin da ya faru a matsayin Mafi alkhairi, Allah ya tanadar miki mafi alkhairi, ni kai na example ne a gareki, dan haka mu cigaba da Addu'a gaba ɗaya" ta jinjina masa kai ta na share hawaye.
*******
Usman ne a zaune ya gama cin abinci, ya kalli Abdallah ya ce "Kai ka san wani hau da wannan Anas ɗin yayi mini yau?"
Abdallah ya ce "Sai ka faɗa"
"Wai ni zai tara ya ce mini ya na son ruma, yarinyar da ko ciwon kan ta ba ta sani ba, ni kuwa na ci ubansa, sai kaɗan na kikkifa masa mari"
Abdallah ya yi dariya ya ce "Ba abokin ka bane ba, na ga filin ball ɗin ku ɗaya ma"
"Dan abokina ne, sai ya ce yana son ƙanwata, mahaukacin ina ne shi?"
"Amma wallahi yaya Usy ba ka kyauta mini ba, 'yan ajinmu na Islamiyya su yi ta labarin saurayi, ni kuma ba ni da saurayi, duk wadda ba ta da saurayi fa wai baƙin jini ne da ita, sai an kai ta wurin malamai sun yi mata Addu'a "
Abdallah ya ce "Saurayin uban wa? Ke ya zaki yi da wani saurayi, ko yake shi Anas ɗin ne ma mara hankali, shi ma irinki ne ai mara kan gado perfect match"
Ɗan saroro ta yi ta ce "Wai Anas ɗin gidan mai taya?"
Abdallah ya ce "Ƙwarai kuwa"
Ta ce "Taɓ, Astagfirullah Allah ba irin wannan ba, kenan addu'a ta ba ta karɓu ba, ina ta Addu'a Allah ya bani saurayi mai kyau, mai kuɗi, mai ƙarfi sosai wanda zai din ga goyani kamar girman brownstrawman na wrestling, kawai sai wani Anas ya ce yana so na, wata uwar ƙeyarsa kamar sirdin keken baban su Ade, gashi siriri da kaɗan ya fi taliya. Ina ga sai na ƙara dagewa da Addu'a ".
Usman ya ce"Ke, kina halitta ne da zaki din ga kushe wasu? Kin ga ki shiga hankalinki, ba ke ce baki da kamun kai ba, dole kowa ma ya ce zai ce yana son ki, kuma wallahi idan ba ki shiga hankalinki ba, sai na bashi ke"
"Allah ya kiyaye, wallahi ba zan aure shi ba, gashi baƙi ƙirin kamar an rina shi".
"Ke zan ci ubanki na kuma jin kina kunshewa wani halitta, ke kyan ne da ke. Ni kullum fatana Allah ya baki miji na gari ko ya fi biri muni" mama ta yi maganar a hasale.
"Mama biri kuma, ba amin ba gaskiya, dan Allah idan irin wannan addu'a ki yi mini ki daina, ni wallahi kyakykyawa na ke so"
"Kyan banza da na wofi, kyan ɗan maciji ki auri kyan ya din ga gasaki ba gara mummuna na gari ba"
Ruma kamar za ta yi kuka ta ce "Ina wani abin arziki a muni"
Mama ta hau ruma da faɗa, ruma ta yi shiru, amma a duk sa'ar da mama ta ce Allah ya bata miji nagari duk muninsa a zuciyarta za ta ce ba Amin ba.
Yau ruma Alla-Alla take gari ya waye, sai murmushi take ita kaɗai.
Yasir ne ya lura da ta na fara'a, dan haka ya ce "Wai ke murmushin me ki ke yi ne haka?"
Ta gyara zama ta ce "Ka san tun da na shiga sakandare, ban yi faɗa da kowa ba, so nake na zama 'yan mata, in din ga tsayawa a cacar baki, to ni cacar baki ba ta biya mini buƙata, na fi son na haɗawa yarinya malaman jikinta, muka yi faɗa da wata yarinya, ka san ni ba na zagi, ta dinga zagina in gaya maka, amma ban yi kuka ba.
Kawai yau na ga babarta ta zo makarantar mu, da ƙyar ta shiga ofishin principal saboda girmanta, ina ga ta yi rabin bangon ɗakin mama.
Kai ina ga fa ta yi yakuzuna na jikin receiver girma, koma ta fishi, shi ya sa nake son Allah ya kaimu gobe, za ta gane ba ta da wayo, ba dai har da cewa babata tsohuwa ba ce, wallahi a jikin allo zan zana babarsu.
Ayshercool
08081012143
[19/07, 8:42 am] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
14
Buɗe baki Abdallah ya yi ya na kallon ruma, bil haƙƙi take maganar har cikin zuciyarta.
"Ke fa hankali bai wadaci ƙaramar ƙwaƙwalwarki ba, sai ki je allo ki zana babar wasu, idan aka zana taki zaki ji daɗi?"
"Ai ni na yi alƙawarin na daina dambe, ta zageni na kasa ramawa, saboda ashar take yi, ni kuma bana zagi, gaba ɗaya ta cuceni ta ɓata mini rai, ni kuwa ba ta san ba a taɓani a ci bulus ba, wallahi sai ta gane kurenta"
Abdallah ya girgiza kai ya ce "No, ki nemi wata hanyar dai, amma ban da iyaye, ba abin wasa bane"
"Iyaye ba abin wasa bane, ta ce mini mara tarbiyya babata tsohuwa, sai na ci buhun ubanta, ranar ma a sanyi ta sameni, da sai na tayar mata da aljanu na yi mata dukan tsiya, to bana som daga shigata makarantar a tsaneni ne, ayi mini mummunar shaida". Duk yadda Abdallah ya so nusar da ruma, ta yi biris ta ƙi fahimta ta yi alwashin ramuwar gayya a kan abin da aka yi mata.
*****
Nasihar da takawa yake yi mata, a hankali ta ji ta ratsata sosai da sosai, daga ita har shi suna fuskantar jarrabawa daban-daban, wanda hakan yake jefa Ammi cikin damuwa.
Nusaiba ta kalli Takawa da Iman ta ce "Iman 'yar gidan yaya, Ammi ta ki yayan ma naki"
Murmushi iman ta yi tana sake gyara zamanta.
Turo ƙofar falon aka yi, suka ɗaga kai gaba ɗayansu suka kalli ƙofar. Jabir ne ya shigo, da sallama a bakinsa. Suka amsa masa gaba ɗaya, hankalinsa ya na kan Iman ya na ƙare mata kallo. Hakan ya sanya ta haɗe rai tana ɗan kawar da kai gefe.
Yayi murmushi ya kalli Adam ya ce "Ni zaka yiwa haka, ka dawo amma sai dai na ji a gari ko ka neme ni"
Takawa yayi murmushin gefen baki ya ce "Ai idan ka san na dawo, zaka dameni ne ka sani yawo a gari, shi ya sa na yi shiru so nake sai na huta, shi ya sanya ma ban zauna a gidana ba, na yo nan"
Nusaiba ta ce "Uncle J, ina wuni?"
"Lafiya lau Nussy, Iman ba magana ne? 'yar rigima"
Ba dan ta so ba ta ce gaishe shi, gaba ɗaya kwanan nan ba ta son abubuwan da Jabir yake mata, wanda ta kasa gane kan su.
Suna tsaka da hirar sai ga sallamar su Fauziyya da Ruƙayya, tare da Samha suka shigo falon.
Gaban Iman ya faɗi da ta ga Samha, musamman wani irin kallo da take bin ta da shi, da Iman ɗin ta kasa gane wane irin kallo ne.
Jabir suka fara gaisarwa, sannan cikin girmamawa suka gaida Takawa. Cikin halinsa na ko in kula da kuma tsare gida ya amsa musu.
Fauziyya ce ta gyara zama ta ce "Yaya ashe ka dawo, bamu san ka dawo ba, sai ɗazu Mummy ta ce mana, ai ka dawo"
"Eh na dawo" ya faɗa a taƙaice.
"Masha Allah, ya ibada?"
Ya amsa da "Alhamdilillah"
"To Allah ya sa an yi karɓaɓiyya".
Samha ta gyara zama, ta na yiwa Adam wani irin shu'umin kallo, ta ɗan murmusa sannan ta ce "Takawa, ni fa kwance jaka na zo yi, daga zuwa wurin su Fauziyy, na ji suna cewa za su shigo yi maka sannu da zuwa, na ce bari na biyo su in yi sannu da zuwa, kuma a bani tawa tsarabar"
A hankali ya ɗago idonsa, ya kalli Samha, ya ɗan yi murmushi tare da girgiza kai amma bai ce komai ba.
Jabir ya dubi Iman ya ce "Iman, duk kin maƙalƙale mana shi, kamar ke kaɗai ki ka yi kewarsa, ki barmu mu ma mu gana da shi sosai mana" yayi maganar da sigar wasa.
Noƙe kafaɗa ta yi kamar ƙaramar yarinya, sai dai suna haɗa ido da Samha, samhan ta sake yi mata wani mugun kallo, da ya tilasta mata sunkuyar da kai.
"Jama'a ya shirin bikin Jamilu Turaki, Takawa akwai kilisa fa ranar Juma'a"
Adam ya girgiza kai ya ce"Kai, ƙyaleni da wata kilisa, duk na gaji, ni ban so ku ka san na dawo ba ma, ina buƙatar hutu sosai "
"Amma ba dai ka na nufin, ba zaka yi hawan ba, Jamil ɗin guda?"
"Sai na yi tunani tukuna, idan ina da time"
Jabir ya ce"Ba ruwana, kai da shi"
Tsarguwa da rashin sukunin da idanun Samha suka sanya Iman ne ya sanya ta miƙe ta ce "Ni dai sai an jimanku, zan je na huta"
Samha ma ta miƙe ta ce "Mu je, ina son na gaida Ammi kan na tafi " jikin Iman ya yi sanyi, dan ta san akwai wani abu a ran Samha data ce za ta bita ta gaida Ammi.
Suna shiga ƙofar da zata sada su da sashin Ammi, Samha ta riƙo hannun Iman, ta tsayar da ita suna fuskanta juna.
Cikin raunaniyyar muryarta kamar mai shirin yin kuka Iman ta ce "Me na yi miki?"
Samha ta ƙarewa Iman kallo, sannan ta ce "Wai wace irin yarinya ce ke, kin manta kashedin da na yi miki ko sai na sake nanata miki?"
Iman ta ɗan ɓata fuska, ta aro jarumta ta ɓoye tsoron ta ta ce "Anty Samha, ni babu komai a tsakanina da takawa, ki yarda da ni mana, ina jin sa kamar wanda muka fito daga ciki ɗaya, ni ba zan iya aurensa ba"
Samha ta ce "Ƙarya ki ke yi, ba wani ki na jin sa kamar wanda ku ka kwanta ciki ɗaya, ai ba ki da kimar da zaki kwanta mahaifa ɗaya da Adam, ko kin manta wacece ke?"
Iman ta girgiza kai ta ce "Ban manta ba, 'yar karere ce ni, wadda ba ta da gado a gidan Galadima, wadda aka taimakawa aka riƙe, ina sane ba sai kin tuna mini ba".
Samha ta yi wani murmushi sannan ya kuma duban Iman ta ce "Ƙwarai kuwa kina sane, ban da Ammi ta nace da a cikin barorin gidan nan ya dace ki tashi ba 'yan gida ba, dan haka ki kiyayi shiga gonata"
"Amma ta yaya, a tare muka tashi da takawa, ta yaya za ki ce sai na nesanta da shi?"
Ta ɗage kafaɗa ta ce "Wannan matsalar ki ce, ba tawa ba, dan na ga alamar tun da ba ki samu wancan ba, wannan zaki hara ki shiga hankalinki".
Iman ta girgiza kai ta ce "Ni babu abin da ki ke tunani tsakanina da takawa, amma ke ma Anty Samha bana tunanin zaki samu abin da ki ke so, akwai katangar ƙarfe a gabanki, kuma kin san takawa kin san halin sa sarai, ki bi a sannu" daga haka tayi gaba ta bar Samha a tsaye.
*****
Kamar yadda ruma ta yi alwashi, haka ta yi, ta je ajinsu ta zana wata shirgegiyar mata a kan allo, ta yi labelling ɗin ta. Gefe kuma ta zana ƙarama wadda ba ta kai matar ba, ta yi labelling ta rubuta Asiya shu'aibu.
'yan ajin suka dinga tuntsira dariya, saboda yadda zanen ya yi.
Ita kuwa Asiya ba ta san me aka yi ba, sai dai tana shigowa ta ga 'yan aji suna kallonta suna dariya.
Saroro ta yi, tana son gane me suke yiwa dariya, ba ta kula ba ta je ta zauna, sai dai ta na zaman idonta ya sauka a kan allon, ta ga ta'asar da ruma ta yi.
A firgice ta tashi tsaye, tana zazzare ido "Uban waye ya yi mini wannan rashin mutuncin"
Ruma ta miƙe ta ce "I am madam"
"Saboda tsabar kin raina wa kan ki hankali, kina nufin wannan babata ki ka zana?"
"An zanata ɗin, ni ba cewa ki ka yi babata tsohuwa ce ba, ashe ma babata ta fi taki kyau"
Kan ruma ta farga, Asiya ta diro gaban ruma ta shaƙe ruma da hijjabinta. Kan ruma ta farga Asiya ta rufeta da duka, ta kaita ƙasa saboda ta rufe mata fuska da hijjabi. Kan ruma tayi wani yinƙuri, Asiya tayi mata duka.
Da ƙyar aka kirawo wani malami, ya janye Asiya daga kan ruma.
Malamin ya tasa su a gaba zuwa ofishin malamai, dan hukunta su, ruma ta shafa bakinta ta ji jini, tun da take a rayuwarta ko da za ta yi dambe a fitar mata da jini, to tabbas a duba wanda suka yi damben ta lallasa shi shi ma.
Gaba ɗaya Wani irin baƙin ciki ya mamaye ruma, gaba ɗaya ta rasa abin da yake mata daɗi, tun da take ba a taɓa galaba a kanta ba sai yau.
Ko da aka je staff room ana mayar da yadda aka yi, ruma taƙi magana, sai idonta da ya yi jawur, aka yo caaa a kan ruma, malamai suka din ga yi mata faɗa a kan bata kyauta ba zana babar Asiya da ta yi, suna kiranta mara ɗa'a.
Haryanzu malaman basu san wacece ruma ba, dan tun da Allah ya sanya ta zo makarantar ba ta taɓa gwada musu halinta ba.
Aka ce sai ruma ta bawa Asiya haƙuri, sannan za ta yi wankin banɗaki na sati guda, ita kuma Asiya zata yi sharar aji na kwana uku, saboda ɗaukar mataki da ta yi suka yi dambe da ruma.
Juyin duniya ruma ta yi magana taƙi, ƙememe taƙi bayar da haƙuri, dan haka aka sakata Kneel down har aka tashi a rana.
Babu abin da take tunani sai abin da za ta yiwa Asiya ta huce daga wannan baƙin cikin.
Ko da aka kaɗa ƙararrawa, ruma ba ta jira malaman su sallameta ba, ta tashi ta tafi aji ta ɗauko jakarta, Asiya ta din ga yi mata dariya har da gwalo. Wata nutsuwa ce ta shigi ruma a lokacin, dan a lokacin ji take da da wani abin dukan a kusa da ita, to tabbas sai ta illata Asiya.
Ta ɗau jakarta ta fice, har ta je gida kamar zararriya jikinta a sanyaye.
Tun da mama ta ga ruma ta shigo babu ko sallama, ga uniform ɗin ruma a duƙunƙune ga busashshen jini a gefen bakin ta, ta san yau ta yi halin na dambe, ga takalminta da jakarta a hannu ta shigo da su, gwiwar wandonta ta yi kaca-kaca da ƙasa.
Ta zubar da su a tsakar gida ta shige ɗakin mama kawai ta nemi wuri ta kwanta.
Ba ta tashi ba sai bayan azahar, ta tashi ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallar azahar, ta kuma neman wuri ta zauna a tsakar gida.
"Mutuniyar, wai ya aka yi ne? Zo ki sayo mana kifi mu ci Abinci, tun da na dawo nake cigiyarki" yayi maganar yana leƙa fuskarta.
Maimakon ta amsa masa kawai ya ga hawaye a fuskarta.
"Ke, menene mama ce?"
"Yaya Usy"
"Na'am rumaisa"
"Ni za a daka a hana kuka? Zuciyata zata fashe" tayi maganar tana sake fashewa da kuka.
Rarrashinta ya shiga yi, yadda ya ga tana neman ta shiɗe, idanunta duk suka yi ja.
Ya din ga lallaɓata ta gaya masa abin da ya faru.
Mama da take jin su ta ce "Allah ya ƙara miki, Allah ya sa yau da ki ka samu wadda ta zane ki, ba zaki sake dambe ba, dama ban da iskanci meye na zana uwar wani, idan ke aka zana taki uwar zaki ji daɗi?"
"Mama cewa fa ta yi babata tsohuwa"
"To sai me? Tsufa ai arziki ne, ruma ita duniya 'yar siyasa ce, ba komai ƙarfi yake baka ba, amma kin kasa gane hakan"
Wani irin kallo take yi wa mama, wato ita mama ko a jikinta kenan.
Usman ya kawar da fuskar ruma daga kallon mama. Abu ne mawuyaci ruma ta yi fushi, ko an ɓata mata rai sai dai ta yi kuka, idan ta gama kuma shikenan ya wuce sai a shirya, amma yadda idanunta suka yi yau ya tabattar masa da ta kai maƙura a ɓacin rai, ba a taɓa defeating ɗin ta ba sai yau. Irin zuciyar mai sunan baba ce da ita, idan rai ya ɓaci silently suke fushi, sai dai suna shiga mawuyacin hali, har gara shi Umar yana shouting wasu lokutan, amma ruma gaba ɗaya kasa komai take idan tana cikin matsanancin ɓacin rai. Wata irin ajiyar zuciya kawai take yi.
"Yaya ni raguwa ce ko? Aka zageni, a kan gaskiyata kuma aka hukunta ni, ni ko?"
Usman ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Ke ba raguwa ba ce, kowa shaida ne, kamar yadda nake gaya miki, ki fuskanci duk wani abin da yake baki tsoro, gaba da gaba na tsaya miki"
Ta ɗaga kai ta kalli Usman, ya jinjina mata kai alamar ƙwarin gwiwa, ta jinjina kai ta mayar da kai ta kwanta a jikinsa, tana cigaba da ajiyar zuciya.
Duk wanda ya shigo ya ga ruma a haka, sai ya tambayi ba'asin meyafaru, ko ba ta da lafiya ne?
Mama ta ce "Ina fa, lafiyarta ƙalau, yau bori ne ya kar boka, ta tsokano wadda ta fi ƙarfinta, aka naɗa mata duka, shi ne take nema ta suma ki cigaba kar ki fasa halinki"
Aliyu ya tsaya a kan ruma ya ce "Ke, ki na wani sokwancin ki ka yadda aka dake ki har ki ke wa mutane kuka?" Ruma ta yi shiru ba ta amsa ba.
"Ina fatan dai ba a gaban wadda ta dake kin ki ka yi kukan ba? Wallahi da ina gidan nan sai kin fita kin rama, dan ubanki yaushe ki ka koma shashasha har aka dakeki aka fitar miki da jini, 'yar uban waye da baki taka mini ita ba"
Buɗe baki mama ta yi, ta kalli Aliyu ta ce "Gadanga, maimakon ku tayani yi mata faɗa, ku ke mara mata baya? Ba sai ku ce Allah ya sa hakan ya zama silar shiriyarta ba"
Aliyu ya girgiza kai ya ce "A'a Addu'a ce kawai za ta shiryata, amma ba a daketa a waje ta tsaya tana kuka ba, babu rago a gidan nan, ko ɗan uban waye ta daka zamu bada haƙuri, amma wallahi aka kuma dukanki a waje, ki ka zo mana gida ki na kuka, sai na ƙara miki wallahi, idan mazane kawai ban yadda ki yi faɗa da maza ba, ki zo ki gaya mini, amma mace dai 'yar uwakki, ki tattaka mini kowacece"
Aikuwa mama ta haɗasu gaba ɗaya ta din ga faɗa kamar ta ari baki.
"Kaf cikinku babu wanda na sha wahalr rainonsa kamar ruma, amma kuna zigata ta ɗauko magana, rainonta dai-dai yake da rainon fitinannun yara maza huɗu, maimakon ku tayani dawo da ita hanya, amma ku ke ingizata"
Gaba daya suka yi wa mama shiru, ta yi ta banbaminta ta yi ta gama.
*****
Karkarwa jikinsa yake yi, tamkar zai hau bori, jikinsa sai wani ƙaƙƙamewa yake yi, tamkar ba jikin ɗan Adam ba.
Wata matashiyar mace ce zaune a kan gadon, tana kallonsa, ido fal hawaye, ya yin da shi kuma ya cigaba da tunkararta.
Girgiza masa kai take yi, amma ta kasa motsawa balle ta gudu.
Yana zuwa ya zauna a gabanta ya tsura mata ido, ya miƙa hannunsa kan cikinta, take jikinta ya hau rawa ta rintse idanuwanta, tana zubar da hawaye. Sautin muryarta ne ya dakatar da shi ga aikata abin da yake ƙoƙarin yi
*Sarki ka ganni, ya na ga sarki da ƙananan kaya, sarki ka kalleni* tamkar a zahiri haka yake jin muryartata a cikin kunnuwansa, a hankali ya buɗe ido ya na ƙarewa ɗakinsa kallo. Sai a lokacin ya gane mafarki yake yi, ba zahiri bane.
A hankali ya tashi ya zauna, ya yaye bargon da ya rufa da shi, ya kalli agogon da ke kafe a jikin bangon ɗakin. Ƙarfe tara da rabi.
Ɗan guntun tsaki ya ja, me yasa yake yawan jin muryarta ne? Anya ba aljana ba ce ita ma?. Gabansa ne ya faɗi da yayi wannan tunanin, da kuma tuna matsalar da yake ciki, yake ta neman mafita a kanta.
Saurin girgiza kai ya yi, ya sauka daga kan gadon, ya wuce banɗaki.
****
Cikin matsanancin razani ta ƙwala ihu "Wayyo Allah mama" a gigice mama tayi kanta tana faɗin "Ke lafiyar ki kuwa?"
Tashi ta yi zaune ta na rarraba ido, tana kallon ɗakin.
"Lafiya menene?"
"Mafarki na yi na tsorata"
Mama ta ja tsaki ta ce "Ba dole ki dinga mafarki kina tsorata ba, tun da ba kya Addu'a kwanciya bacci".
"Wallahi mama na yi"
"Ke ki ka sani dai, ko a garin neman maganar ki ruma, kya tsokano abin da zai dinga tsorata ki, ya hana ki bacci tashi ki je ki yo alwala, yanzu za a kira sallar asuba.
Haka nan jiki babu ƙwari, ta tashi ta yi alwala ta gabatar da raka'atanul fajr, sannan ta yi sallar asuba.
Jikinta duk yayi sanyi da mafarkin da ta yi, amma ta kasa tuna me ta gani a mafarkin ya tsorata ta.
Babu wanda Ruma ta kula a ajinsu, ta nemi wuri ta yi zamanta ta yi shiru, tana ta takura ƙwaƙwalwarta, ta tuna mafarkin da ta yi ya bata tsoro, amma ta kasa har aka kusa tashi, hankalinta baya tare da ita.
Asiya ce ta zo kan ruma ta tsaya, ta riƙe ƙugu ta ce "Ki je ki wanke banɗakin da aka saka ki, ko na je na faɗa" tamkar ruma na jin tsoron Asiya, haka ta tashi jiki na rawa zata fita daga ajin, sai dai ta yi burki a gaban allo, ta ɗaukko chalk a aljihun rigarta, ta sake zana wata shirgegiyar matar, wadda tafi ta jiya, ta yi labelling ɗin ta.
Ta waiwayo kuma tana kallon Asiya, tare da jiran ko ta kwana.
Aikuwa kamar ruma ta san a rina, Asiya ta kuma nufo ruma, tana zuba ashar, kan ta ƙaraso ruma ta yi ciki da ita, suka faɗa kan wasu ɗalibai.
Hannun Asiya ɗaya ta samu, ta din ga duka kamar ta samu ɓarawo, sai da ta tabattar da ba zata iya kai duka da hannun ba, sannan ta koma fuskarta.
An kai ruwa rana kan a ƙwaci Asiya daga hannun ruma, sai a lokacin ruma ta ji hankalinta ya kwanta, baƙin cikin da ya tokare mata zuciya ya sauka.
Babu wata-wata, malamin su ruma ya saka su kneeldown a rana, ba tare da ya tsaya ya ji ba'asin ma meyafaru ba.
Tun a lokacin Asiya ta ji ba ta iya motsa hannun da ruma ta din ga jibga, ta din ga jin kamar ba a jikinta yake ba.
Suna Kneeldown ruma ta riƙe ƙugu ta ce "Ke kin isa ki dakeni na ƙyaleki, hmm baki sanni bane, kuma wallahi ban huce ba, zaki ga abin da zan yi miki, ki dakeni ki zageni, sannan ki zaci kin ci bulus, ai faɗa ni da ke daga yau har ranar busa ƙaho, ba dai uwata ce tsohuwar banza ba sai ka ce babata sa'arki ce ba? Ai ki yi mini komai ban da taɓa uwata, ban taɓa zagin uwar wani ba, kema babarki jibgegiyar bayerabiya masu kashi a leda"
Gigicewa Asiya ta yi, tana kuka tana son kaiwa ruma duka, amma ta kasa sarrafa hannunta ga ciwon da jikinta yake yi mata.
Ruma ta durƙusa ta dinga dumbuzar ƙasa hannu bibbiyu tana watsawa Asiya a fuska. Ban da kuka babu abin da Asiya take yi.
Ranar ma sai da aka tashi sannan aka sallame su, aka ce gobe da safe za su cigaba da punishment.
Rumaisa ta riga Asiya tafiya, ta je ta samu hanya, ta tattara duwatsu, ta tara su a cikin jakarta. Ta kuma datsar Asiya a hanya, ta dinga kabbara tana jifanta. "Sheɗaniya gara na jefeki na huta, na ga haka ake yi idan an je makka a jefi sheiɗan, gobe ko cewa aka yi ki kalleni, ba zaki sake ba balle ki dakeni"
Sai da ruma ta gama abin da Allah ya nufeta da yi, sannan ta wuce gida. Yau kam bakinta har kunne, jin ta take wasai ba ta da wata damuwa ko banza ta rama abin da aka yi mata har da riba, malamai kuwa ko zasu kwaɗata su cinye bai dameta ba.
Abdallah ne yake ta shiri, ruma sai tambayarsa take ina zashi?.
"Ke wai kin aikeni ne?"
"A'a, amma dan Allah ka gaya mini"
"Cikin gari zani ziyara"
Ta haɗa hannayenta biyu ta ce "Dan annabin rahama ka tafi da ni" hararta ya yi ya cigaba da shirinsa.
Ta dinga bin sa tana lallaɓa shi, har ya amince zai tafi da ita.
Mama ta ce "Hmm in dai ruma ce zata baka kunya, Allah ya sa kar ta ɗauko maka magana"
"Ta ɗauko ma, dakuwa zata yi wallahi"
Ruma ba ƙaramin daɗi ta ji ba, ganin ta a cikin gari cikin 'yan uwa, akwai 'yan uwan mama sosai a cikin gari, sai dai mama ba ta zuwa da ita, saboda ta din ga neman magana da dukan 'ya'yan mutane kenan.
Akwai wata 'yar cousin ɗin mama, da rashin jin su ya kusa zuwa ɗaya da na ruma, duk da ruma ta fita. Ta ce "Ruma, zo mu je yakasai, akwai ƙawata a gidan Turakin Kano, jikarsa ce biki ake a gidan, kuma za ayi kilisa, kan Abdallah ya dawo mun je mun dawo, mu je mu ciyo banza"
Ruma ta ce "yauwwa hauwwaliya, yi sauri ki shirya mu tafi kan ya dawo ya hana ni zuwa"
"Ke har da babbar leda zan ɗauko, idan mun ci mu ƙullo sauran"
Haka suka shirya, suka yi sallama a kan zasu je biki su dawo.
Suna tafe a hanya suka sai masara, suna tafe suna ci suna hira.
Tabbas idan ka ji wane ba ƙarya ba, gidan ya tsaru yayi kyau sosai da sosai, gini ne na sarauta da aka ƙawata da kayan alatu, ruma sai rarraba ido take yi.
Ƙawar hawwaliya ta din ga murna da ta gansu, ta kai su wani falo suka zauna.
Ruma kuwa hankalinta na kan wata mata, da ta sha ado sai kai wa take tana komowa tana wani hura hanci, tana dakawa mutane tsawa.
Ruma ta ce "Taɓ, wai wacece waccan?"
Yarinyar ta kalli wadda Ruma ta nuna ta ce "Laa Anty Samha ce, ƙanwar mama ce, ba mata bace ba ta da aure".
Ruma ta ce "too na ganta wata gwabjejiya, sai masifa take yiwa mutane, ni na zaci matar sarki ce ma, yakamata a samu mai kwaɗeta ya zata din ga hantarar mutane?"
Hauwwaliya ta daki cinyar ruma ta ce "Ke, ƙanwar mamanta cefa"
Yarinyar ta yi murmushin yaƙe ta ce "Bari a kawo muku Abinci, sai mu je wurin kiɗan ƙwarya da kilisa"
Ruma ta miƙe ta ce "Hauwwaliya, ni dai zan je wurin da na ga an ɗaure dokuna na kallesu, idan an kawo Abincin ki ƙulle mini nawa a ledar da ki ka zo da ita" buɗe baki Hauwwaliya ta yi, da jin hansfreen da ruma ta yi musu.
Kai tsaye ruma ta fito tana cigaba da kallon gidan, da yadda manyan mata ke shiga suna fita, da shiga kala-kala.
"Ke ba kya gani ne, meye haka?" Ruma ta ɗaga kai ta kalli wadda ta daka mata tsawar. Matar da take ta hantarar mutane ce.
"Eh bana gani, sandata na fito nema, ke da ki ke gani meya hana ki kauce?" Ruma ta yi maganar tana tsare Samha da ido.
Wata mummunar faɗuwar gaba ta ziyarci Samha, da ta yi tozali da idanun ruma, ga ta ƙarama amma wani abu mai kaifi ne a idanun ruma.
Ruma ta raɓata ta wuce abinta. Da sauri Samha ta bi bayan ruma, amma ta nemeta ta rasa.
Kai tsaye burgar dawakin da suka wuce ta je ta tsaya. Ta tarar da wani dogari yana basu Abinci.
"Sannu da aiki"
Ya kalli ruma ya ce "Yauwwa sannunki"
"Dan Allah ina dokin sarki a nan?" Yayi murmushi ya ce "Nan babu dokin sarki, na 'ya'yan sarki da manyan Hakiman fada ne"
"Dan Allah ka cewa sarki ya bani doki ɗaya"
Yayi dariya ya ce "Ke idan aka baki doki ya zaki yi da shi?"
"Hawa zan din ga yi mana" ruma ta din ga yiwa dogarin nan surutu, sai da ya gaji sannan ya ce "To ai Shikenan, yanzu dai fita za ayi da su, za ayi kilisar angwaye"
Ta jinjina masa kai, ta koma gefe ta tsaya, tana kallo aka shirya dawakan, aka yi musu kwalliya sannan aka fita da su.
Hauwwaliya ce ta fito ita da ƙawar ta ta tana faɗin "Ke ruma, tun ɗazu jira nake ki dawo, amma ki ka ƙi komawa"
"Ke ƙyaleni, kallon dokuna nake"
Ƙawar hawwaliya wadda suke da Turaki, ta ce "Mu je to, sai mu kalli kilisar"
Suka fita daga cikin gidan gaba ɗayansu, kan barandar wani gida suka je suka tsaya, suna tsumayin a fara kilisar.
Abin yana burge ruma sosai da sosai, duk wanda ya zo wucewa sai ta ɗaga masa hannu tana tsalle.Tun da suke wucewa babu wanda ta kira sarki, sai da ya zo wucewa tare da ango.
"Sarki mai koriyar alkyabba, a dawo lafiya, dan Allah ka bani kyautar doki, ko kuma ka ɗanani a kan dokinka!!!"
(Wannan 'ya ni kaina tana bani ciwon kai 😒 in kun ji ni shiru ku dinga yi mini addu'a, Allah ya ƙara mini lafiya 🙏)
Mai nema daga farko, ya duba watpad Please 🙏
Ayshercool
08081012143'
